MATSALAR TSARO A NAIJA New post 2

MATSALAR MANYANMUNE!!

Matsalar tsaro A’kasata Fitowa ta biyu (!!) ✍️Ismail Hussaini Adam

Matsalar tsaro akasar Nigeria abune mai matukar wuya amaganceta da hanzari, Domin Al’amuran Sun jima Da Cakud’ewa cikin mummunar qaddara da muka samu kanmu aciki musanman Mu Al’umar Arewa. Ansamu akasi tahanyar wasunmu suna goyon bayan ta’addanci aboye, bincki da akeyi ana kin bayyana gaskiya, Shine babban Al’amarin daya gur’bata Al’amuran tsaro A’kasarnan. Wai sai ace anrufa asiri akwai ‘yan Alfarma.

Shifa d’an ta’adda, ko mai goyon bayan ta’addanci, Koda uwarsace data haifeshine yasan zata fallasheshi, Wallahil aziim zai aikata lahira, komai Son da takemai, balle jami’an tsaro ko Masu fad’a aji na gari Wad’anda aganinsu sune Cikas d’insu aharkar dasuke ciki. Yazama wajibi akan hukumomi, Da Shuwagabannin Al’uma ta ayyadar da hukunci, akan dukkan wani mai laifi data kama, takuma yi bincike akan dukkan wanda take zargi da ta’addanci, ko goyon bayan ‘yan ta’adda. Idan Tayi bincike inya tabbata kuma tazartar da hukuncin daya dace.

Hakan shine hanya mafi sauki, Ta hanyar da za’a gyara matsalar tsaro acikin Al’uma.

WANI ABINDA MUKA MANTA

Wad’annan masu laifi da’ake kamawa da sunan ‘barayin gida da masu fasa shagunan, Idan ba’azartar masu da hukuncin daya daceba Sune ake Sayansu Su girmama, Abasu Makamai sucigaba da ta’addanci dakuma Kisan mutane, haka kurum ba gaira ba dalili.

Dole ne acire maganar Alfarma, Dukkan wanda hukunci ta haushi kawai azartar masa shine adalci. Allah yafi kowa son bayinsa Amma yana hukumtasu idan sun aikata ba daidaiba. Tayadda yakema ‘Kona wasuma domin mummunar aiki dasuka aikata. Kuma yayi umarni garemu akan mu zartar da hukunci da adalci akan dukkan wanda doka ta haushi.

Hakika Al’uma tana shiga firgici da mummunar yanayine tahanyar sakaci da’akayi da hukunta masu laifin cikinta. A Nigeria mun sami kanmu cikin wannan yanayi tahanyar Sakacin hukumominmu da shugabanninmu.

RASHIN AIKINYI GA MATASA MA QALUBALENE

Matasa babu aikinyi a kasarnan dalili kuwa Shine, manyanmu basu kishin kafa wadatattun masana’antu burinsu gina gidaje kawai da zuwa ‘kasashen waje. Taya ‘Kasan wajen suka sami Cigabane Bayan samun nagartattun Shugabanni masu kishi Suna kula da hakkin Talakawansu. Yakamata Asamarda wadatattun masana’antu tayadda za’arage masu zaman banza dakuma yan Fasa ‘kwauri akasarnan. A’kasarnan akwai arzi’ki wanda yagirmi lissafi amma kuma munfi kowa Talakawa, wannan yasamo asaline danganeda Rashin tallafin jari da aikinyi ga masu ‘karamin ‘karfi, Saudadama wasu na fara kasuwanci amma da zarar sunsami karayar arzi’ki shikenan yazama abin tausayi. Mai iyuwa ma wanin daganan yakan koma goyan bayan ta’addanci, domin yasamu dukiya koma yazamo member na ‘yan ta’adda.

ANA ZALUNTAR ‘DALIBAN KARATU

Harajin karatu awannan kasa nada wahalar Gaske, ga kuma ana matukar Cin dunduniyar ‘Dalibai tahanyar mugayen Lecturers. Kai harda keta alfarmar (Mutuncin) ‘yan mata. A iya Saninmu ga Manyanmu na yanzu Shine. Sunyi karatune akyauta kokuma cikin sauki, Amma donme suke musgunawa Mutane ayanzu? Mafiya yawan malaman yanzu burinsu shine su samu kudi Suma a’kirgasu acikin masu Arzi’kin ‘Kasa. Bawai su bada karatu ga d’alibai ba kamar yadda yake a hukunce. Wannan yasa suke neman Kudi ido rufe a governati domin cimma burikansu dakuma kirkiro wasu tsaruka mabambamta. wadanda suke da rauni da Da’kushe har’ko’kin ilimi akasarnan.

Strike da ake samu a jami’o’i da Colleges yasamo Asaline daga, Son duniyar wasu daga cikin Malamai. Dolene Govrenati tasan hanyar da zata shawo kan Wannan Al’amari. Mutane na kashe kud’ad’e masu yawa kuma Suna d’aukan dogon Zango kafin su kammala karatunsu. Duk asadin matsalar Yajin aiki (Strike). Kuma akarshe yazamo Sun gama karatu kuma sun rasa aikinyi, Tambaya anan itace, idan mutum mai raunin imani yasha wannan wahalar kuma yarasa aikinyi, Me kuke tunani Zai biyo baya?

MATSALAR ASAMACE

Manyanmu na sama Sune ke morar arzikin ‘kasarnan. Manyan Nigeria mutum daya na d’aukan ma’kudan kud’i a governatin tarayya fiyeda Lissafin mai tunani Amma Nakasansu kuwa suna shan wuya matu’ka, Amma abinda suke samu ko na man mota baya wucewa, ballema aje ga Masarufi, dakuma Suturar jikki da kayan ‘Kawar ado. Don me corruption bazai Existing atsakanin muba Alhali wasunmu naci da gumin wasu. Su kuma manta da Hakkin dake tsakaninsu na zamantakewa. A’ka’idar Zamantakewa ta mususukunci dolene kasan Ci da Shan ma’kocinka Kamar yadda zakasan na Iyalinka.

Amma ayanzu babu ruwan wani da Wani, Anyi watsi da karantarwar addini anbi yahudu kuma gashi an’bace ba akamo yahuduba kuma Ambar Allah. Wadannan ma Suna daga cikin Hanyoyi mafiya girma na sanadin Lalacewar Tsaro a Nigeria. Zanci gaba Insha Allah. Allah ya tabbatar damu akan gaskiya da shiriya.

RAYIWAR YAN MATA

📝 QALUBALE GA RAYUWAR ‘YAN MATA ✍️ ******* GABATARWA *******

Assalamu alaikum warahmatullahi wabarkatuhu mai karatu.

Zanyi wannan rubutunne don nuni zuwaga yan uwana maza, domin kusan wa zaku auro ku kawo cikin gidanku, amatsayin abokiyar zama. Mata kuma su san dawa zasuyi qawance don gudun faďawa akomar halaka. Inda hali kutsaya kukaranta gabaki ďaya, domin zaka/zaki k’aru kuma inshaa Allahu zaku rabauta da waďannan zantuka nawa.

Ina bukatan addu’arku Allah ya haskaka qabarin mahaifina, dana mai karatu idan kuma suna raye, Allah yasa mugama dasu lafiya yakuma basu rabon cikawa da imani. Allah ka albarkaci rayuwar lahaifiyata da ayyukan alkhairi daku mumaďin gabaki ďaya.

‘YAN MATAN JAMI’A

Allah sarki rayuwarsu gwanin birgewane, saidai kuma abin tausayine awani bangaren, tayadda zaka samesu mafi yawancinsu akwai tsaftar jiki dana tufi. sannan sun san yakamata matuka, Saidai wasu acikinsu suna son yin aure kuma Suďin sun kame kansu. amma rashin dama takansa wasu acikinsu afkawa izuwa ga zina, Allah yakare. Hakan yana faruwane don rashin samun dama daga iyayensu. Zasu fidda gwani amma sai suce sam sai kin kammala karatu, sun manta da wasiyyar manzon Allah (s.a.w). Wasu kuma suna sheke ayarsune kawai tahanyar biyan bukatarsu ga maza, aduk sadda sha’awarsu ta motsa. Wasu kuma na fama da jimamin rayuwa tayadda suke fama da fuskantar barazanar lecturers lalatattu, da yunkuri batamasu tarbiyya da fansar jarrabawarsu da mutuncinsu. Iyaye ayi hattara zaku iya shiga wuta akan hakkin ‘ya’yayenku don rashin sadaukar musu da hakkinsu daya rataya akanku

‘YAN MATAN LUNGU

Idan akace matan lungu: sune mata masu talle akan titi, dakuma lungu da sashen unguwanni da sakokin ma’aikata, da shaguna (Kwantinan) kasuwanni. irin wadannan matan, idan basu sami kulawar tarbiyyaba sunfi kowasu mata sharri. Domin awani bangaren sukan ‘boye kamarsu suyi kama da mutanen kikrki amma sam bahakan bane azahirance. Kuma mafi yawanci acikinsune ake samun masu sace_sace, da bin maza bayan sunyi aure. domin sun saba da rike kudi masu kauri ahannayensu, ayayin budurcinsu. Hakazalika wasu acikin sunma suna saida budurcinsu kafin aure, a son zuciyarsu kokuma ara’ayin iyayensu mata. Ko uwayen goyensu na bariki. tayadda sukan taradda wulakanci agun mazajensu, dalilin rashin budurci bayan sunyi aure, hakan yake tursasu fita karuwanci bayan aure, ko sata wa mazansu na aure.

‘YAN MATAN BARIKI

Irin wadannan matan basuda mutunci. wanda su kansu sun yadda da hakan, kuma suna iya furtawa da kansu cewa su marasa kunyane amma daga fitsararrun cikinsu. Irin wadannan matan sukan tasone aguri mai lalacewar tarbiyya.

A gunda iyayensu ke zaune babu tarbiyya kuma iyayen basu kulawa da tarbiyyarsu. kuma babu addini agunda suke zaune. Saidai holewa da sha’anin duniyanci dakuma ta’ada, da muta kabbaranci. Ga uwa uba rashin dattako don ko waye ‘yar bariki zata zaki asalinsa ko da kuwa shugaban unguwarsune ko sarkin gari. Wadannan matan ko acikin garine shigarsu daban take sune Manzon Allah (s.a.w) yayimanz ishara dasu acikin hadisi ruwayar bukhari da muslim ” Akwai wasu nau’in mutane da Annabi baigansuba amma zasuzo anan gaba yake fadawa sahabbansa. Yace dasu dukkan wadannan mutane ‘yan wutane. ” na farko dai shugabanni azzalumai yake nufi kokuma masu hukunci da zalinci. nabiyu kuma yace; wasu matane zaku gansu da kaya ajikinsu amma tsaraicinsu na waje suna tafiya suna karairaya jiki, sa’annan kawunansu kamar tozon rakumi, yace kuma bazasu shiga aljannaba, kuma bazasu ta’ba jin kanshin aljannah ba. Domin awani qaulin anajin kamshin aljanna a tsahon tafiyar shekaru dari biyu ko dari biyar.” Allah kakare ‘ya’yanmu da ‘ya’yan ‘yan uwanmu daga Gurbacewar tarbiya.

‘YAN MATAN ASALI

Allah sarki wadannan sune abin tausayi, kuma sune masu wahala, kuma sune masu rabauta duniya da lahira. Tayadda suke fitowa daga gida na mutunci, iyayensu nagartattune su kuma kamammune. Sukan rike budurcinsu iya jimawar da zasuyi gabanin suyi aure. dashi suke samun martaba da nagartar zamantakewarsu ta aure. Kuma kafin suyi aure basu koda cakuduwane cikin maza ballema suyi wani mummunr mu’amala da namiji, hartakai ga sun zubadda mutuncinsu da budurcinsu. Suna matukar Kula ha hakkokin dake kansu na addini dana zamantakewar rayuwa. sune Allah ya ambacesu acikin Alqur’ani yadda yake cewa a Suratul_ahzab. surah ta-33 Aya ta:35 ”Lalle, Musulmi maza da Musulmi mãtã da muminai maza da muminai mãtã, da mãsu tawãli’u maza da mãsu tawãlĩu mãtã da mãsu gaskiya maza da mãsu gaskiya mãtã, da mãsu haƙuri maza da mãsu haƙuri mãtã, da mãsu tsõron Allah maza da mãsu tsõron Allah mãtã, da mãsu sadaka maza da mãsu sadaka mãtã, da mãsu azumi maza da mãsu azumi mãtã da mãsu tsare farjõjinsu maza da mãsu tsare farjõjinsu mãtã, da mãsu ambaton Allah da yawa maza da mãsu ambatonsa mãtã, Allah Ya yi musu tattalin wata gãfara da wani sakamako mai girma.”

Hakika mata masu addini sune mafi dacewa ga dukkanin wani ďa namiji musulmi. Kuma sune zakasamesu masu kyakkyawan hallayya dakuma tsaftatacciyar budurcin wanda babu kazanta acikinsa.

Duk da cewar kwaciyar aure na rana daya tak, yana wanke dattin kazantar bariki, duk jimawar da akayi dashi. Amma kuma duk da hakan kazanta bariki, yakan sanya zargi atsakanin ma’aurata, Zargi na har abada. Musamman ma yazamanto shima mijin mutumin banzane.

Allah karabamu da danasanin duniya da hasarar lahira. Ameen Dukkannin wanda yakaranta wannan rubutun nawa ya sanya aransa shima zai bada gudun mawa wajen gyara yau da goben Al’umar mususulmi kusani acikin addu’arku dani da mahaifana. Albarkacin wannan wata mai albarka ta Raladhana.

AHLUSSUNAH AYAU Posst No 1

MAFAKAR SUNNAH AYAU!!!

        Haqiqah Babu batun Sonkai, Salafawa da ‘yan izala sune ke da’awar sunnah Haqiqanin ta zallar madarar sunnah babu gauraye.

Dalilin wannan rubutu nawa:
Shine nuna mecece koyarwar aqeedar sunnah. Da manufar Izala da Salafawa akan sunna dakuma mecece asalin haqiqanin aqidar sunnah

  ********MECECE AQIDAH********

Aqidah:  amahangar Arufai (Malamai)_ wata hanyace wacce mutane suka kebance yadda zasu yi addini karkashin wata mazhaba bisa fahimtar magabata na farko, Bugu da kariaqidah takasance abace wacce take a aikace da furincin baka banda qudirin zuci. Ma’ana Azuci ni musulmine kuma nayarda da dukkan shika_shikan musulunci ina aikatasu amma bisa mazhabar malikiyya. To idan hakane madogarata bani da Ikon tilasta maibin mazhabar shafi’iyyah ko  ko hanafiyya. Bani damar cewa sai sunbi Hambaliyya
Idan mukayi duba danganeda yanayi nayanzu yadda rayuwa tashige rudani yadda Ake kawo abubuwa daban daban acikin addini. Dasunan addini.
Maluma na gaskiya suna iyakacin iyawarsu wajen wayar wa mutani kai dan ganeda hanyar tsira na addini, Amma saidai kuma akasi.
  Anasamun wasu miyagu da suke juya hankulan jama’ah suna b’ata Da’awar tasu.

Danganeda hakane Aka rarraba addini gida_gida aka kuma kirmiro aqidoji iri daban_daban hakika koda yahudu da nasarah suma abinda yararraba kawunansu kenan rabuwar kan maluma.

******Mafakar sunnah dai sune****
Marubuta da wa’azi da walima Wadannan sune hanyoyin da. Sunnah suke yada da’awarsu. Sabanin sufaye Shi’awa da ‘Yan dariqu. Su suna yada aqidun sune da sha’irai (mawaqa) da Majalisi dakuma Mawalid, idan akace mawaali shine jam’in maulidi.
   To A inda gizon ke saqa kuma, shine:   Akan samu sa’bani dan ganeda wasu al’amuran na Hanyoyin yada da’awoyin nasu.
Misali
  ‘Yan izala Da Salafawa sukan soki mauludi da zaman da’ira da Majalisi, dama kuma wake waken da yan dariqu sukeyi. Su kuma yan dariqu Basuda hanyar dasuke yada manufofi da da’awoyinsu sama da wadannan hanyoyi, Dan hakane suma suka sha AlwasAnfagdaura kambun yaqi da dukkannin wanda zai munantawa hanyar da’awarsu.

******Tasirin tarbiyyar aqidu******

***IZALAH SALAFAWA***

Yan izala da salafawa mafiya yawancin makarantunsu haddane da hadisai sai Tauhidi saikuma wasu littattafan addini a matakin farko kuma suna Anfanine da mashabobin makka da madina. Yawancin littattafansu wallafar can ne da sharhohin magabatansu.

***SHI’AH DA DARIQU**
Su kuma yawancinsu suna anfanine da mazhabobin iran da iraqi kuma afannin ilimin farko yawancinsu karatun tsangaya sukeyi. Sai agaba sunfi bada karfi wajen ilimin tarihi da baitoji yabo dana dafawa wannan dalilin ne ma yasa ake samun mawaka dayawa acikinsu.
*****“Nuni sananne dan gane da da’awar sunnah**””””””””
Maganar Gaskiya izala da salaf munada kyakkyawar manufa akan addinin musulunci kama daga maluman  mu dama marubutan mu dama Mu dalibai bakidaya . Burinmu  Azauna da juna lafiya da lumana.
Yan uwana masu  karatu kusani cewa manufar wannan rubutun nawa shine in bayyana mecece haqiqanin Sunnah
Kuma suwaye Ahlussunnah na gaskiya
Danhaka na rarraba rubutun kaso uku
Wannan shine nafarko agaba zakujini da wasu kamar haka:
        
           ******Haske Akansu******

### Suwaye Ahlussunnah?…………..)

Dukkan wanda yariqi sunnah ta annabi kuma yake kokarin dabbaqata kuma yake nesanta daga barna da rarraba kan al”umar musulmi.
      
                 ***Dakuma**

### *Sunnah ba Aqida bace!………….)

Ahlussunnah yana suffantuwane da kyawawan dabi’u baya neman ilimi domin muqabala ko dan.yakare aqidah ba.

BAYAN RAYUWAN DUNIYA AKWAI RAYUWA BAYAN MUTUWA

GASKIYA AKWAI MATTSALA!!!!


Sau nawa kake zama domin Bincike ko sauraron Yadda zaka gyara Ibadarka?????
         Sau dadama idan na kadaita sai nayita tunani dan ganeda lammarin gudanar addini agun wasun mu. Zakaji mutum nakiran kansa musulmi amma farillan alwala ma bai sani balle in ta ‘baci ya gyara farillan sallah ma bai saniba balle inyayi Rafkanuwa yagyara. Ko na wanka ballema ilimin gyaransu.
    Wayyoooni duniya ina zaki damune kowa kagani abinci kawai yake nema kokuma yadda zai huta ko yadda zaiji dadin duniya gaba. Saidai kash itakuma tafiyarnan da take gaban mu batta da rana. Kawai zuwa take kwatsam kara zube ba zato ba tsammani.
    To taya zamu tara guzirin komawa ga mahaliccin mu domin samun hujja garemu aranar sakamako?
    Ansa
    Mukoma munemi ilimin addini mugyara ibadu da mu’amalarmu kafinnan musami hanyar tsira. Wani abin ban takaici shine yawanci mukan jahilci lammarin addini bawai don rashinsaba sai don aqidanci. Mutum baida karatun komai jahilin kauye afagen addini amma saikaji na karyata abubuwan da malamai ke fada dan ganeda hukuncin halasci ko haramcin wani al Amarin addini. Dalili kuwa shine don aqidarsu ta banbanta, Alhali baida hujja ta aya ko hadisi data karyata al’amarin dalili kawai don malumansu basayi yan abiyari (inbasu wane bazamuyiba).
    Wannan shi ake kira da shi’anci ashari’ar musulunci ma’ana raba kan al’umar musulmi. Tahanyar sabawar fahimta ko mazhaba. Abubuwan da kejawo haka sune:
    _Jahilci
    _Son zuciya
    _Son shahara
    _Munafinci
          ***JAHILCI***
    Idan jahilci yayi naso (katutu) azuciyar mutun saikaga na karyata koma mene ne addini ni kuma in yayi shugabanci zai dinga shirme yayita kawo jahilci alammuran dasunan gyara daga karshe zaiyita kokarin fada da malamai idan suna fada masa gaskiya. Jahilci nasa girman kai da hassada matukar maishi na tare da masu ilimi kuma akayi rashin sa’ah yawuce su wata daukakaka tarayuwa.
       ***SON ZUCIYA***
Idan mutum nada son zuciya komai aka fada bazaibiba sidai yakowo tasa abi. Koda tasa hanyar me raunice zai toge yadage akan sai anbi tasa daga karshe in anki zai fara neman mabiya daga baya saikaji ya Fidda tasa sabon kungiyar daban ko juma yafandare yayi reshe akungiyarsa daban.
    ****SON SHAHARA****
    Mafiya yawanci anfi samu daga wanda suka ‘Danyi karatu amma bamai nisaba sunason taka hawa mai nisa amma kafarsu baikaiba. Burinsu dai komai zai wakana yazam anyishi harda furucinsu. Amma basuda cikakken ilimi abangaren irin wadannan ywanci akansamu masu kyakkyawar manufa amma rashin ilimi mai nisa yana wargaza manufar nasu.
    Yakai dan uwa shawarata gareka katsaya iya matsayin ka kabar abinda Bakasaniba.
    Masu hikima nacewa Bansaniba shima wani yankin ilimine.
   
      *****MUNAFINCI****
    Akwai wasu burinsu kawai azagi musulunci da musulmai. Zasu tsaya kai da fata su tabo wannan aqidan da wata ta daban, Harsu haddasa wata rigima tsakanin musulmai wadannan basuda wata kyakkyawar manufa akan musulmai wasunma bamusulmai bane burinsu su wargaza wata shiri ko wata tanadi wacce musulmai sukeyi, ko don su raba kawunan al’umar musulmi.
    Allah katsaremu daga sharrin makirai da fajiran munakan addini.
    Allah yamayar da makircin garesu dasu da wanda suke sasu.
    Allah kabudemana kwakwalenmu don gujewa afkawa rudanin addini.
    Allah  kabawa maluman mu damar isar mana da gaskiyar koyi na Addini.
   

AQEEDAH TA ITACE MUSULUNCI

AQEEDATA

Dasunan ALLAH MAI RAHAMA MAI JINKAI

      Wasallahu Alaa man Laa Nabiyya ba’adahu Muhammadun bn Abdullah .(ﷺ) Salawatullahi Alaihi, wa Alaa Aalihi wasahbihi wasallama tasliiman khasira.

Waba’ad;
Assalamu alaikum warahmatullahi warahmatullahi wabarkatuhu, Mai karatu idan baka manta ba ada nayi Alqawwarin fadawa mai karatu mecece aqedata, dakuma matsayata dangane da halascin wakokin yabo da kirari da Haramcin kida Amusulunci.

Ⓜ Mashaa ALLAH Alkawwari yacika;
     Ni Ismail Hussaini Basalafene (Assalafy) Ne. Sala ba Kungiyace ta Aikin addini bawai Shi`anci bane. Wata al umace dake aiki akan Hani ga barna dakuma umarni da aikin Alkhairi. wacce take kuma koyi da magabata. Ainihin Kalmar Salaf tana nufin Magabata.

Salagiyya kuma tana nufin Bin tafarkin magabata. Wannan itace Al umar damuke koyi dasu na kwarai din cikinsu. Amma mu musulmaine kamar Sauran musulmi. Kuma munyi imani da Alqur`ani da hadisai kuma manzon mu shine مُحَمَّد ﷺ

Shi muke kwaikwayo a hali dakuma ayyukan.
Basai nayi bayani akan ko mene aqidah ba. Domin abaya nayi bayani akai karin bayani dan ganeda aqidar salafawa shine { (Aqeedadussalafussalih bi muwafaqati Sunnatin_nabawiyya wa Ashabuhum) (Ma ana aqidar bin tafarkin annabawa da sahabbansu) }.
   Aqidar itama Ahlussunnah ce akarkashinta akwai izala kamar yadda akasani, wadda suke da manufa iri daya dan ganeda da`awa da tsarukan karantarwa iiri daya saidai ita salafiyya kuma tafi yada da awarta ta social media fiye dana izala. ma`ana tafi dukufa wajan rubuce rubucen tarihi ta hanyar wayar da kai ga addinin musulunci da musulmai bisa yadda Zamani yakasance.  Dawayar da kan mutane Dan ganeda rayuwarsu dazamantakewarsu da Ladaftar dasu da koya masu dabarun rayuwa dawayar dasu Ga addini suyishi sukuma dabbakashi dayadashi a duniya.  Dukka sune Aikin salafawa.
Kar nazurfafa atakaice wannan itace aqidata. saikuma magana akan maulidi da kasidu masu kida da da marasa kida.

WAKOKIN YABON ANNABI
Haqiqa wakokin yabon annabi babu Kida ya halasta kaidai dolene yazama duk yaren dazakayi wakan yabon annabi dashi. yazamana kana da ilimi akan yaran sosai domin kiyaye kalmomin da zakayi amfani dosu, donyin yabon kuma dolene ka koyi ilimomi aka yaran kamar haka: ilimin balaga, Qaamusu, Ka`idojin rubutu, Ilimin Grammar, Dakuma tarihim annabin dama mawakansa  nada, domin azamanin annabi  ﷺ Anyi masa waqoqi dayawa harma ayari yake dasu na mawaka Ammafa su basuyi da kida bakuma yi sukeba Dan holewarsu ba ssunayine domin maida martani wa kafirai sai kuma domin dafawa Ga fiyayyen halittaﷺ kutambayi malamai zasu baku karin bayani akai.
    To awannan zamani namu akwai mawakan dake waqoqi nayabo amma da kida ko nace kayan sauti mabanbanta. wallahi! Tallahi!! Billahillazi La ilaha illahuwa wuce gona a kayan kida sautin shaidanune!!!

Me karatu kayi shari ah ta adalci٠
Masu wakokin yabo ayanzu musan man agun maulidi shin kaso hamsin cikin dari suna tantance me suke fada kafin su fada awakokinsu? babu shakka Amsar itace a`a.
   Muyi wa kanmu adalci waqa na ilimi wanda ba kida nayabon Annabi yahalasta amusulunci, ko muma a Tafiyarmu ta salafawa munada mawaqan yabon annabi amma basuyi da kida kuma sai an karantaddasu kuma littafai suke bugawa akuma tantancesu agaban malamai kafin suje subayar ga masu hazakar furuci su rera wakokinsu ba cinzarafi da zagi ko aibata wani ko wata aqida da ace ´yan d`ariqun sufaye da ´yan Shi`ah suma zasuyi adalci wa kawunansu dasai suma su rage msu hankalin cikinsu yakamata su daina waka da kida suyi waqa tsarkakakkiya da yabo wanda yadace da tunani mai kyau da koyarwar Addinin musulunci.
 

 BIKIN MAULIDI 

Bashakka bikin Maulidi Bai ingantaba koda ahadisine mai raunine babu, ba  ko wata yarjeniya ta wata ayari namaluman sunnah danayanzu dana da duk sun daidaita akan bai ingantaba. Hasalima suna kirantane da bidi´ah muhadatha ma`ana bidi`ah kirkirarriya. Batada tushe ko asali daga magabata, akwai hadisai dayawa wadanda suke tsawatarwa danganeda kirkira a addini. Arufai na tsawatarwa danganeda kirkira a addini. Ayanzu acikin maulidi allah ﷻ Shine kawai yasan bidi`o`in da aka kirkiro.
  Banso Raba rubutun  ba amma dolene ta saka `yan uwa kuyi hakuri muhadu arubutu nagaba mai Taken Aqeedata