BAI JUYA MAKU BAYA BA!!! MU HUKUMTA JUNA BISA ADALCI

Sau dadama Wasu Zakaji Suna Korfin Cewa Wane Tun Sadda Yasami Wata Daukaka Ko Wani Cigaba ko Shugabanci, Shikenan Yamanta Damu Cikin Huldarsa Na rayuwa Da Tarayya!

Dafarko dai Shi Al amarin Cigaba Nufin Allah neﷻ,  Haka Kuma Aka Halicci Dan Adam da Rauni Na Mantuwa da Kuma Shagaltuwa da Al`amuran Duniya Da Mance Baya, Kuma Cikin Hikimar Ubangijiﷻ Wannan Al`amari Shima Nada Amfani Arayuwar Dan Adam Bisa Yadda Harkokin Rayuwa Ke Wakana Inbabu Mantuwa! Tabbas Dan Adam Bazai Samu Sukuni ba.

Kada Kazargi Wani Dan Yasamu Daukaka Da cewar Ya Gujeka Kazargi Kanka da Hassada dakuma Yanke Zumunci, Domin da zarar Mutum Yasamu Daukaka Al`uma Sun kara Yimasa Yawa Kuma Bazai Samu Damar Ji Da Kowaba dole Sai anayimasa Uziri, Kuma Kai me Raki Dolene Ka ziyarceshi Matukar Ba Hassadar Daukakarsa Kake ba, Inhar Kana Buqatar Zumuncinku Yacigaba.

Mudinga Yiwa Juna Uziri Muna Tuntubar Lafiyar Juna Mudaina basar da Junanmu Cikin Lamarin Rayuwa, Mu Sulhunta Junanmu Cikin Sabanin tunanani Ko Rashin fahimta, Muyawaita Yiwa Junanmu Fatan Alkhairi Da Nasiha.

TARIHIN SAHABBAI 001

TARIHIN SAYYIDINA ABUBAKAR SADDIK ALLAH YA YARDA DA SHI,

(manzon Allah S. A. W) “yace ya Abubakar kai ne farko wanda zai shiga Aljanna daga al’umma ta”

Sayyidina Abubakar shi ne Abdullahi dan Abu kuhafatu ” usman” usman dan Amir dan Amir dan ka”abu dan sa”adu da taimu dan murratu dan ka”abu dan lu”aayu, bakuraishe. Bataime. Nasabarshi ta hadu da manzon allah ta wajan murratu dan ka”abu kakansu na biyar. Sunan shi a lokacin jahiliya “Abdul ka” aba” daya musuluta sai manzon allah ( S. A. W) yakara shi “Abdullahi” An yi mishi alkunya da Abubakar saboda riganyenshi wajan dabi”antuwa da kyamara halaye. Kuma an yimasa lakabi da saddik sabo da saurin bayar da gaskiyar shi ga dukkan abunda manzon allah (S. A. W) ya fada kuma manzon allah (S. A. W) yakara shi da “Atiku” shine mutumin da yafara musuluta a manyan. Shi ne mutum na farko, da ya fara kira zuwa ga addinin musulunci. Bayan manzon Allah Annabi Muhammad (S. A. W) shine yafara haduba a addinin musulunci. Shine abokin zaman kogo tare da manzon Allah na farko kuma shine nafarko cikin sahabbai goma da aka musu albishir da gidan Aljannah tun a duniya shine farkon Amirul hajji kuma yana cikin marubuta wahayin da akema Annabi Muhammad (S. A. W) An haifi Sayyidina abubakar (R. A) a makka bayan Shekara giwaye da shekaru uku (573 A. D) manzon Allah. Ya girma shi da shekaru uku. Yana cikin manyan shuwagabannin kuraishawa a lokacin jahiliya kuma a bakin manzon allah ne na kasa tun kafin aiko shi. Sau dayawa ma. Yakanje gidan shi su tattauna shine mafi sani duk larabawa game da tarihin nasabar kuraishawa. 
Kuma yakira mutane da yawa zuwa ga addinin musulunci. Biyar daga cikin su suna cikin sahabbai goma. Da aka yiwa bishara da Aljannah sune kamar haka :  
Ya sha a zaba iri – iri daga kafiran makka saboda shigar shi musulunci 
Har takai babu wani musulmai da azabtu kamar shi. Duk da irin matsananciyar azabar da suka sha suda sauran musulman farko daga kafiran makka. Bai yi kauraba zuwa kasar habasha ba. Ya tare ga manzon allah (S. A. W) lokacin kaura zuwa madina yana tare da Annabi Muhammad (S. A. W), tare suka shiga kogo kafin suwuce zuwa madina shine cukon mutane biyu da Allah ya ambata a alkur”ani in da yace : ” Idan baku taimakeshiba. ( Annabi), to ai Allah ya taimake shi yayin da kafurai suka fitar da shi ( daga makka) na biyu (mutane) biyu yayi dasuka shiga cikin kogo yake cewa da abokin shi (Abubakar)” kada kaji tsoro, Mu Hakika Allah ya na tare damu “( da taimako shi)” cikin suratul tauba:40, yayin da suka isa madina. Sayyida Abubakar, A wurin kharijatu dan zaidu. Da shi kuma manzon allah yahada su ‘yan uwantaka yayi da ya rinka hada yan’ uwantaka (ta musulunci) tsakanin mutane makka ( muhajiruna), da na madina (Ansaru) Sayyida Abubakar shine tamkar Waziri ga Annabi Muhammad (S. A. W), wajan gudanar da al’amuran daular musulunci. Mai babbar hedikwata a madina: birnin manzo,,,

Abubakar saddik ( R. A) ya dukkan yake _ yaken daukaka musulunci da yada shi da Annabi Muhammad (S. A. W) a yakin badar shine kan gaba wajan kula da wurin da manzon allah yake. Yana shir yanda yake zai gudana tare da rokon allah. har dai allah ya amsa addu’ar Annabi, ya aiko da rundunar mala”iku. Musulmai suka samu nasara. A yakin uhudu kuwa, Sayyida Abubakar. Shine jagora tsirarun Manyan sahabbai, suka gabata a filin yakin. Tare da manzon allah (S. A. W) yayin da kafurai suka tarwatsa rundunar musulmai.

Bissalam

Continue reading

MAGUNGUNA AMUSULUNCI

AMFANIN SABAYA A JIKIN YA”MACE

*DR ABDULWAHAB GONI BAUCHI*

Idan Mutum Ya Hadawa Matarsa (SABAYA) Yana Da Matuqar Ta’asiri a Jikin Ya”Mace Kuma Yana Haifar Mata Da Ababe Uku a Jikinta Akwai Matar Da Idan Tana Shayarwa Zakaga Kamar Ta Fito Daga Gidan Yari Wata Jikinta Yana Zubewa Ruwan Nononta Yana Lalacewa

*Nafarko Idan Mace Tana Amfani Da Sabaya Zai Taimaka Wajen Dawo da Halittan Da Allah Yai Mata Jikinta Nonon Bazai Zube Ba
*Na Biyu Idan Mace Tana Amfani Da Sabaya Jikinta Zaiyi Laushi Kamar Kwalabiya
*Na Uku Idan Mace Tana Amfani Da Sabaya Da zarar ta Haihu Irin Ramar Da Mata Keyi Baza Tayi Ba

Kuma Ruwan Nononta Zai Qara Yawa Sannan Bazai Lalace Ba Kuma Yaron Data Haifa Allah Zai Kareshi Daga Dangin Cututtuka

Kuma Hatta Magidanci Idan Yasha Yana Qara Masa Lafiya Da Kuma Kuzari a Jikinsa

MEYA KAMATA ASAMO WAJEN HADA SABAYA TASU KAMAR HAKA:
*Al Kama 1Mudu
*Danyen Shinkafa 1Mudu
*Waken Suya 1Mudu
*Ridi ½Mudu
*Hulba ½Mudu
*Gyada Mai Bargo/Kamfala
*Madara
*Zuma

YA ZA’A HADASU SHINE:
Ridi Da Gyada Ana Hadasu Wuri Guda Ridi a Soyashi Yadda Ake Kantu, Gyadar A Soyata Yadda Ake Quli Quli, Shinkafa Da Alkama Ana Jiqasu Tsawon 5hour Sai a Shanya Da Laima a Jikin Sai a Hadasu Wuri Guda

Da Ridin Da Gyadar Da Al Kama Da Hulba Da Shinkafar Sai a Niqa Matarka Tin Tana Da Ciki Ya Kamata Ka Fara Bata Har Zuwa Haihuwa Kaga Yadda Zatai Da Yaronta Kuma Nononta Dana Shayarwa Ko Bata Shayarwa Bazai Canza Ba Da Ikon Allah

TO YA AKE SHANSA
Yadda Ake Dama Kunu Haka Ake Damashi Sai Dai Idan aka Zuba Ruwan Zafi Ana Iya Maidashi Kan Wuta,
Sukace Karta Wuce Cokali Uku a Rana Musamman Cikin Babban Cokali Idan Kuma Harda Magidancin Sai a Sanya Cokali Shida

Su Kace Amma Idan Mace Bata Da Aure Kada Tasha Domin Yana Qara Sha’awa Kuma Yana Qara Yawan Nono Ma’ana Yafi Dacewa Da Matar Datake Shayarwa Domin Samun Ingancin Lafiyar Jikinta Don Kada Ya Zube

Kuyi Amfani Da Wannan Link Din Domin Samun Magunguna a Sauqaqe

ALLAH ﷻ Yasa mu amfana dash

ماشاءاللہ