BAI JUYA MAKU BAYA BA!!! MU HUKUMTA JUNA BISA ADALCI

Sau dadama Wasu Zakaji Suna Korfin Cewa Wane Tun Sadda Yasami Wata Daukaka Ko Wani Cigaba ko Shugabanci, Shikenan Yamanta Damu Cikin Huldarsa Na rayuwa Da Tarayya!

Dafarko dai Shi Al amarin Cigaba Nufin Allah neﷻ,  Haka Kuma Aka Halicci Dan Adam da Rauni Na Mantuwa da Kuma Shagaltuwa da Al`amuran Duniya Da Mance Baya, Kuma Cikin Hikimar Ubangijiﷻ Wannan Al`amari Shima Nada Amfani Arayuwar Dan Adam Bisa Yadda Harkokin Rayuwa Ke Wakana Inbabu Mantuwa! Tabbas Dan Adam Bazai Samu Sukuni ba.

Kada Kazargi Wani Dan Yasamu Daukaka Da cewar Ya Gujeka Kazargi Kanka da Hassada dakuma Yanke Zumunci, Domin da zarar Mutum Yasamu Daukaka Al`uma Sun kara Yimasa Yawa Kuma Bazai Samu Damar Ji Da Kowaba dole Sai anayimasa Uziri, Kuma Kai me Raki Dolene Ka ziyarceshi Matukar Ba Hassadar Daukakarsa Kake ba, Inhar Kana Buqatar Zumuncinku Yacigaba.

Mudinga Yiwa Juna Uziri Muna Tuntubar Lafiyar Juna Mudaina basar da Junanmu Cikin Lamarin Rayuwa, Mu Sulhunta Junanmu Cikin Sabanin tunanani Ko Rashin fahimta, Muyawaita Yiwa Junanmu Fatan Alkhairi Da Nasiha.