TARBIYYAR ‘YA’YA AMUSULUNCI

══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════TARBIYYAR ‘YA’YA AMUSULUNCI══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════

══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
                       GABATARWA
══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
                            ﷽
Dukkan Yabo da Godiya Su Tabbata gin Ubangiji Allah Madaukakin Sarki, Wamda Yayi Komai da Kowace Iriyar Halitta Kuma yakyautata Surarmu Yabamu Tagomashi Yasnyamu Musulmi, Muna Gode Masa Bisa Wadannan Falala da Baiwar Arziqi Muna Salati da Sallamawa ga Fiyayyen Halitta Mai Tarin Matsayi da Girman Daraja Annabi Muhammad, Tsira da aminci Sutabbata agreshi da Iyalan Gidansa Da Sahabbansa, Da Dukkan Wadanda Suka bi Kyakkyawar Tafarkinsa Madaidaici Har izuwa Ranar Sakamako.

     Godiya Ta Musamman ga Iyayena da Malamaina, Wadanda Sukayi Dawainiya Dani Wajen Gina Rayuwata domin Tayi inganci Ina Rokon Ubangiji Yakarawa Rayuwarsu Albarka, Dani Dasu da masu Karatu Allah Yahadamu Agidan Aljannah Alfarmar Rahamarka Allahﷻ.
══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
           ✍️Ismail Hussaini Adam
══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════

════ ❁✿❁ ══❁✿❁══ ❁✿❁ ══❁✿❁                                   
❁✿❁ ❁✿❁ALPHOLTAWY❁✿❁ ❁✿❁
════ ❁✿❁ ══❁✿❁══ ❁✿❁ ══❁✿❁

                       SHINMFIDA
══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════

_Tarbiyya Abace mai wahala, sai an dage an tashi tsayin daka sannan za’a dasa ta, ya ku Iyaye abu na farko daya kamata ku cusa a zuƙatan yaran ku, ko zuciyar yarinyar ku, ko kuma zuciyar ɗan ku Shine <TSORON ALLAH.
Domin samun nagartacciyar rayuwa a tare dasu da kuma tarbiyya mai kyau.

_Daga lokacin da yaro ya fara wayo, ya fara magana, yasan abincin da zai sanya a bakin sa, ko kuma abin sha to daga wannan lokacin ya kamata ku fara cusa masa jin tsoron Allah a zuciyar sa sannan su San Wane ne Manzon Allah S.W.A, Menene Matsayin sa a Wajen Al’ummar Duniya baki ɗaya da Wajen Allah.._
_ku cusawa yaran ku jin tsoron Allah ta hanyar sanar dasu ubangiji, abinda yayi umarnin a aikata da kuma abinda yayi hani a kai.kamin ku jefa yaran ku a makarantar boko ku fara tura su ta islamiya, malamai magada Annabawa nayin nasu kuma kuna yin naku to insha’Allahu tarbiyar yaran ku zata zamo mai sauƙi a wurin ku a lokacin da suka balaga suka gama mallakar hankalin kan su._
_Sa’annan ku cusawa yaran ku son ilimi na addini dana zamani Kasancewar ilimi Shine Ginshiƙin Rayuwa, hakkin kune iyaye ku bawa ƴaƴan ku ilimi wanda zai amfanar da su duniya da lahira, ba ƴaƴan ku kawai ba hatta ku iyaye yana da kyau ku samarwa kan ku ilimi. Shi ilimi haske ne mai haskaka rayuwar ɗan adam ta kowanne fanni ba kawai don neman aikin abin duniya ba..wanda mafi akasarin iyaye yanzu sun fi gina ilimin ƴaƴan su akan neman aikin abin duniya duk da cewar hakan ba laifi bane amma ya kamata mu nazartu muyi duba sose akan hakan, muyi faɗi tashi mu jajirce mu cije don ganin mun inganta rayuwar ƴaƴa da ilimi na addini domin da shine za’a tafi lahira saɓanin na duniya da inda muka same shi anan zamu bar shi._
_Sose muke tafka kuskure a rayuwar yanzu, an cusawa yara musamman mata son abin duniya, ku farka iyaye musamman iyaye mata, kin cusawa ɗiyar ki son abin duniya, kin cika rayuwar ƴar ki da burin abin duniya, kin ƙawata idanuwan ta da hangen abin cikin duniya an manta da mutuwa na tafe a kowanne lokaci. fatan ki, burin ki, mafarkin ki, jin daɗin ki, kwanciyar hankalin ki, tayi-tayi ta gama Secondary School ta Shiga Jami’a tayi degree tayi Masters Domin ta tara Muku Dukiya kuyi kuɗi duniya tasan da ɗiyar ku ko ɗan ku, ku huce takaicin duniya, hakan yana da kyau kuma ba laifi bane sai dai ta gefe guda a kwai illa, akwai matsala._
_Duk saboda wannan burin kun hana ƴar’ku aure, baku sashi a cikin lissafin da zai inganta rayuwar ƴar’ku, terming ɗin ku da terget naku shine kawai wancan duk saboda kada burdget naki ke uwa ya rushe (ga wasu iyayen). Shin idan anyi auren nan ba’a karatunne?, shin idan anyi auren nan ba’a aikinne?, shin idan tayi auren nan zai hanata dukkan muradin ki da kike son ya cika?. Kin Hanata yin Aure, ƴaƴayen mu ba duwatsu ba, b marasa lafiya, sha’awa na Damin ta, Samari kullum kawo mata hari suke, koda yaushe tana tare da su a makaran ta ko a waje, yau da gobe sai Allah ba fata ake ba, Allah ya tsare mu ya tsare mana ƴaƴayen mu._
_Mu riƙa kai zuciya nesa a kan yaran mu, duka da hantara da zagi da mummunar kalma basu zasu gyara yaro ba face ƙara lalata shi, ku dinga yawan yi masu adu’a a koda yaushe, kar ku faɗi kalma mara daɗi a kansu a lokacin da suka ɓata maku rai, don Allah iyaye mu iya bakin mu akan yaran mu, kar mu manta matsayin bakin mu akan su, fata na gari da adu’a ta gari a kansu shine dai-dai.._
_ku koyar da yaran ku da sabar masu yin sallah akan lokaci, ku koyar dasu adu’oin neman tsari da kariya kamar yanda ma’aiki ya koyar damu, ku zama masu lura da irin fina-finan da suke kallo domin kuwa shima kallo na ɓata tarbiyar yaro ya rusa duk ginin da kayi a baya, ku sabar masu da sauraran wa’azi kamar yanda ya kamata bakin ku ya saba wajen yi masu wa’azi._
_Haka Zalika ku kasance abin koyi ga yaren ku, kuyi ƙoƙarin aikata abu mai kyau tayanda zasu gani su ɗauka daga gare ku.. Ku zama masu zama da yaran ku kuna shiga cikin su domin jin matsalolin su, sannan ku zama masu sanya ido a duk abubuwan da yaran ku ke gudanarwa na yau da kullum tun kama daga kan ƙawaye, lura da irin abokan da yaro ke mu’amala dasu yana da kyau matuƙa da gaske, kuma hanya ce ta kiyaye yaron ki daga faɗawa ga miyagun abokai, idan har kun sanya ma yaro ido akan abokan tarayyar sa lalle tabbas zai ji tsoron zama da ɓata gari, zai yi duk yanda zai yi yaga yayi ƙoƙarin nisan ta da banzan abokai, fatan mu Allah ya kare mana zuri’a ya kuma shiryar dasu._
_mu guji kuma mu kiyaye bama ƙananun yaran mu da suka tasa wayar hannu, wannan waya da muke ganin ta haƙiƙanin gaskiya ba ƙaramar musiba bace, haɗari ce babba ga rayuwar ƴaƴa wallahi, don haka mu kiyaye basu waya musamman ta android a lokacin da suke da ƙarancin shekaru…. Ku zama masu sanya ido a kan shige da ficen ƴaƴan ku musamman ke uwa da kike zaune cikin gida koda yaushe, ba kowanne wuri ya kamata ku bar yaran ku suke zuwa ba, kuma ba’a koda yaushe ya kamata kuke barin su fita ba, duk da cewar rayuwar yanzu ta sauya yaran mu sunfi mu wayo da dabara… Idan dama ma da hali duk sanda ƴarki mace ta buƙaci zuwa wani wuri kiyi mata jagora, sannan ki hani yaran ki tarayya da ƙawaye barkatai._
_yake uwa ki zama mai sa’ido sosai da sosai akan ɗiyar ki mace wajen duban irin littafan hausa dana turan ci da take karantawa, ki tsoratar da ƴar’ki kiyi mata barazana da karanta littafin daya kauce hanyar kunya da tarbiyya, haka zalika idan ƴarki ta taso da sha’awar rubuta littafi shima ki tsoratar da ita ki mata baraza na ta yanda zata ji tsoro ta kuma kiyaye rubuta abinda ba shi da kyau, ki tunatar da ita cewa lalle ubangiji zai tsaida ita akan abinda ta rubuta, ki zama mai bincikar wayar ta akai-akai, ki zama ƴar jarida ga yaran ki, kisa musu ido akan duk abinda zasu samu, bi ma’ana dukkan abinda kika gani a hannun su ki sasu gaba ki titsiye su don jin daga ina suka samo shi?, taya suka same shi?, koda yaro zai ce maki ga wurin daya samu kuyi ƙoƙarin bin diddigin inda ya same su ɗin… Karku sabarwa yaron ku da riƙe kuɗi domin kuɗi na ɗaya daga cikin abinda ke rusa tarbiyar yaro._
_yake uwa ta gari, ki sanya ido akan fitar ƴarki daga gida wajen sanya sutura, ki tuna musulunci ki tuna faɗin Allah maɗaukakin sarki a cikin littafin sa mai tsarki mai girma, ki tilastata ki sabar mata da suturce jikin ta a yayin da zata fita… Idan mai sanya hijab ce ki sanya ido wurin ganin kayan data sanya aciki da kuma abinda ke ƙunshe cikin jakar hannun ta, domin wasu ƴaƴan namu kan yaudare mu da fuska biyu.. Ki hani yarinyar ki da amsar kuɗin hannun samari, ki kuma hani yaran ki da saurin miƙa hannu, ki hani yaran ki da kwaɗayi da son abin duniya._
_ya ku iyaye na gari, daga lokacin da kuka fahimci ƴaƴan ku na buƙatar aure, lalle kuyi gaggawar yi masu, kuyi gaggawar yi masu, kuyi gaggawar yi masu, hakan shi zai hana yaɗuwar ɓarnar dake faruwa a doron ƙasar mu, ba komi ke jefe ƴaƴan mu cikin baƙincikin rayuwa ba sai wajen tauye masu hakki da muke, musamman ƴaƴa mata, don Allah iyaye da zarar kun fuskanci ƴaƴan ku na son aure kuyi masu domin shine mafita kuma shine kariyar su daga faɗawa mummunar halaka, kuma shine yayewar damuwar da za’a shiga a gaba._
_Daga ƙarshe karmu manta zamu cimma kyakykyawan burin mu ne akan tarbiyantar da yaran mu wajen yawan tunsar dasu faɗin Allah da Ma’aikin Allah._
_Ya Allah kasa mu dace, Allah kuma ya bamu ikon sauke hakkin ƴaƴan mu da Allah ya ɗora mana domin Ƴaƴa Amana ce Allah ya bamu.

══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
                 ASALIN TARBIYYA
══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════

Kalmar tarbiyya, ararriyar kalma ce daga Larabci (التربية aka Hausantar da ita. Kalma ce magamaiya, wacce ke iya ɗaukar ma’ana ta renon jikin yaro; hanyoyin kyautata ruhi da kuma koyar da kyakkyawar cuɗanya da jama’a. Abin da ake nufi a nan shi ne cewa, tarbiyya ta shafi gangar jiki, ruhi da kuma yadda mutum yake cuɗanya da sauran jama’a, a al’ummance da kuma ɗaiɗaiku.

Ƙololin buƙatar tarbiyya ita ce gina cikakken mutum mai amfanar da kansa da kuna waninsa.

Bisa la’akari da wannan faffaɗar ma’ana da wannan kalma take da ita, rubutun zai taƙaitu ne wajen yin magana a kan abin da ya shafi ruhi da kuma cuɗanya. Zai yi magana bakin gwargwado a kan ma’anar tarbiyya, manufarta, amfaninta, masu bayar da ita, jerin wasu kyawawan halaye da kuma yadda Bahaushe yake bayar da tasa tarbiyyar, da sauransu bakin gwargwadon iyawa.

══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
Ma’anar Tarbiyya
══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════

Saboda zamowar kalmar tarbiyya mai tushe a Larabci, zan kawo ma’anarta a Larabce da cewa, “Ita ce ayyukan ɗaukakowar halittu, wato ƙarawa mutum mutumtaka domin ya samu kaiwa cikakkiyar daraja matabacciya a jiki da aiki da ruhi da kuma cuɗanya”, Abu Hamza (2013). Daga wannan ma’ana za mu iya fahimtar cewa, tarbiyya reno ce. Saboda dukkan abubuwan nan da aka ambata suna ƙunshe cikin reno. Shi kuwa reno ana yin sa ne mataki-mataki. Sai dai ya fi zafi a tsakanin ranar farko ta haihuwa zuwa shekara uku. A wannan tsakanin komai yi wa mutum ake yi.  Ɗawainiyoyin suna fara raguwa ne bayan an yaye mutum wato daga watanni 15 na haihuwa zuwa shekaru 2. Daga wannan mataki yawancin yara sukan fara yi wa kawukansu wasu abubuwan kamar ci da sha da sauran ƙananan abubuwan rayuwa.

Daga wannan mataki na yaye kuma, sai a shiga kiwonsa, da ma’ana ta lura da zirga-zirgarsa ƙut-da-ƙut har zuwa kamar shekaru 5 ko 6, idan zai kai kansa mahallaka ko dai a ce da shi bari, ko kuma a je a ɗauke shi ko a janye shi da sauransu.

Idan ya haura shida kuma, to ya fara kai wa matakin da zai fara cuɗanya da wajen gida, sai kuma ya shiga makaranta. A makarantar ma renonsa ake yi, saboda a koyar da shi ne alaƙoƙin da suka shafi rayuwarsa ta duniya da kuma ta lahira, iya tsawon karatunsa da ma rayuwar baki ɗaya.

Saboda haka idan muka koma kan waccar ma’ana ta tarbiyya muka ciro kalmomin cewa, ayyuka ne da ke ɗaukaka halitta, za mu gan su cikin wannan ɗan taƙaitaccen bayani game da reno da na yi.

Ana kuma iya cewa, tarbiyya ita ce horas da yaro kyawawan halaye domin ya zama mutum nagari. Ko kuma a ce, hanya ce ta nuna wa yaro yadda zai tashi da kyawawan halaye ababen yabo a cikin jama’a.

══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
Manufar Tarbiyya
══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
Babbar manufar tarbiyya ita ce samar da mutum mai kyawawan halaye ababen yabo domin ya zama mai amfanar da kansa da kuma waninsa.

══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
Amfanin Tarbiyya
══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
Amfanin tarbiyya ba zai ƙidayu ba, amfaninta na ƙarshe; wato maƙurar amfanin nata shi ne mutum ya samu kansa a gidan Aljana a lahira, a nan duniya kuma ya zama son kowa, ƙin wanda bai samu ba.Waɗannan gajiyoyi da za a ci; duniya da lahira, su ne maƙura, sai kuma wasu ɗaiɗaikun abubuwa da zan lissafo kamar haka:

══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
Tsarkake Halaye: Tarbiyya tana tsarkake halayen mutum ya zama mai kyawawan halaye.
Sauƙin Rayuwa: Kyakkyawar tarbiyya tana saka mutum ya rayu, rayuwa mai sauƙi. Saboda zamowarsa mai wadatar zuci.

══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
Farin Ciki: Mutum mai cikakkiyar tarbiyya akan same shi cikin annashuwa a mafiya yawan lokutansa. Saboda koda wani abu can gefe ya ɓata masa rai, to yasan idan ya zo yin hulɗa da wani wanda abin bai shafe shi ba, sai ya danne wancan ɗacin a ransa shi kaɗai.

══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
Girma da Ɗaukaka: Kyakkyawar tarbiyya tana ɗaukaka darajar mutum a idon mutane a nan duniya, haka nan ma a wajen Ubangiji Mai Girma da Buwaya.
Kwarjini: Kyakkyawar tarbiyya tana saka mutum ya zama mai kwarjini.
Matakan Bayar da Tarbiyya.

══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
Akwai matakai ko hanyoyi da ake bi wajen bayar da tarbiyya da suka haɗa da nuni, lura, umarni da kuma hani.

══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
Nuni: Abin da ake nufi da nuni a nan shi ne aikata aiki a aikace, wanda daga nan shi wanda ake tarbiyantarwa zai gani ya koya. Tirƙashi, masu iya magana sun ce; “Idan mutum ya ce zai baka riga, to duba ta jikinsa”. Wannan magana ta zo daidai da faɗin Larabawa cewa; “Maras abu baya bayar da shi”. Saboda haka dole ne mai bayar da tarbiyya ya zama mai tarbiyya.
Wannan hanya ta bayar da tarbiyya ita ce mafi tasiri da kuma muhimmanci wajen bayar da tarbiyya. Saboda haka dole ne masu bayar da tarbiyya; iyaye, malaman makaranta da sauran jama’a suma su zama masu tarbiyya. Misali, dole iyaye su zama masu tsafta a aikace, kafin su dasa halin tsafta a zukatan ‘ya’yansu. Idan yaro ya tashi ya ga iyayensa suna share gida tsaf-tsaf, basa barin kwanon abinci da dauɗa, basa jefar da sutura ko’ina a ciki da wajen ɗaki, to a haka shi ma zai girma mai kula da tsafta. Kuma zai tashi shi tsafta ya sani bai san ƙazanta ba. Saboda haka da zarar ya fara zuwa makaranta malaman makaranta ba za su wahala da shi ba.

══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
Umarni da Hani (Kwaɓa): Umarni shi ne a riƙa gaya wa yaro yi kaza. Misali, idan yaro ya tsoma hannun hagu cikin kwanon abinci, ko ya riƙe abinci da hannun hagu zai kai bakinsa, sai a gaya masa cewa, wannan ba shi ne hannun cin abinci ba, ga na cin abinci nan. Da haka zai gane hannun dama dana hagu.
Shi kuwa hani shi ne kore abu. A wannan gaɓar kuma yana nufin kare ko dakatar da yaro daga aikata aikin da ba mai kyau ba. A cikin wannan misalin dana kawo a sama, akwai gaurayen hani da kuma umarni. Yaro ya tsoma hannun hagu domin cin abinci, sai aka hana shi; wato aka dakatar da shi daga cigaba da amfani da hannun hagu. Sannan aka gaya masa; wato aka umarce shi da amfani da hannun dama.

══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════Lura/Kula: Lura ko kula, suna ɗaukar ma’anar saka ido a kan kai-komo na yaro; wato zirga-zirgar yara. Wannan hanya ta lura, cikamakonta shi ne kwaɓa. A nan, iyaye za su saka ido sosai game da zirga-zirgar ‘ya’yansu, duk lokacin da suka ga wata baƙuwar halayya maras kyau, sai su yi maza-maza su ɗauki matakin da ya dace tun kafin ta zama jiki.
Da zarar yaro ya fara fita wajen gida domin zuwa makaranta; wato daga shekaru uku zuwa sama, to fa dole iyaye su riƙa lura da shi sosai, saboda yanzu kuma ya je ya gwamutsa da sauran yara daga gidaje barkatai. Saboda haka idan iyaye basu saka lura ba, to tarbiyyar ‘ya’yansu sai ta koma barkatai.

═════ ❁✿❁MATAKAN TARBIYYA══════ ❁✿❁

Dasunan ALLAH Mai RAHAMA Mai JINKAI.
Haqiqa tarbiyya dolece a addinin mu na musulunci musan man ma na iyalanka/ki
Domin ALLAH MADAUKAKI yana cewa:

ﯾﺎ ﺃﯾﻬﺎﺍﻟﺬﯾﻦ ﺁﻣﻨﻮ ﻗﻮ ﺃﻧﻔﺴﮑﻢ ﻭﺃﻫﻠﯿﮑﻢ ﻧﺎﺭﺍ ﻭﻗﻮﺩﻫﺎ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻭﺍﻟﺤﺠﺎﺭﺓ
Awannan aya ALLAH yayi umarni ga Muminai dasu Kare kansu da iyalansu daga wata wutta Wanda yakasance makamashinta mutane ne dakuma duwatsu.
ALLAH UBANGIJI katsaremu amin ya RABBI. Awannan ‘Bangaren Nakeson nayi rubutu domin yan uwa musulmai su anfana.
ALLAH MADAUKAKIN SARKI ya dafamin.

══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════MATAKIN FARKO
(Neman Aure zuwa da yakai 5yrs)
Dole Akan kowa Idan yazo neman aure
Yanemi Mai addini Da hali nagari Da kakkyawar zuciya. Ba kawai kyawun fuskaba ko wani martaba ko nasabar Abokin zama ba. Kuma yazamto anyi auren tanasonsa yana sonta.
Domin hakanne Zaisa suji dadin zamantakewarsu ta Aure Kuma hakan Zaisa yayansu sutaso dason junansu Da Bin doka ko umarnin Da akayi masu. Domin kada yazamto uwa tace fari uba yace Bahakaneba Baki yake. Bayan haka
Yazama dole asakawa yaro kakkyawar suna alokacin dayake jinjiri. Yazama dole ka karantar Da matanka tsarin tarbiyyar addinin musulunci ko kasa akarantar da ita Awannan sahar kokuma MA kafin wannnan lokacin. Ma’ana kafin ta sami d’a (yara).
Domin kaso saba’in Cikin Dari (70%) Na Tarbiyyar cikin Gida maqasudinsa na uwace. Yazama dole takasance Mai Lura da Meke gudana me sukeso me yakamata suyi ko so Bari duk wadannan uwace takeda hakkin koyar da yaranta.
Dakuma koyardasu Ibaadaat Kamar Sallah Azumi Dakuma koyamusu karatun Alqur’ani da tilawarsa dama haddarsa. Har sukai 10yrs Kafin daga bisani Sai Aturasu Islamiya. Sucigaba da karatu daneman ilimin addini. Hakan zaisa sutaso da ganin girman iyayansu. Dama duk wanda yagirmesu tayadda basai ance ga malam waneba kafin sudaina abinda sukeyi.

══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════MATAKI NA BIYU
(Daga 5yrs zuwa 15 to 18yrs)
Dolene akan iyaye su San abokanan yayansu, Susan Kuma menene alaqarsu dasu Domin duk kyawun tarbiyyar dakasamu agida abokai sukan wargazashi, matsawar dakayi abota da marasa tarbiyya koda baka zama tamkarsu ba. Zaka rudu da wani hali acikin munanan halayyarsu.
Yazama dole iyaye su bawa yayansu tarbiyyar addini da wayewar rayuwa tahanyar sanaddasu yadda zasuyi addini da hikimomin tsara rayuwa bisa kykkyawar tsari. Kamar koyamusu dabarun kare kai da addu’o’in neman tsari da kariya. Da sanardasu tarihohi Wanda zasu sami hikima da, wa’azozi acikinsa. Domin abinciken masana kwakwalwar dan adam sun yarda akan cewa kwakwalwar dan adam takan bude da adana bayanai alokacin da mutum yake dan shekaru takwas (8) zuwa Sha biyar (15) koda haddane mutum yafi nutsuwa dashi awannan lokacin Inhar kaga yaro ya natsu awannan lokacin to tabbas ana kyautata zaton shiryayye ne. Inkuma ya kangare kuwa yanada wuyar shiryuwa Yakamata iyaye sudunga zama da yaransu suna zantawa dasu domin suji damuwoyi da bukatunsu, Harsu san tahanyar da zasu bullo musu gurin bada shawara ko kore musu matsalarsu tarayuwa.

══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════MATAKI NA UKU NAKARSHE
(Daga 15/18yrs. zuwa auraddasu)
Yakamata iyaye su lura da yayansu su san menene wane/wacce tafi/yafi kwarewa akai saisu dage gurin nema masu mafita ta hanyar basu tallafi ko jari domin samun damar gudanar da harkokin rayuwarsa cikin sauki batare da yana zauneba saidai kullum abashi.
Domin hakan yana kashe zuciyar mutum yazanto baya iya kafuwa da kansa balle ma har yagina wasu. Saidai kullum a bani_bani sai kuma bin abokai da yawace yawacen banza da hofi, da bin bangar siyasa, wadda daga karshe ke jawo mutum yakoma ta’asa da ‘barna acikin al’uma kokuma ma yakama shaye_shaye da bin mugaye mutane. Duk adalilin rashin aikin yi. ALLAH ya tsaremu da zuri’armu baki daya.
Rashin aikinyi na daya daga cikin abubuwa mafi girma wanda suke lalata tarbiyya arayuwar mutane.
Allah ka bawa iyayen mu hakurin zama damu kasauke musu hanyar dazasu tarbiyyantar damu tarbiyya ta Addinin musulunci, ALLAH kajikan maifina kahaskaka qabrinsa.

`YAN UWANA MATASA!!! MU KOMA GA ALLAH
══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════

   Rayuwar Matashi abin tausayine, Kana fama da Quruciya Ga kuma bakin Al`uma akanka. Idan za`afadi Damuwar Al`uma Dari, Kaso  Chasa’in da Biyar (95) Na Matasa ne.
         Qalubale Garemu Matasa, Ban cire kainaba domin nima cikin Quruciya nake.
Tabbas Muna Fuskantar Qalubalen rayuwa daga ´Bangaren zamantakewa, Har da Ibada. Saidai Raunin zuciya kuwa ya danganta da Yadda mutum yataso, Wahala ko Qunci, Tarbiyya ko Akasin hakan (Garari), Riskar iyaye da Rai ko Tashin Maraici. Idan Kasamu yin Makaranta Fani’ima (Haka akeso) In MA bakasamu ba Kaidai kada Kabar Neman ilimin Addini Domin Shidin Yalwatacce NE. Ako Ina akwaishi Amma kayi Takatsan_tsan Maluman da  Kake Saurara. KADA kabi Maison Zuciya.
Dukkan Wadannan Matsololin Rayuwa ce, Kirata Agaremu Shine, Mugane inane hanyar tsira kuma mecece mafita ta rayuwar mu, Ina Muka fito, Ina Zamuje, Me zamu Riska, Ina Tafiyar zata Tiqe?

MATASA BAYIN ALLAH NE
══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════

Kada Mushagaltu da Rudin Rayuwar duniya, Ko kuma Yanayin juyin Rayuwa yasanya Mu ´Bata Rayuwar mu da Shaye_shaye, ko Ta`addanci, ko Daba, Da zama `Yan Iskan gari.
       Mugyara Rayuwarmu tahanyar kaucewa had`arurrukan da Suka shafi aikata Munanan Laifuka, Mutuna Cewa Allah yake bada arziki, kuma Shike bada lokaci dakuma damar Amfanar Arzikin namu. Zamu iya tarawa ahanyar ‘Barna (Haram) Amma mu mutu, bamu ciba kuma Hisabinta Nanan Akan mu.
Zamu iya shiga Matsalar Rayuwa, Mugur´bata Rayuwar mu da Shaye_shaye ko garari Sanadiyyar wani, ko wata Mattsala, Mun manta cewa ga Allah za a koma kuma akwai hisabi, Shifa Allah ako ina Mukayi kuka Yana jinmu. Idan Ka Shiga Mummunar Hali Mu tuna da ALLAH. Sannan Mu dunga Yawan Ambaton Allah d`in kada Muce zamu Sha kwaya, ko Mu Kunna Sigari, Yi Hakan kamar An watsa maka Kashine ka Wanke da Kwata. ‘Barna bata Kawar da ‘Barna.

Mu waita yin Istigfari, Wata Qila Jarrabawace ta Yawan zunubin mu, Allah yakeso ya kankare mana. Allah ya yafe mana Yakuma ´Dauramu akan Shiriyar Addininsa, Yakuma Tseratar damu daga Tabewa da Halaka, Allah ka Albarkanci Iyayenmu, da Malumanmu, da Yayunmu, da Kannen mu, Damu kanmu, Wadanda Suka Rasu a Gafartamasu Musamman Mahaifina Allah kajikansa Da Rahama

KUYI TARBIYYAR ZUCIYOYIN ‘YA’YAYENKU DA ‘KANNENKU!!!
══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
══════ ❁✿❁ ═══════════ ❁✿❁
Zaku gyara Ahaliku Masu Zuwa
══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════

      Malaman Tarbiyya Sukace Idan Yaro yana ‘karami Daga Haihuwarsa Har Yakai Shekaru Bakwai (7), Ba’a Dukansa Ko Yimasa Mummunar Tsawar Dazai Ta’ba Zuciyarsa Domin Awannan Lokaci Yanada raunin  Zuciya. Sannan Dolene Yazama Ana Kula dashi ta Dukkan Yadda Zai Shiga Ko Fitarsa Sannan adunga Kyautata masa Suturarsa Ma’ana Kada Adunga  Sanya Masa Sai Sutura ta Mutunci Da Kamala, Kuma Dolene Iyaye Sudinga Sa Ido Akan Ayyukansa Da Yanayin Kitsonta Ko Askinsa.
     Bugu Da Qari Iyaye Dolene akansu Sudinga Lura da  Yanayin Himmarsa Abangaren Sana’a Ko Karatunsu, Hakazalika Awannan Lokaci Ba’a Barinsa Yayi Ko Tayi Tafiya Mai Nisa! Wanda Zaizamo an Wuni Ba’a Ganshi Ko Anganta ba, Saidai Idan Makarantane Domin Sunce Awannan lokaci Yaro Kamar Sarkine Ko Shugaban Kasa Tsakaninsa Shi Da Iyayensa, ( Shine Sarki Iyayensa Fadawansa).
   Sannan Sukace Idan Yaro Ya Haura Shekaru Goma (10 Yrs): Babu Laifi Za’a iya Dukansa Idan Yayi Laifi Mai Girma Amma ba Dukan Dazai Cutar da fatarsa ba ko Yadugunzuma Zuciyarsa ba, Kuma Dalilin Dukansa/tan Zai Zamo Daliline Na Ana Ladaftar dashi Bawai Anayi bane Domin Abata ransa, ko Dan Abata Ran Mahaifansa Ba. Idan Har Antarbiyyantar Da Yaro ma Daga Farko Da Lallami Sukace ”Zaiyi wahala Yazama Sai Andakeshi Kafin Ya Ladaftu” Wai Kafin Yayi Abinda akeso.

  Idan Kuwa Yaro Ko yarinya Sunkai Shekaru Sha Biyar Zuwa  Sha Shida (15–16), To Awannan Lokacin Yazama Abokin Hira Da Abokin Harka, Ma’ana Za’akoyar dashi Sabgogin Rayuwa Kamar karfafashi Abangaren Abinda yafi Karfi Na Karatunsa Ko Sa’ana Ko Dukkansu, Sannan Idan macece do Dolene akoyarda ita Kula Da Dawainiyar Gida Da Hidimar Daya Shafi abinci dadai Wasu Hidimomin Dasuka Shafi Rayuwar Gida, Sa’annan Yana dakyau Iyaye Su Dinga Shawari Dasu Awannan Lokacin. Domin Tantance Zurfin Tunaninsu Da Hankalinsu, Kuma hakan zaisa suma idan suna Bukatar shawara Suma Suzo Garesu, Domin Sunsan Iyayensu Suna girmama tunaninsu Kuma Suma Suna Nemansu Da Shawarwari, Idan  Har Iyaye suka Kuskure Awannan Lokaci To Tabbas Zasuyi Asarar Kaso Mafi Yawa  Na Morar ‘Yayansu, Domin Awannan Lokaci ne ‘YA’YA Suka Fara Fuskantar Dawainiyar Rayuwa Wacce take Iya Zama Nasara Ko Akasinta, Kuma Awannan lokaci Suke Bukatar Anusar Dasu Ahanya Domin Samun Ingantacciyar Rayuwar Da Suma Zasu Tarbiyyantar Da Wasu.

      Awannan Lokaci Kuma Ana Bukatar Iyaye Sudinga Nusar Dasu D a Nasiha, Ba Mummunar magana Hatta Daga Yayu; ( Ba Tir, Allah wadai, Allah tsine, Kayi/kinyi Asara, Allah Ya’isa) Dolene Yayu Da Iyaye Su tsare Harsunansu Daga furta irin Wadannan kalmomi Da Makamantansu Ga ‘Ya’yansu, domin Suna Tasiri Wajen Tarwatsa Rayuwar Yara Duk Tarbiyyanda Suka Samu Bazai Anfanesuba, Zaicutar Dasu Kuma Yakan Shafi Dukkan Sashin Rayuwarsu, Abinda yadace Na Furuci Tsakanin Iyaye Da Yara Ko Yayu Da Kannensu Sune: Sanya Albarka Da Yafiya Da Abinda Zai Faranta Rayukan Juna, Kada Kuyi Sakaci Da Neman Afuwar Juna Dakuma Yafewa Juna Hatta Idan ma Ba Laifin Da Ya Bayyana, Domin Yafiya Tsakanin Iyaye Da ‘Ya’yansu Ko Yayu Da ‘Kannensu ( Man Motan Nasara Ce) Matukar Babu Shi Nasarar Yara Bata Samuwa.

  Daga Karshe Nasiha ta Ga IYAYE Da YAYU Amatsayina Na ‘Da itace;
Dan Allah IYAYE Kuriqemu Amatsayin Amana, Sannan Kusani Sakacinku Damu Zai Iya Kailu Wuta Dukanmu Subhanallah, ALLAH yakare! Kusani Awannan Zamanin Dolene Iyaye Da Yayu Sudinga Lura Wayoyin ‘Ya’yansu ko Qannensu, Haka Kwatsam Kace Wane/Wance; Bani Aron Wayarka Ko Wayarki Ka/ki Ciremin PinCode d’in, Kada Kuji Nauyin Hakan inkunyi Sakaci Kuwa Lahirarku ce Da Tamu Zata ‘Baci, Subhanallah Kada Muzo Alahira Muna La’antar Juna! Wa’iyazu BILLAAHI!!!
Allah Yatsare.
══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════
✍️Ismail Hussaini Alpholtawy
══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════

MU KIYAYE ALLAH NIDA KU

Ismail Hussaini Adam

Bazamu Kauce Shari`ah Ba
Duk Wuya Bazamu rabe ba
Kunci Bazaisa Mu Sarye ba
Balle Wuya ba Mutuwa ba
Duk Rintsi Bazamu Rabe ba

Dan Arzikinka Ga Bayi Allah Tabbatar Mana Alkhairinka

Duniya Ba`a Zauna ba
Rayuwa ba Mutuwa ba
Zamani Ba Namutum ba
Arzikin ba Nakun ba
Iyawuya Ninakine Zainaba

Ya Zul jalalu Kaduba Isarmu Kabamu  Iyawar dan Tasirinka

Dafamana ya Rabbana
Ka iyamana ya Jalla na
Da Isarka ne Khaliqa na
Rayuwarmu Arzuq Na
Bi Izzatuka Ya Ahya Na

Ka Nuna Isarka Cikin Ayyukan Bayi Ka Tabbatar Da Samuwarka

Ya Arhamrrahimina
Ya Alimul Alamina
Ya Khairul Munzalina
Ya Fatihul Raziqina
Ya Alimussirruna

Alhayyul Qayyumu Bamu ikon Tuba Kayima duniya da Lahirarmu Tsari Ya Mai Tsarkin Tsarkaka

MATAN ZAMANI AYI HATTARA

  Duk iya Gyaran Bakanike Bazai Iya Maida Tsoho Izuwa Sabo ba, Komai Zaiyi Lallabene.

“Babu wanda zai so siyan abu sabo a kwali sai yaje gida ya bude ya tarar duk ya koke ko kuma yaga wani alamu da ke alamta cewa wani yayiamfani da abun kafin shi.

Wani zai iya daurewa ya cigaba da amfani daabun a haka amma ba da daďin rai ba,wani kumazai fusata ya mayar da abun inda ya siyo ne donyaji dalilin da zaa sayar masa da second hand amatsayin sabo,

Kada a rudu da rudin zamani don shi dai mutunci madara ne, don haka sai a kula!
Allah Ya shirya mu da zuri’ar mu gaba daya.”

Aishatu Bint Shafili

19 June 2021

  • Nasarorin Ƙungiyar Arewa Media Writers
    Nasarorin Da Ƙungiyar “Arewa Media Writers” Ta Samu Cikin Shekaru… Read more: Nasarorin Ƙungiyar Arewa Media Writers
  • TARBIYYAR ‘YA’YA AMUSULUNCI
    ══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════TARBIYYAR ‘YA’YA AMUSULUNCI══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁… Read more: TARBIYYAR ‘YA’YA AMUSULUNCI
  • ZATIN UBANGIJI
    SHAUQI CIKIN AL AMARIN GAIBIYYA Kasantuwar Ubangiji A Buya Bai… Read more: ZATIN UBANGIJI
  • GODIYA TA GA ALLAH BUWAYI
    Ban Shan Sigari Ban Shan MoringaBan Shan 200 Kayan zamani… Read more: GODIYA TA GA ALLAH BUWAYI
  • KUJI TAUSAYIN MARAYAN ALLAH
    Bansan me Nayi mussu baNufata da Sharri suke basu barniba… Read more: KUJI TAUSAYIN MARAYAN ALLAH
  • FASAHAR ZAMANI
    Menene capacitor?  Dauki masu gudanar da wutarlantarki guda biyu (abubuwan da suka bari Wutarlantarki ta ratsa su) sai ka raba su da insulator(kayan da ba su barin wuta ya ratsa sosai) sai kayi capacitor: wani abu da zai iya adanamakamashin wutar lantarki. Kara makamashinlantarki ga mai iya aiki shi ake kira caji ; fitar dakarfin daga mai iya aiki shi aka sani dadischarging. Capacitor yana dan kama da baturiya, amma yanada wani aiki daban. Baturiya na amfani dasinadarai don adana makamashin lantarki da sake shi a hankalita hanyar zagaye; wani lokaci (a yanayin agogonkwata) zai iya daukar shekaru da dama. Mai iyaaiki yana sakin karfinsa da sauri-sau da yawa acikin sakanni ko kasa da haka. Idan kana daukanhoton flash, misali, kana bukatar kyamararka don samar da babban burst na haskea cikin fraction na sakan daya. Wani mai iko daaka hađe da bindigogin flash na ‘yan sakanni taamfani da makamashi daga batirin kyamararka.(Yana daukar lokaci kafin caji capacitor shi yasayawanoci dole ka jira kadan.) Da zarar an caji maikarfin, zai iya sakin duk karfin nan take ta hanyarxenon flash bulb. Zap! What is a capacitor?Take… Read more: FASAHAR ZAMANI
  • MU KIYAYE ALLAH NIDA KU
    Bazamu Kauce Shari`ah BaDuk Wuya Bazamu rabe baKunci Bazaisa Mu… Read more: MU KIYAYE ALLAH NIDA KU

HANYAR KUTSE TA SIYASAR YAHUDAWA

Alpholtawy

  • May 20,2021
  • Gabatarwa Dukkan Yabo ya Tabbata ga Allah ﷻ Wanda yayi Rana, Da wata, yayi Halittun Duniya da Dukkan Abinda Yafaru Iyawarsane. Muna yabamasa, Muna Godiya Agareshi, Daya Sanyamu Cikin Aluma wacce take Mafificiya. Wacce tazamo Mafi daraja daga Cikin Alumomin da Allah Yake Sanyawa adoron Kasa, Karkashin Manzo Mafi Daraja Cikin Manzanninsa Mafiya Daukaka Annabi Muhammadﷺ . Muna Godemasaﷻ daya Sanyamu Musulmi Kuma Masu Kokarin Neman Sanin Gaskiya Dakuma Bincike Akan abinda Zai Zama Hanyar Tsira Agaremu. Bayan haka; hakika Ban Wallafa Wannan Rubutu nawa Domin Cin Zarafin Kowa ba Sai Dan Fayyace Haqiqanin Abinda Allah ne Yamana Ishara Cikin Littafinsa Mai Tsarki Karkashin Ayoyi dayawa Amma Zangina Rubutuna akan Wannan ayoyine Guda biyu Wadanda Suke Bayani Karara Akan Siyasar Dunya watau Dilomasiyya Fadisa Yahudu da Nasara Basa Yarje Muku Harsai kunbi Tafarkinsu Dakuma Fadinsa ´´Bazasu Gujeba Suna Yakarku Harsai Kunbar Addininku Insun Samu IkoAmma Kuma Ubangiji Yafada mana Wadanda Suka Fi Gaba Da Musulunci Dakuma Wadanda Suke da Sassaucin Ra`ayi Inda Yake Cewa ﷻ ´´Zakasamu Mafiya Kusancin Soyayya ga Wadanda Sukayi Imani, Sune Wadanda Suke Riya Cewa Lallai mune Nasara Saboda Acikinsu Akwai Malaman Qissisin da Ruhban Wadannan Ayoyi da Makamanatansu Sune Babban Abinda Zagina Maqala ta Akai, Haqiqa Ubangiji ﷻ Shine ya Sansu, Kuma shidin Yafimu Sanin Halayemsu, Shiyasa Shi da Kansa Yake Bayyana Mana Halinsu, Kuma Yayimana Gargadi Akan cewa kada Muyarda Mubi Tafarkinsu, Domin Sudin Daga Wadanda Ubangiji Yayi Fushi dasu Saboda Kin Aiki da Gaskiya ne, Sai kuma Batattu Wadanda Suka Ki Sunemi Ilimin Da Zasu Fayyace Gaskiya, Wannan Shi Yahukumta Dolene Kanemi Ilimi, Kuma Dolene Kayi Aiki Da Iliminka Wajen Neman Lahira, Inkuwa Baka nema ba Bakada uziri agun Ubangiji, domin Yafada mana Kuma Inkasamu Bakayi Aiki bama, Shima Qalubalene Domin zai iya Zama Hujja akanka, Fatanmu Ubangiji Yabamu Ikon Aiki da Ilimin da Yabamu Yakuma Bamu ilimi na Tsoronsa da Aiki dominsa Yahore mana Sanin Gaskiya Da Aiki Da Ita. Mawallafi ✍️ Ismail Hussaini Alpholtawy Website alpholtawy.jw.Lt Tsikaci; Banyi Wannan Rubutu Domin Cin Zarafin Wani ko keta Mutuwacin wataba. Nayishine Domin fahimtar da Wasu wadanda Suka Jahilci Lamarin Diplomasiyya Na Yanzu, Tayadda Aka kasa gane Menene manufar mamayar Turawa Dakuma Illar dasuke Jefawa Al’uma, Misali Mafi girma Irin ‘Barnar rayuka dasuka haifar a Gabas ta Tsakiya dasunan Rikicin Aqeedah dakuma Addini. Lamarin Zai Karene Akan Gida Kuma Yankinmu Africa Tayadda Suka Maidamu Bayi Kuma Suke Sa Muna kashe Junarmu Domin Biyan Bukatunsu.
  • MAQALA TA FARKO Bayanin Suwaye YAHUDAWA
    MAQALA TA BIYU Kutsen YAHUDAWA a Gabas Ta Tsakiya
    MAQALA TA UKU Illar dasuke Yiwa Larabawa Na Mulkin Kama Karya
    MAQALA TA HUDU Illar Dasuke Yiwa Africa Ayanzu
    MAQALA TA BIYAR Hanyoyin dasuke Bi Don Kutsewa Duniya
    Zanyi Bayaninsu Daya Bayan Daya INSHAALLAH Inafatan Mai KARATU Bazai Gajiya ba, Zan takaita Rubutun Nawa Domin Ina Sanyawa A Social Media Dan yazama nasayashi a Post Guda Daya.
    MAQALA TA FARKO
    Bayanin Suwaye Yahudawa Dukkan Mai bibiyan Tarihi Kokuma Wanda yake Karanta ALQUR’ANI Basai Anyimasa dogon jawabi ba, Yasan YAHUDAWA Sufarsu Ahali Saidai Ayanzu Idan Zamu Nemi Saninsu Zamuce Mutanen da 👉Hitila Ya Yakesu 🔥. Wad’anda Ayanzu Sukafi Rayuwa awadannan Kasashen kamar Haka; US, UK, Canada, France, Germany, Italy, Portugal, Turkey da sauransu. Wad’anda Suke a Yammacin Duniya Kuma Suna da Karfin Iko Tayadda Yazama Kaso Saba’in da Biyar Cikin Dari (75%) Na duniya Su Suke juyata Da ikonsu na Salon Mulkin kama Karya Dakuma Zalnci Hakan yafaru ne Dalilin Mugun halinsu Na Tusa Talauci Da Ta’addanci Wa Dukkan Kasar dasukaga Zata yimusu Tawaye Harsai Sunkarya Daukarta. Mai Karatu Na iya Tambaya Shin Menene ikonsu Da Gadara? **Amsarka itace:— Sunada Karfi Iko aduniya Sunada Kudi Wanda Sunhada Wad’annnan Abubuwane tahanyar Tanadin da Suke fata na Kare Kansu a Yaki Idan ta fado Musu domin Gamai bibiyan Tarihi yaji Yadda aka Tarwatsamusu Daula A Yakin Duniya ta Biyu akayi Kusan Karar Dasu Adoron Kasa. Wannan Dalili yasa Suka kulla kawance da Junansu Suka Kuma fara Tattali da Tara Makamai da Kutse Cikin kowace Al’uma domin Suyada Kansu aduniya Dan Subazama Takowani Shashi, Suna da Qungiyo Ayanzu kamar haka; 👉NATO (North Atlantic Treaty Organization 👉CSTO (Collective Security 👉G7 (Group of Seven) 👉EU (European Union) Sannan Suntara Makamai Ba Adadi Sunada Karfi Fiyeda sanin ‘Dan Adam, Kuma Zasu iya Tunkarar kowa Aduniya, insuka farwa kasa To ALLAH ne Kawai Gatanta Amma Babu Mahaluqinda ya isa Yatsayar musu Da Aniyarsu Sai ALLAH Saikuma In Ansamu Masharranta Irinsu. Muna Rokon **Ubangiji ** yatsaremu daga Sharrin YAHUDAWA.
    MAQALA TA BIYU
    Kutsen yahudawa a Gabas Ta Tsakiya Wannan Maqalar zata iya Zama izina kokuma nace Hannunka Mai Sandan ga Hukumomi Dakuma Shugabannin Africa. Haqiqa Larabawa Sundauki YAHUDAWA amatsayin Aminai Kuma Mataimaka, Wanda Aminci yakai alakar Auratayya Tashiga Tsakaninsu Tayadda Suna Auren juna Kamar Yadda Addinin Musulunci yasawwaqe. Tofa Saidai Awannan zamanin Juyin Yanyi Yacanza al’amuran, Tayadda Yahudawa Suke Amfani dawannan HANYAR Suna Sanya Gaba da Tsanar juna Wa YAHUDAWA Tahanyar Cusawa ‘ya’yansu mata Suna Koyamusu Yadda Zasu Sanya Mijin Daya Auri Bayahudiya Yakori Dansa Ko Kaninsa kowani Nasa Wadda Yake Karakashinsa Saboda Sharri irinna Matayen YAHUDAWA dasuka Auro, Kuma hakan Koyine daga Iyayensu domin Acewarsu Hakan Shine Zai fara Karya Daular Larabawa Domin Awannan Lokacin babu Daular datake Qalubale agaresu kamar Larabawa Domin Sunfi Kusa dasu kuma Sune Al’uma mafi yawa Awannan Lokacin. Wannan Shine Farkon Faruwar Rushe Daular Larabawa.
    ,MAQALA TA UKU
    Illar dasuke Yiwa Larabawa Na Mulkin Kama Karya Bayan Sun Karya Karfinta da mata Sai kuma Suka Fara Yakar Tattalin Arzikinta Tahanyar Yanke Huldar Kasuwancinsu da Kasashen Duniya. Ga GA’bar Tambaya! Taya Zasu yanke Huldar Kasuwancinsu da Kasashen Duniya? Amsar mu Anan itace;— Sunyi Amfani da Wasu ‘Yan Gidan Gofnatin da Larabawa ke Mulka Wad’annan Wad’anda Yayunsu da Iyayen Gidansu Suka Kora Sukayi Amfani Dasu Wajen Kirkiran Qungiyoyin Ta’addanci domin Suyi Kamfen din ‘Bata Wannan Daular datayi Sanandin Barinsu Gari daganan YAHUDAWA Suka Karfafa Wad’annan Qungiyoyi na Ta’addanci Suka Taramusu Kudade da Makamai Suka Dinga Ruguza Al’uma Gefe Guda Kuma YAHUDAWA Suna Shigowa Suna Bada Magunguna Masu Illa Dasunan Tallafi Suna Kashe Al’umar da Gubar magani ‘yan Ta’adda sunayi Da Bindiga da Bomabomai. Sannan A’bangaren Gofnati Sunshiga Da Zimmar Zasu Taimaki Gofnatin Amma Suna bata Bashin Makamai Sannan dahakan Sukayi Amfani Suka karya Wannan Daular Suka Ruguza Himma da Mafarkin Wadannan Shuwagabannin Har ila Yau Kasashen Larabawar Gabas ta Tsakiya Suna Cikin halin Tausayawa da Alhini da Kuncin Rayuwa da Halin Tausayawa
    . MAQALA TA HUDU
    Yadda Suke Wanzar da Shirin Kutse Cikin Al’umar dasuke So! Suna yin Wannan ayyuka nasune tahanyar damuka ambata abaya, da mata Dakuma Tsirar da Tsiro na ‘Yan Ta’adda daga Cikinku Wanda Hakan Zaibasu Daman Saida Makamai Akasarku, Tayadda Zasu Sami Damar Shiga Gofnatin Kasarku daganan sai su Karya Tattalin Arzikin Kasarku. Sannan Daga Baya Suma Sufara Shigowa suna Baku Guba dasunan Magani. Tabbas Akwai Wani Mummunar aiki Wanda YAHUDAWA Suke Shiryuwa Wanda Wannan Tafi Shafan Wad’anda Suke Musulmi Domin Acewarsu Bisa bincike dasuke Aiwatar wa ”Nan Da ‘yan Wasu Shekaru Duniya da Mulkin ta Zaikoma Hannun Musulmi Wannan Dalili Yasa Suke Kirkiran Wasu Qungiyoyi Wad’anda Suke Fada da Rusa Tsarin Musulunci Dakuma Hadin kansu Dama Uwa uba Tunkud’esu Akan Turbarsu ta Imani Da Ubangiji ALLAH izuwa Ga Bautan Aljanu da Kaucewa Hukumcin Ubangiji Izuwa Hukumci na son Zuciya Maras Tushe Da Asali. Tambayar dayakamata Me Karatu yayi; Taya Suke Aiwatar da Wad’annan ayyuka kuma me Suke So Su cimma kuma Menene Qungiyoyinda Suke Kirkiran? Suna Aikinne Kaitsaye Domin Rushe Bautar Ubangiji Dakuma Hani akan Aikin Da Littattafan Ubangiji Sannan, Domin Burinsu Sumulki Duniya Amma hakan Bazai yiwuba Matukar Mutane sunada Tsarin rayuwa Da Addini Domin Hakan Zaihanasu Samun Cikakken iko Dakuma Dama, Saboda Haka Aikin da Zasuyi nafarko Shine Raba Mutane da Addini, Ba Musulunci kadaiba; Dukkan Addinin dasukaga yanada Littattafi Burinsu Su Sanyawa Mabiyansa Rauni Tayadda Zasuyi Amfani da Matsalolin Aqidar Addinin Suhaddasa Rigima daga Baya kuwa Su fara Yiwa Malamanku Kisan Gilla dasunan Suna kawo Sabanin ADDINI.
    MAQALA TA BIYAR
    Kammalawa da Bayanin Hanyoyin dasuke Bi Don Kutsewa Duniya Dukkan Godiya ta Gabbata Ga Ubangiji Mahalicci, Mai Hukumci Bisa Adalci Mai Karamci Baya Butulci Sassauci Baya Ha’inci. Masani Mai Bada Kyautar Komai Mai Yadda Yaso Ayanda Yaso Ko Anaso Ko Ba’aso, Salati Da Aminci Sutabbata Ga Shugaba Ja Gaba Mai Martaba Annabi (S. W. A.) Da Iyalan gidansa mataye da Yayayensa Da Sahabbansa Ubangiji kayimusu Aminci Aminci mai Yawa. Bayan Haka Wannan Maqala Itace ta Kammalawa Kuma Zankara Haskamana Wasu Abebenda Zamu kara Lura Dasu Muma Mudau Izina Sannan Mukula DA Sha’anin YAHUDAWA Dakuma Kokarin Gujewa Turbarsu ta Munafurci Dayaudara.
    👉Muyi Hakuri da Junanmu muna Tsayuwa Domin Neman Fahimtar Juna Yayin Rikicin Addini ko Qabilanci. 👉Kada Shigar Tsaraici Na Matan YAHUDAWAn Yamma ya rudeka Ka Kwaso Bala’i Wa Kasarku. 👉Kuyi Kokarin Koran Tsarin Rayuwarsu DA Al’adunsu Na Dabbanci Kuyi Hukumci da Littattafanku. 👉Kutabbatar Kuna Rike DA Tarihin Duniya Awulkanci Wani Lokaci idan Fitina Ta Auku Ku Nemi Maslaha daga Tarihin Al’umomin Bayanku. 👉Kada Kubar ‘ya’yanku Akasashen Turawan Yamma Kawai Suna Karatun Boko Batareda Koyar Dasu Addini ba. 👉Kutabbatar Kuna Kwatanta Aiki Tsarin Addininku Domin Gujewa Sa’banin Zamani. 👉Kada Kukarbi Wani Tallafin Magani Ko Abinci Daga Garesu Harasai Masana Daga Kasarku Sun Tantance. 👉Kada Kuyarda Kukarbi Bashi daga Garesu Duk Matsin Rayuwa Saidai Idan Zakuyi Trade By Barter. 👉Ku Sanya Masana Akan Dukkan Wasu Muqaman Gofnati Ba Jahilaiba Kuma Masu Addini Ba ‘Yan Duniya ba. Akwai Dalilai Dayawa Amman Zantsaya Anan Domin Kada Rubutun Nawa Yazamto Najashi Yayi Yawa Anan Nake Cewa Daku Bissalam. Nine Naku Ismail Hussaini Alpholtawy

BAI JUYA MAKU BAYA BA!!! MU HUKUMTA JUNA BISA ADALCI

Sau dadama Wasu Zakaji Suna Korfin Cewa Wane Tun Sadda Yasami Wata Daukaka Ko Wani Cigaba ko Shugabanci, Shikenan Yamanta Damu Cikin Huldarsa Na rayuwa Da Tarayya!

Dafarko dai Shi Al amarin Cigaba Nufin Allah neﷻ,  Haka Kuma Aka Halicci Dan Adam da Rauni Na Mantuwa da Kuma Shagaltuwa da Al`amuran Duniya Da Mance Baya, Kuma Cikin Hikimar Ubangijiﷻ Wannan Al`amari Shima Nada Amfani Arayuwar Dan Adam Bisa Yadda Harkokin Rayuwa Ke Wakana Inbabu Mantuwa! Tabbas Dan Adam Bazai Samu Sukuni ba.

Kada Kazargi Wani Dan Yasamu Daukaka Da cewar Ya Gujeka Kazargi Kanka da Hassada dakuma Yanke Zumunci, Domin da zarar Mutum Yasamu Daukaka Al`uma Sun kara Yimasa Yawa Kuma Bazai Samu Damar Ji Da Kowaba dole Sai anayimasa Uziri, Kuma Kai me Raki Dolene Ka ziyarceshi Matukar Ba Hassadar Daukakarsa Kake ba, Inhar Kana Buqatar Zumuncinku Yacigaba.

Mudinga Yiwa Juna Uziri Muna Tuntubar Lafiyar Juna Mudaina basar da Junanmu Cikin Lamarin Rayuwa, Mu Sulhunta Junanmu Cikin Sabanin tunanani Ko Rashin fahimta, Muyawaita Yiwa Junanmu Fatan Alkhairi Da Nasiha.

TARBIYAR MATASA

•••°°°TARBIYAR MATASA°°°•••

Godiya ta tabbata ga ALLAH madaukakin sarki, Tsira da amincin ALLAH su tabbata ga fiyayen Halitta, kuma cikamakin ANNABAWA DA MANZANNI, shugabanmu Annabi Muhammad (SAW) da Alayensa da Sahabbansa tare da mabiya sunnah har zuwa ranar qarshe.
Bayan haka ‘yan uwana ina mai farin cikin gabatar muku da wannan muhadara wanda na sanya mata taken ★TARBIYAR MATASA★ badon wai na iya ba, ba kuma don nuna qwarancewa ba a’a kawai dai ina ganin ya kamata mu rinqa tattaunawa abisa matsalolin rayuwarmu ta yau da kullum.

•••WANENE MATASHI???•••
MATASHI shine (Almukallab) wato baligi wanda shari’a ta hau kansa, shine wanda idan yayi aiki Nagari za’a rubuta masa ladan aikinsa haka kuma idan yayi mummuna nan ma za’a rubuta masa abunda ya aikata acikin littafinsa.

°FARKON ABINDA YAKE WAJABA AKAN MATASHI° Farkon abinda yake wajaba akan matashi shine yayi imani da ALLAH ma’ana ya kadaita ALLAH shi kadai ya kuma shaida Muhammad bawan ALLAH ne kuma Manzon sa ne (SAW), kuma yayi imani da littatafanda ALLAH ya sauqar kuma yayi imani da qaddara mai kyau da maras kyau, kuma ya san da cewa akwai kwanciyar kabari akwai kuma tambayoyin cikin kabari akwai tashin alqiyama akwai hisabi akwai sakamako akwai tsallaka siradi, akwai wuta akwai aljannah. Kuma ya san cewa duniya gidan aro ce, lahira ita ce gida na gaskia ya kuma kyautatawa mahaifansa, kuma ya tsaida ibadarsa kamar yadda aka umurci dan Adam.

••TA YAYA ZAI ZAMA NAGARI GA AL`UMMA???••
Dole ne sai matashi ya kiyaye abubuwa muhimmai na rayuwa wa enda matuqar yana son ya zamanto matashi daga cikin matasa ingantattu kuma nagartattu, sai ya kiyaye addininsa, sai ya kasance mai Hakuri, mai ladabi, mai biyayya, mai neman ilimi, mai kauracewa alfasha, mai girmama na gaba dashi, mai tunani kafin aiwatar da wani abu mai neman shawara kafin gabatar da wani abu, mai sada zumunci mai yawan tausayi, mai gudun duniya, mai dogaro da kansa da neman abun kansa ta hanyar halak, wadannan abubuwa da muka lissafa sune zasu karfafa ★TARBIYAR MATASA★.
Ita dai TARBIYA ta samo asali ne daga tushen iyaye, Tarbiya tana ginuwa ne daga samun uwa tagari domin ita ke kasancewa makaranta ga ‘yayanta. Shiyasa Annabi MUHAMMAD (SAW) yayi umurni da a auri mace ma’abociyar addini domin kasancewar saita san addini sannan tasan yadda zata yi ta tarbiyantar da ‘yayanta.
A yau mun wayi gari Tarbiyar Matasanmu yana gur6acewa ta hanyoyi da dama a wannan zamani da muke ciki.★TARBIYAR MATASA★ tana samun matsala daga manyan mutane walau masu siyasa walau sarakuna ta hanyar amfani da matasa a wannan lokaci da suke yi na haddasa gaba da qiyayya a tsakani, da yin qoqarin aiki da matsa wajen basu makamai don kashe musu abokan gabansu wannan ba daidai bane. Ya kamata MATASA suyiwa kansu fada kuma su duba duk sanda aka umurce su da kai hari na kisa ba zaka ga daya daga cikin ‘yayan wanda suka tura su don ta’addancin ba, saboda haka mai zai sa su tsaya suna kashe junansu???, bayan ALLAH (SWT) yana cewa acikin suratul Anfaal: ( FATTAQULLA WA ASLIHU ZATA BAINIKUM WA’ADILLAHA WARASULAHU INKUNTUM MU’AMINEEN). Ma’ana:- (kuji tsoron ALLAH kuma ku daidaita tsakaninku kuma kubi ALLAH da Manzonsa idan kun kasance muminai)
Kuma ALLAH (SWT) ya qara cewa acikin suratul Hujurat :- (INNAMAL MU’UMINUNA IKHWATUN FA ASLIHU BAINA AKAWAIKUM WATTAQULLAHA LA’ALLAKUM TURHAMUUN). Ma’ana :- (su muminai yan’uwan juna ne don haka idan wani abu ya faru, to ku daidaita tsakaninku kuma kuji tsoron Allah ko a jiqanku) to saboda me matasa zasu rinqa kashe junansu.

•MATSALOLIN MATASA A YAU•
Yau an wayi gari MATASA sune shaye shaye, batsa duk wani abunda bayida kyau sai a samu MATASA ne suke aikata shi. Alal haqiqa ana samun iyayenda suke yiwa yaransu cikakkiyar tarbiya amma daga bisani sai yaran sufi karfinsu. Ba wani abu bane ke kawo haka illa zamantakewa na rayuwa a wurare guda (4) GIDA, MAKARANTA, KAN HANYA, ABOKAI wadannan abubuwa suke kawo illoli ga ★TARBIYAR MATASA★ a wannan qarni a wannan zamani da muke ciki.
Cudanyar Mata da Maza tana daga cikin hanyar lalacewar ★TARBIYAR MATASA★ musamman MATA zaku ga mace don tana ganin ta girma tana ganin tsayinta yayi daidai dana mahaifiyarta, tana ganin ta hadu da abokai na banza masu fure mata kunnuwa, to wallahi ki sani duk wani taqama da kikeyi a rayuwa da sanya damammun kaya masu fidda surorinki a bayyane tare da yin tozo da kanki kamar tozon raqumi wanda ake qira da a cuci gara saboda kina jin ke kin balaga kina jin tashe yana tashi a tare dake to wallahi kiji tsoron ALLAH. Domin Annabi MUHAMMAD (SAW) yace (Mata mafi yawansu ma’abota wuta ne, kuma Manzon ALLAH (SAW) Ya siffanta mata nau’i nau’i da ya gani acikin wutan jahannama, Wallahi Mata abun tausayi ne amma sai suka zama masu bijirewa baiwar da ALLAH yayi musu suka tsiri koyi da yahudawa da nasara. Abun mamaki wai Yarinya tasa Hijab har qasa ta fita sai kaji tace maka kunya take ji saboda tsantsar koyi da yahudawa.
Mafi yawan MATASA basa bada hankalinsu wajen karatun Addini kowa ka ta6a Boko, musamman mata zaku ga akan karatun boko tamkar zata kashe kanta, amma idan aka bincika wata zaka samu ko farillan al’awala bata sani ba, amma idan ka tambayeta Geography, Biology, chemistry zata yita kawo maka tamkar a qwaqwalwarta aka gina su, Haba Matasa !!!
Ina qara jan Hankalin ‘yan uwana Matasa dasu kiyaye Tarbiyarsu, su kula da rayuwarsu kada su shagala da wannan duniyar domin Annabi (SAW) yace: Duniya kurkukun Mumini ce kuma aljannar kafiri ce) Muslim ne ya ruwaito wannan Hadeeth din.
Kuma Manzon ALLAH (SAW) yayi qiran Matasa da cewa:- Yaku taron samari duk wanda yake da iko acikinku to yayi aure don yafi rintse ido kuma yafi kame farji, wanda kuma bai samu iko ba to na hore shi da yin azumi domin shi yana kashe sha’awa) (Bukhari da Muslim da Tirmizi da Abu Dawud da Nasa’i suka ruwaito wannan hadeethin). Ina Qara qira ga ‘yanuwana Matasa dasu kasance masu neman abun Hannunsu, ma’ana su kasance masu sana’a, domin fadin ALLAH (SWT) acikin suratul Naba’i :- (WAJA’ALNAN NAHARA MA’ASHA) ma’ana:- (Mun sanya muku rana domin ku fita ku nemi abinci). Kuma Manzon ALLAH (SAW) yace (ALLAH yana son mumini mai riqe da sana’a saboda ALLAH. Manzon Allah Ya qara cewa:- (Mafificiyar sana’a ita ce sana’ar mai akikin hannu idan yayi adalci) (Ahmad ne ya ruwaito wannan hadeeth din a musnadinsa).
Haka kuma bayani yaxo daga cikin Hadithin Abu-Huraira cewa an tambayi Manzon ALLAH (SAW) cewa wace sana’a ce tafi dadi??? Sai Manzon ALLAH (SAW) yace aikinda mutum yake yi da hanunsa da dukkan wani ciniki ingantacce (Ahmad ne ya ruwaito shi). Saboda haka ya kamata MATASA su kwadaitu ga yin sana’a kuma ayi sana’ar saboda ALLAH. Ina kuma qara qira ga ‘yanuwana matasa har da dukkan dan ‘adam da su guji KARYA, ZINA, SHANGIYA, ANNAMIMANCI, KASHE JUNA, GIBA (GULMA), RASHIN TAUSAYI, CACA, SON DUNIYA, YAUDARA da dai sauransu. Ina ganin wannan shine dan abunda ALLAH ya iyar dani wajen kawowa game da ★TARBIYAR MATASA★ ina kuma roqon ALLAH ya qara shiryar damu a bisa hanya madaidaiciya yasa muyi kyakykyawar qarshe.
Ina kuma roqon ALLAH dukkan abunda muka fada daidai ya hadamu gaba daya acikin ladan, abunda muka fada bisa kuskure kuma ALLAH ya gafarta mana daman ALLAH shine ya sani ba muba.

Daga:
Yar Uwarku
Faridah Bintu Salis
(Bintus~Sunnah)