GODIYA TA GA ALLAH BUWAYI


Ban Shan Sigari Ban Shan Moringa
Ban Shan 200 Kayan zamani Ban Leqa taga
Kayan Wani bai idona Ni nai ga Katanga
Shiga Sha`anin Wani banayi Cikin Garinga
Bana da Abokin Hamayya koda A Singa
Ni Ba Alfaharifa Nake Ba Sunce Banda Siga
Kawai Dan Bana Kula Mai haukar Marashin Balaga
Burina tarayya Damai Son Mutane ko a Daga
Komai Wuya Bai mantawa da Allah Garinga

Buwayi Jallah ne Yatsareni ga Dukkan Wauta
Shi ya Nufa Bana Daukan kayan wani Sata
Kuma Ya Horemin Baiwar Neman Azurta
Cikin Tsafta da Ilimi Babu Son Zuciyata
Meyakai Hakan Rabone ga Tambayata

Ga baiwa Basira nasam rabauta
Shin Wazai Samu Ilimi Kamata
Yakuma Tsarkaka ba Tozarta
DaSanin Falsafar duniyata
Cikin Nema Ba Qazanta
Kuma Yasan Hanyoyin Rabauta
Amma Dan Gudun Duniyata
Naki Duba Nai Nazarta
Da kyawun hali Ba Mugunta
Mutan Gari Na nufata da Cuta
Na Bisu da Kyawun Hali Mai tsafta
Kullum Cikin dare Har Safiyata
Bana Nufin Sharri dan Gabata

Matukar Jallah Yarubuta Zan Azurta
Ina Ruwana damai Duban Duniyata
Yai ta Qunci Cikin rai karya Huta
Yaitayi Dan Shine Zai Qaranta
Bamai Hanawa Koda da Cuta

Zasu barni In wala har na Huta
Duk Rintsi nafada Zan Azurta
Indai Buwayine ya Qadarta
Dan Shike Ayyada Qaddarata

Cikin Mafarki
Wallahi Cikin Mafarki Naganta
tana ta Raki
Tana fadin wai Nayi karatu Najita
Nabada Maki
Ahakan fa Nabata Maki na Sota
Taminni Kirki
Asalinta Naduba nayi Nazarta
So ne da Ba Raki
Asalin Furuci yasaka Nai Zumunta

Muryarta da Dad`i
Dana jishi Yasanya Na ´Dimauta
Nayi Matta Gargad`i
Abokina Nura Yagoyan Baya Gareta
Abin yasakani Zumud`i
Wallahi Da Murmushi fa Afuskarta
Dahakan naji Dad`i
Furucinta da Sanyi Nayi Nazarta

Zanen Zabo Da Shi Aka ganta
Kukan Kura Jawabi Najigata
Ra`ayin wani Babu Ni acikinta
Burina In Tabbatar da Halinta
Intana da Kirki Ni Zan Sota
Dama Na Ganta azahiri na Ganinta
Sannan Nafurta Abinnan na Huta
Na Kalmar Soyayya Zan Kirata
Sanna Nabita Da Furicin Qaunata

Na Yarda tana da Halin Kwarai
Domin na jita Garai Garai
Sannan Siffanta Sarai Sarai
Ba Mai Kinta Idan da Rai
Girma Zan Bata Cikin Tirai
Zafin Qaunarta idan da Rai
Zai Bi Jikina ya  Yata´b´ba Rai

Mai gaskiya Shi Ake gudu Awannan zamani

Mara Gaskiya madubin A’uma Oh na Bani

Indai Daranka Ayanzu kasha kallon gini

Wai Ta Tarbiya agidan giyane Jan Rini

Ga Zamani yayo Muni Maqurar Sani

In Laddabi Akayima To kai kasani

Bawanda Zaimaka banza inkai tini

Inmacce ce taga Kudine ko sabon zani

Ko ko Abinci takeso agareka kayo sani

Dan mai Bara da Rikon kwarya To kasani

Barar Zamani da Baki Akeyinsa da Bude zani

Kaima Kasani Ga Mai Kod’aka aran Yini

Amarsuce Take Wautar kukan dadi mundai Sani

Banza Nasha Na Wuni Da Qishi na Tuntuni

Bazanci Banza ba Ace Nakwan Dana sani

LITTATTAFAN ADDIN

Daga Shafin Alpholtawy media

Zamu Daura Guda Goma insha Allahu muna Kyautata Zaton Zakuci Moriyarsu.

.

ANNABI MUHAMMAD ﷺ

  • Nasarorin Ƙungiyar Arewa Media Writers
    Nasarorin Da Ƙungiyar “Arewa Media Writers” Ta Samu Cikin Shekaru Biyu, July 2020, Zuwa July 2022 Ga wasu daga cikin nasarorin… Read more: Nasarorin Ƙungiyar Arewa Media Writers
  • TARBIYYAR ‘YA’YA AMUSULUNCI
    ══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════TARBIYYAR ‘YA’YA AMUSULUNCI══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════ ══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════                       GABATARWA══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════                           … Read more: TARBIYYAR ‘YA’YA AMUSULUNCI
  • ZATIN UBANGIJI
    SHAUQI CIKIN AL AMARIN GAIBIYYA Kasantuwar Ubangiji A Buya Bai zama tawaya Ga Imanin Mai imani Sai dai Yana kara imanine… Read more: ZATIN UBANGIJI
  • GODIYA TA GA ALLAH BUWAYI
    Ban Shan Sigari Ban Shan MoringaBan Shan 200 Kayan zamani Ban Leqa tagaKayan Wani bai idona Ni nai ga KatangaShiga Sha`anin… Read more: GODIYA TA GA ALLAH BUWAYI
  • KUJI TAUSAYIN MARAYAN ALLAH
    Bansan me Nayi mussu baNufata da Sharri suke basu barniba Nayi kukan ZuciyaHar na Ido Hawayena Basu fad’i ba Ganinan na… Read more: KUJI TAUSAYIN MARAYAN ALLAH
  • FASAHAR ZAMANI
    Menene capacitor?  Dauki masu gudanar da wutarlantarki guda biyu (abubuwan da suka bari Wutarlantarki ta ratsa su) sai ka raba su da insulator(kayan da ba su barin wuta ya ratsa sosai) sai kayi capacitor: wani abu da zai iya adanamakamashin wutar lantarki. Kara makamashinlantarki ga mai iya aiki shi ake kira caji ; fitar dakarfin daga mai iya aiki shi aka sani dadischarging. Capacitor yana dan kama da baturiya, amma yanada wani aiki daban. Baturiya na amfani dasinadarai don adana makamashin lantarki da sake shi a hankalita hanyar zagaye; wani lokaci (a yanayin agogonkwata) zai iya daukar shekaru da dama. Mai iyaaiki yana sakin karfinsa da sauri-sau da yawa acikin sakanni ko kasa da haka. Idan kana daukanhoton flash, misali, kana bukatar kyamararka don samar da babban burst na haskea cikin fraction na sakan daya. Wani mai iko daaka hađe da bindigogin flash na ‘yan sakanni taamfani da makamashi daga batirin kyamararka.(Yana daukar lokaci kafin caji capacitor shi yasayawanoci dole ka jira kadan.) Da zarar an caji maikarfin, zai iya sakin duk karfin nan take ta hanyarxenon flash bulb. Zap! What is a capacitor?Take two electrical conductors (things that letelectricity flow through them) and separate… Read more: FASAHAR ZAMANI

Kanun bayannai

  • Nasabar Sa
  • Iyayen Sa
  • Haihuwar Sa
  •  Aiko Shi
  •  Hijirar Sa zuwa Madina
  •  Yaƙoƙinsa
  • Matan Sa
  • Yayayen Sa
  •  Masu yi masa hidima na musamman

 Muhammad  Annabi ne kuma Manzo ne wato ma’aikin Allah Madaukakin Sarki. Allah Ya aiko shi domin ya tabbatar da addinin da Annabawan da suka gabace shi suka koyar, Kamar Annabi Ibrahim da Annabi Musa da Annabi Annabi Isah da dukkannin sauran Annabawan Allah (tsira da amincin Allah ya kara tabbata a gare su) Annabi Muhammad (s.a.w) shine cikamakon Annabawa, wato Annabin karshe wanda daga kansa babu wani annabin Allah. Dukkan wanda yayi ikirarin annabta bayan zuwan Annabi Muhammad (s.a.w) to karya yake. Shine kuma ya hada kan dukkan larabawa suka dunkule waje daya, tare da daidaita yan adam ta hanyar koyarwar sa da Alkue’anin da yazo da shi.   

Nasabar Sa

Muhammad ɗan Abdullahi ɗan Abdul-Muɗɗalibi ɗan Hashimi ɗan Abdu-Manafi ɗan Ƙusayyi ɗan Kilabi, Sallallahu alaihi wa aalihi wa sallam, (Harshen Larabci: Abūl-Qāsim Muḥammad ibn ʿAbd Allāh ibn ʿAbd al-Muṭṭalib ibn Hāshim ibn ˁAbd Manāf ibn Qusayy ibn Kilāb) nasabarsa maɗaukakiya tana tuqewa zuwa ga Annabi Ibrahim, alaihi salatu wassalam. Manzon Allah ne. Khataman-Nabiyyin da addinin Musulunci. 

Iyayen Sa

Mahaifiyarsa: Ita ce Aminatu (Āminah) ‘yar Wahbi ɗan Abdu-Manaf ɗan Zuhrata ɗan Kilabi (Radhi Allahu anha). Alkunyarsa: Abu-Qasim, Abu Ibrahim. 

Laƙabinsa:

Al-Musɗafa (zababben Allah) yana da sunaye da suka zo a cikin Ƙur’ani Mai Girma kamar, Khataman-Nabiyyin, da Al-Ummi da Al-Muzzammil da Al-Muddassir da An-Nazir da Al-Mubin da Al-Karim da An-Nur da An-Niˁima da Ar-Rahma da Al-ˁAbdu da Ar-Ra’uf da Ar-Rahim da Ash-Shahid da Al-Mubasshir da An-Nazir da Ad-Da’i da sauransu. 

Haihuwar Sa

An haifi Annabi Muhammad (s.a.w) a wajen shekara ta 570Miladiyya. Mahaifinsa shine Abdullahi ya rasu kafin haihuwar Sa. Mahaifiyar sa Amina itama ta rasu lokacin da yake dan shekara shida a [[duniya]. Haka yasa kakan sa Abdul-Mudallib ya rike shi har zuwa lokacin daya rasu, lokacin Annabi Muhammad (s.a.w) yana dan shekara takwas a duniya. Daga nan sai kawun sa Abu-Talib yaci gaba da rikon sa. Abu-Talib ya taimaka ma Manzon Allah (s.a.w) sosai a rayuwar sa. 

Aiko Shi 

Kogon Hira, wajen da aka fara wa Annabi WahayiAikoshi: An aiko shi a Makkah 27 Rajab yana ɗan shekara arba’in. Koyarwarsa Ya zo da daidaito tsakanin dukkan halitta da ‘yan-uwantaka da rangwame na gaba ɗaya ga wanda ya shiga musulunci, sa’annan ya kafa shari’a maɗaukakiya da dokoki na adalci da ya karɓo daga wajan Allah su kuma musulmi suka karɓa daga gare shi.

 Mu’ujizozinsa

 Mu’ujizarsa madauwamiya ita ce Ƙur’ani amma waɗanda suka faru a farkon Musulunci suna da yawa ba sa kuma kirguwa. Kiransa Ya kira mutane zuwa ga Tauhidi a Makkah a ɓoye shekara uku ya kuma kira su a bayyane shekara goma. 

Hijirar Sa zuwa Madina

Bayan Tsanani da takurawar Kafuran Makkah akan Annabi Muhammad (s.a.w) da wadanda sukayi inami da shi yayi yawa, sai Allah Yayi ma Manzon Sa da sauran Wadan da sukayi imani da shi izinin akan suyi kaura daga garinsu na haihuwa wato birnin Makka zuwa wani garin daban na wati Madina. Mutanen birnin Madina kuwa sunyi matukar murna da zuwan sa garin su kuma sun bashi kyakkyawan masauki. Sanna kuma sukayi imani dashi suka shiga AddiMusulunci. A farkon Hijira dai Shi Annabi da kansa dakuma babban aminin sa kuma na farko wajen imani dashi wato Sayyadina Abubakar Sukayi tasu hijirar tare. Sannan sauran musulmai sukayi ta bin bayansu daya bayan daya. Kaurar Annabi (s.a.w) daga Makka zuwa Madina shine ake kira Hijira kuma shine farkon kalandar Musulunci. 

Yaƙoƙinsa

Inaso Mai Karatu Yayi haquri, Wannan Babi Zamu daukeshi amatsayin Darasinmu na Gaba

إن شاء الله 

Matan Sa

Annabin Musulunci Muhammad Ya auri mata goma sha daya, ga Jerin sunayen su. 

  • Khadijah(Kubura ‘yar kuwailadu)
  • Saudat
  • A’ishah(‘yar Abubakar )
  • Hafsah(‘yar Umar)
  • Zainab(‘yar Kuzaimata)
  • hindatu(ummu salama)
  • Zainab(‘yar jahshin)
  • juwairiyya
  • ramlat
  • safiyya
  • maimunah

Yayayen Sa

Ammominsa: Tara ne, su ‘ya’yan ˁAbdul-Muɗɗalib ne: Al-Haris da Zubair da Abu Ɗalib da Hamza da Al-Ghaidaq da Dirar Al-Muqawwam da Abu Lahab da ˁAbbass. Ammominsa mata: Su shida ne daga iyaye mata daban-daban su ne: Aminah da Ummu Hakima da Barra da Atiqa da Safiyya da Arwa. Wasiyyansa goma sha biyu ne, su ne: Amirul-Mu’minina Ali ɗan Abi Ɗalib (a.s) da Hasan ɗan ˁAli da Hussain ɗan ˁAli da ˁAliyyu ɗan Husaini da Muhammad ɗan ˁAli da Jaˁfar ɗan Muhammad da Musa ɗan Jaˁfar da ˁAli ɗan Musa da Muhammad ɗan ˁAli da ˁAli ɗan Muhammad da Alhassan ɗan ˁAli da Muhammad ɗan Hassan Mahadi (a.s). 

Masu yi masa hidima na musamman

Mai tsaron ƙofarsa: Anas ɗan Malik. Mawaƙinsa: Hassan ɗan Sabit, da ˁAbdullahi ɗan Rawahata, da Ka’abu ɗan Malik. Mai kiran sallarsa: Bilal Al-Habashi da ˁAbdullahi ɗan Ummu Maktum da Saˁad Al-Kirdi. Tambarin zobensa: Muhammadur Rasulullah! Tsawon rayuwarsa: shekaru 63. Tsawon lokacin Annabtarsa: shekaru 23. Tarihin wafatinsa: 28 Safar 11 H. 

Wajan da ya yi wafati: Madinah.

 Inda aka binne shi: Madinah a Masallaci Maɗaukaki Mai Alfarma. Ka sani cewa Muhammad (S.A.W) shi ne ƙarshen annabawa kuma addininsa shi ne musulunci mai shafe duk wani addini kuma shari’arsa zata wanzu har zuwa qiyama kuma ita kaɗai ce shari’ar da zata arzuta mutum da tabbatar masa da burinsa da amincinsa har zuwa ƙarshen rayuwar duniya da lahira. Kamar yadda shi kaɗai ne mutum abin koyi ga dukkan duniya baki ɗaya, dukkan mutanen duniya idan suna son alheri ga kawukansu to dole ne su bi tarfarkinsa su yi koyi da kyawawan halyensa (S.A.W) da kuma sanin sashen tarihinsa da ba makawa mu kawo wasu daga siffofinsa (S.A.W): Shi ne Muhammad ɗan ˁAbdullah (S.A.W) kuma babarsa ita ce Aminatu ‘yar Wahab. An haife shi a Makkah ranar juma’a goma sha bakwai ga watan Rabi’ul awwal bayan ɓollolwar alfijir a shekarar giwa, a zamanin sarki mai adalci Kisra . (wato idan an kwatanta shi da ire-irensa). 

Aiko Annabi Mai Daraja (S.A.W)

 An aiko Annabi Muhammad (S.A.W) da saqo a 27 ga Rajab bayan yana ɗan shekara 40 yayin da Jibrilu (A.S) ya sauka gareshi daga wurin Allah (S.W.T) yana kogon Hira wanda yake dutse ne a Makkah ya ce masa ka karanta kuma ya saukar masa da ayoyi biyar na surar Alaƙi . Sai ya zo ya tsaya a kan dutsen Safa a masallaci mai alfarma na Makkah a lokcin akwai jama’a masu yawa a wurin da ake taruwa ya isar da saƙon Allah na shiryar da mutane zuwa ga imani da shi yana cewa da su: “Ku ce babu abin bauta sai Allah kwa rabauta” . A lokacin tunda mutanen Makkah mushrikai ne, kuma suna ganin maslaharsu ita ce shirka kuma suna tsoron maslaharsu sai suka riƙa yi masa isgili suna yi masa dariya suna cutar da shi. Kuma duk sa’adda ya dage wajen shiryar da su sai su dage wajen cutar da shi har ya ce: “Ba a cutar da wani Annabi ba kamar yadda aka cutar da ni” . Ba wanda suka yi imani da shi sai mutane ƙalilan, na farkonsu Imam ˁAli sannan sai matarsa Khadijah (A.S) sannan sai wasu mutane. Farkon wanda ya yi imani da shi daga maza Imam Ali sannan daga mata sai Hadiza (A.S). Yayin da takurawar mushrikai ta yi yawa sai ya yi hijira zuwa Madinah wannan kuwa ita ce hijirar farko a tarihin Musulmi, yayin da suka yi yawa sai qarfinsu ya daɗu kuma suka samu koyarwa daga Manzon Allah da shari’arsa Mai Sauƙi Mai Hikima, da kuma misali na kyawawan halaye da mutumtaka da wayewa da cigaba a Madinah har suka fi dukkan duniya da addini na sama da waɗanda ba na sama ba. Kuma an samu yaƙoƙi masu yawa a Madinah kuma dukkanninsu sun zama domin kare kai ne daga maƙiya mushrikai da yahudawa da kiristoci da suke kai hari kan musulmi, kuma Annabi a kowne lokaci yana zaɓar ɓangaren sulhu da zaman lafiya ne da rangwame, don haka ne ma adadin waɗanda ake kashewa daga ɓangarorin biyu ba su da yawa a dukkan yaƙoƙinsa tamanin da wani abu, wato; waɗanda aka kashe na musulmi da kafirai duka ba su kai sama da dubu ɗaya da ɗari huɗu ba. Mutuwa Mai Zafin Gaske Tun lokacin da aka aiko Annabi da saƙo har ya tafi daga duniya wahayi yana sauka gareshi kuma Jibrilu (A.S) shi ne ake aiko masa daga wajen Ubangiji (S.W.T) a hankali a hankali har littafin Ƙur’ani ya ciki a cikin shekaru ishirin da uku, sai Manzo (S.A.W) ya yi umarni da a haɗa shi kamar yadda yake a yau ɗin nan. Manzo (S.A.W) ya kasance yana tsara wa musulmi duniyarsu da addininsu, yana sanar da su littafi da hikima kuma yana yi musu bayanin dokokin ibada da biyayya da mu’amala da zamantakewa da siyasa da tattalin arziki da sauransu.

Continue reading

MAGUNGUNA AMUSULUNCI

AMFANIN SABAYA A JIKIN YA”MACE

*DR ABDULWAHAB GONI BAUCHI*

Idan Mutum Ya Hadawa Matarsa (SABAYA) Yana Da Matuqar Ta’asiri a Jikin Ya”Mace Kuma Yana Haifar Mata Da Ababe Uku a Jikinta Akwai Matar Da Idan Tana Shayarwa Zakaga Kamar Ta Fito Daga Gidan Yari Wata Jikinta Yana Zubewa Ruwan Nononta Yana Lalacewa

*Nafarko Idan Mace Tana Amfani Da Sabaya Zai Taimaka Wajen Dawo da Halittan Da Allah Yai Mata Jikinta Nonon Bazai Zube Ba
*Na Biyu Idan Mace Tana Amfani Da Sabaya Jikinta Zaiyi Laushi Kamar Kwalabiya
*Na Uku Idan Mace Tana Amfani Da Sabaya Da zarar ta Haihu Irin Ramar Da Mata Keyi Baza Tayi Ba

Kuma Ruwan Nononta Zai Qara Yawa Sannan Bazai Lalace Ba Kuma Yaron Data Haifa Allah Zai Kareshi Daga Dangin Cututtuka

Kuma Hatta Magidanci Idan Yasha Yana Qara Masa Lafiya Da Kuma Kuzari a Jikinsa

MEYA KAMATA ASAMO WAJEN HADA SABAYA TASU KAMAR HAKA:
*Al Kama 1Mudu
*Danyen Shinkafa 1Mudu
*Waken Suya 1Mudu
*Ridi ½Mudu
*Hulba ½Mudu
*Gyada Mai Bargo/Kamfala
*Madara
*Zuma

YA ZA’A HADASU SHINE:
Ridi Da Gyada Ana Hadasu Wuri Guda Ridi a Soyashi Yadda Ake Kantu, Gyadar A Soyata Yadda Ake Quli Quli, Shinkafa Da Alkama Ana Jiqasu Tsawon 5hour Sai a Shanya Da Laima a Jikin Sai a Hadasu Wuri Guda

Da Ridin Da Gyadar Da Al Kama Da Hulba Da Shinkafar Sai a Niqa Matarka Tin Tana Da Ciki Ya Kamata Ka Fara Bata Har Zuwa Haihuwa Kaga Yadda Zatai Da Yaronta Kuma Nononta Dana Shayarwa Ko Bata Shayarwa Bazai Canza Ba Da Ikon Allah

TO YA AKE SHANSA
Yadda Ake Dama Kunu Haka Ake Damashi Sai Dai Idan aka Zuba Ruwan Zafi Ana Iya Maidashi Kan Wuta,
Sukace Karta Wuce Cokali Uku a Rana Musamman Cikin Babban Cokali Idan Kuma Harda Magidancin Sai a Sanya Cokali Shida

Su Kace Amma Idan Mace Bata Da Aure Kada Tasha Domin Yana Qara Sha’awa Kuma Yana Qara Yawan Nono Ma’ana Yafi Dacewa Da Matar Datake Shayarwa Domin Samun Ingancin Lafiyar Jikinta Don Kada Ya Zube

Kuyi Amfani Da Wannan Link Din Domin Samun Magunguna a Sauqaqe

ALLAH ﷻ Yasa mu amfana dash

ماشاءاللہ