TARIHIN SAHABBAI 001

TARIHIN SAYYIDINA ABUBAKAR SADDIK ALLAH YA YARDA DA SHI,

(manzon Allah S. A. W) “yace ya Abubakar kai ne farko wanda zai shiga Aljanna daga al’umma ta”

Sayyidina Abubakar shi ne Abdullahi dan Abu kuhafatu ” usman” usman dan Amir dan Amir dan ka”abu dan sa”adu da taimu dan murratu dan ka”abu dan lu”aayu, bakuraishe. Bataime. Nasabarshi ta hadu da manzon allah ta wajan murratu dan ka”abu kakansu na biyar. Sunan shi a lokacin jahiliya “Abdul ka” aba” daya musuluta sai manzon allah ( S. A. W) yakara shi “Abdullahi” An yi mishi alkunya da Abubakar saboda riganyenshi wajan dabi”antuwa da kyamara halaye. Kuma an yimasa lakabi da saddik sabo da saurin bayar da gaskiyar shi ga dukkan abunda manzon allah (S. A. W) ya fada kuma manzon allah (S. A. W) yakara shi da “Atiku” shine mutumin da yafara musuluta a manyan. Shi ne mutum na farko, da ya fara kira zuwa ga addinin musulunci. Bayan manzon Allah Annabi Muhammad (S. A. W) shine yafara haduba a addinin musulunci. Shine abokin zaman kogo tare da manzon Allah na farko kuma shine nafarko cikin sahabbai goma da aka musu albishir da gidan Aljannah tun a duniya shine farkon Amirul hajji kuma yana cikin marubuta wahayin da akema Annabi Muhammad (S. A. W) An haifi Sayyidina abubakar (R. A) a makka bayan Shekara giwaye da shekaru uku (573 A. D) manzon Allah. Ya girma shi da shekaru uku. Yana cikin manyan shuwagabannin kuraishawa a lokacin jahiliya kuma a bakin manzon allah ne na kasa tun kafin aiko shi. Sau dayawa ma. Yakanje gidan shi su tattauna shine mafi sani duk larabawa game da tarihin nasabar kuraishawa. 
Kuma yakira mutane da yawa zuwa ga addinin musulunci. Biyar daga cikin su suna cikin sahabbai goma. Da aka yiwa bishara da Aljannah sune kamar haka :  
Ya sha a zaba iri – iri daga kafiran makka saboda shigar shi musulunci 
Har takai babu wani musulmai da azabtu kamar shi. Duk da irin matsananciyar azabar da suka sha suda sauran musulman farko daga kafiran makka. Bai yi kauraba zuwa kasar habasha ba. Ya tare ga manzon allah (S. A. W) lokacin kaura zuwa madina yana tare da Annabi Muhammad (S. A. W), tare suka shiga kogo kafin suwuce zuwa madina shine cukon mutane biyu da Allah ya ambata a alkur”ani in da yace : ” Idan baku taimakeshiba. ( Annabi), to ai Allah ya taimake shi yayin da kafurai suka fitar da shi ( daga makka) na biyu (mutane) biyu yayi dasuka shiga cikin kogo yake cewa da abokin shi (Abubakar)” kada kaji tsoro, Mu Hakika Allah ya na tare damu “( da taimako shi)” cikin suratul tauba:40, yayin da suka isa madina. Sayyida Abubakar, A wurin kharijatu dan zaidu. Da shi kuma manzon allah yahada su ‘yan uwantaka yayi da ya rinka hada yan’ uwantaka (ta musulunci) tsakanin mutane makka ( muhajiruna), da na madina (Ansaru) Sayyida Abubakar shine tamkar Waziri ga Annabi Muhammad (S. A. W), wajan gudanar da al’amuran daular musulunci. Mai babbar hedikwata a madina: birnin manzo,,,

Abubakar saddik ( R. A) ya dukkan yake _ yaken daukaka musulunci da yada shi da Annabi Muhammad (S. A. W) a yakin badar shine kan gaba wajan kula da wurin da manzon allah yake. Yana shir yanda yake zai gudana tare da rokon allah. har dai allah ya amsa addu’ar Annabi, ya aiko da rundunar mala”iku. Musulmai suka samu nasara. A yakin uhudu kuwa, Sayyida Abubakar. Shine jagora tsirarun Manyan sahabbai, suka gabata a filin yakin. Tare da manzon allah (S. A. W) yayin da kafurai suka tarwatsa rundunar musulmai.

Bissalam

Continue reading

MAGUNGUNA AMUSULUNCI

AMFANIN SABAYA A JIKIN YA”MACE

*DR ABDULWAHAB GONI BAUCHI*

Idan Mutum Ya Hadawa Matarsa (SABAYA) Yana Da Matuqar Ta’asiri a Jikin Ya”Mace Kuma Yana Haifar Mata Da Ababe Uku a Jikinta Akwai Matar Da Idan Tana Shayarwa Zakaga Kamar Ta Fito Daga Gidan Yari Wata Jikinta Yana Zubewa Ruwan Nononta Yana Lalacewa

*Nafarko Idan Mace Tana Amfani Da Sabaya Zai Taimaka Wajen Dawo da Halittan Da Allah Yai Mata Jikinta Nonon Bazai Zube Ba
*Na Biyu Idan Mace Tana Amfani Da Sabaya Jikinta Zaiyi Laushi Kamar Kwalabiya
*Na Uku Idan Mace Tana Amfani Da Sabaya Da zarar ta Haihu Irin Ramar Da Mata Keyi Baza Tayi Ba

Kuma Ruwan Nononta Zai Qara Yawa Sannan Bazai Lalace Ba Kuma Yaron Data Haifa Allah Zai Kareshi Daga Dangin Cututtuka

Kuma Hatta Magidanci Idan Yasha Yana Qara Masa Lafiya Da Kuma Kuzari a Jikinsa

MEYA KAMATA ASAMO WAJEN HADA SABAYA TASU KAMAR HAKA:
*Al Kama 1Mudu
*Danyen Shinkafa 1Mudu
*Waken Suya 1Mudu
*Ridi ½Mudu
*Hulba ½Mudu
*Gyada Mai Bargo/Kamfala
*Madara
*Zuma

YA ZA’A HADASU SHINE:
Ridi Da Gyada Ana Hadasu Wuri Guda Ridi a Soyashi Yadda Ake Kantu, Gyadar A Soyata Yadda Ake Quli Quli, Shinkafa Da Alkama Ana Jiqasu Tsawon 5hour Sai a Shanya Da Laima a Jikin Sai a Hadasu Wuri Guda

Da Ridin Da Gyadar Da Al Kama Da Hulba Da Shinkafar Sai a Niqa Matarka Tin Tana Da Ciki Ya Kamata Ka Fara Bata Har Zuwa Haihuwa Kaga Yadda Zatai Da Yaronta Kuma Nononta Dana Shayarwa Ko Bata Shayarwa Bazai Canza Ba Da Ikon Allah

TO YA AKE SHANSA
Yadda Ake Dama Kunu Haka Ake Damashi Sai Dai Idan aka Zuba Ruwan Zafi Ana Iya Maidashi Kan Wuta,
Sukace Karta Wuce Cokali Uku a Rana Musamman Cikin Babban Cokali Idan Kuma Harda Magidancin Sai a Sanya Cokali Shida

Su Kace Amma Idan Mace Bata Da Aure Kada Tasha Domin Yana Qara Sha’awa Kuma Yana Qara Yawan Nono Ma’ana Yafi Dacewa Da Matar Datake Shayarwa Domin Samun Ingancin Lafiyar Jikinta Don Kada Ya Zube

Kuyi Amfani Da Wannan Link Din Domin Samun Magunguna a Sauqaqe

ALLAH ﷻ Yasa mu amfana dash

ماشاءاللہ

INGANCIN ZUQATAN BAYI

INGANCIN ZUCIYA!!! ***************************************** Hakika gyaran zuciya itace maqasudin kar´bar aiki. Da Akwai Ayoyi da hadisai ingantttu dake nuna jinjina ga ayyukan bayi amma dukkansu suna yabawane akan tsarkin zuciya domin shine (sababin karbar aikin). Hakazalika. ibadar da Allah yafisoma, ~Maqasudinsa zuciyace watau (Azumi).

Shi Azumi ALLAHﷻ (s.w.a) Shine kadai keda hakikanin gasgata maiyinsa, Saikuma Zuciyar maiyinsa, Sa`annan kuma ma ALLAHﷻ shi da kansa yake cewa yana son masu tuba damasu tsarki Ma´ana masu tsarkake zuciyoyinsu daga bari munanan ayyuka. Da ayyukan da aka kyamata. Gashinan in arabic text إن الله یحب التوابین ویحب المتطهری Manzon ALLAH ﷺyana cewa إن فی الجسد مضغة إذا صلحت صلح الجسد کله وإذا فسدة فسد الجسد کله علی وهی القلب Arufai kuyimin afuwa nai muku Shisshigi inda kuskere atusaddani. Dan Adam ajizine ALLAHﷻShine masani. dafatan anyi Juma`ah lafiya

MATAKAN TARBIYYA GUDA UKU


MATAKAN TARBIYYA
Daga. Alqalamin Ismail Smart
Dasunan ALLAH Mai RAHAMA Mai JINKAI.
Haqiqa tarbiyya dolece a addinin mu na musulunci musan man ma na iyalanka/ki
Domin ALLAH MADAUKAKI yana cewa:

یا أیهاالذین آمنو قو أنفسکم وأهلیکم نارا وقودها الناس والحجارة
        Awannan aya ALLAH yayi umarni ga Muminai dasu Kare kansu da iyalansu daga wata wutta Wanda yakasance makamashinta mutane ne dakuma duwatsu.
ALLAH UBANGIJI katsaremu amin  ya RABBI. Awannan ‘Bangaren Nakeson nayi rubutu  domin yan uwa musulmai su anfana.
ALLAH MADAUKAKIN SARKI ya dafamin
MATAKIN FARKO
(Neman Aure zuwa da yakai 5yrs)
Dole Akan kowa Idan yazo neman aure
Yanemi Mai addini Da hali nagari Da kakkyawar zuciya. Ba kawai kyawun fuskaba ko wani martaba ko nasabar Abokin zama ba. Kuma yazamto anyi auren tanasonsa yana sonta.
Domin hakanne Zaisa suji dadin zamantakewarsu ta Aure Kuma hakan Zaisa yayansu sutaso dason junansu Da Bin doka ko umarnin Da akayi masu. Domin kada yazamto uwa tace fari uba yace Bahakaneba Baki yake. Bayan haka
Yazama dole asakawa yaro kakkyawar suna alokacin dayake jinjiri. Yazama dole ka karantar Da matanka tsarin tarbiyyar addinin musulunci ko kasa akarantar da ita Awannan sahar kokuma MA kafin wannnan lokacin. Ma’ana kafin ta sami d’a (yara).
Domin kaso saba’in Cikin Dari (70%) Na Tarbiyyar cikin Gida maqasudinsa na uwace. Yazama dole takasance Mai Lura da Meke gudana me sukeso me yakamata suyi ko so Bari duk wadannan uwace takeda hakkin koyar da yaranta.
Dakuma koyardasu Ibaadaat Kamar Sallah Azumi Dakuma koyamusu karatun Alqur’ani da tilawarsa dama haddarsa. Har sukai 10yrs  Kafin daga bisani Sai Aturasu  Islamiya. Sucigaba da karatu daneman ilimin addini. Hakan zaisa sutaso da ganin girman iyayansu. Dama duk wanda yagirmesu tayadda basai ance ga malam waneba kafin sudaina abinda sukeyi.
MATAKI NA BIYU
(Daga 5yrs zuwa 15 to 18yrs)
Dolene akan iyaye su San abokanan yayansu, Susan Kuma menene alaqarsu dasu Domin duk kyawun tarbiyyar dakasamu agida abokai sukan wargazashi, matsawar dakayi abota da marasa tarbiyya koda baka zama tamkarsu ba. Zaka rudu da wani hali acikin munanan halayyarsu.
Yazama dole iyaye su bawa yayansu tarbiyyar addini da wayewar rayuwa tahanyar sanaddasu yadda zasuyi addini da hikimomin tsara rayuwa bisa kykkyawar tsari. Kamar koyamusu dabarun kare kai da addu’o’in neman tsari da kariya. Da sanardasu tarihohi Wanda zasu sami hikima da, wa’azozi acikinsa. Domin abinciken masana kwakwalwar dan adam sun yarda akan cewa kwakwalwar dan adam takan bude da adana bayanai alokacin da mutum yake dan shekaru takwas (8) zuwa Sha biyar (15) koda haddane mutum yafi nutsuwa dashi awannan lokacin Inhar kaga yaro ya natsu awannan lokacin to tabbas ana kyautata zaton shiryayye ne. Inkuma ya kangare kuwa yanada wuyar shiryuwa Yakamata iyaye sudunga zama da yaransu suna zantawa dasu domin suji damuwoyi da bukatunsu, Harsu san tahanyar da zasu bullo musu gurin bada shawara ko kore musu matsalarsu tarayuwa.
MATAKI NA UKU NAKARSHE
(Daga 15/18yrs. zuwa auraddasu)
Yakamata iyaye su lura da yayansu su san menene wane/wacce tafi/yafi kwarewa akai saisu dage gurin nema masu mafita ta hanyar basu tallafi ko jari domin samun damar gudanar da harkokin rayuwarsa cikin sauki batare da yana zauneba saidai kullum abashi.
      Domin hakan yana kashe zuciyar mutum yazanto baya iya kafuwa da kansa balle ma har yagina wasu. Saidai kullum a bani_bani sai kuma bin abokai da yawace yawacen banza da hofi, da bin bangar siyasa, wadda daga karshe ke jawo mutum yakoma ta’asa da ‘barna acikin al’uma kokuma ma yakama shaye_shaye da bin mugaye mutane. Duk adalilin rashin aikin yi. ALLAH ya tsaremu da zuri’armu baki daya.
       Rashin aikinyi na daya daga cikin abubuwa mafi girma wanda suke lalata  tarbiyya arayuwar mutane.
Allah ka bawa iyayen mu hakurin zama damu kasauke musu hanyar dazasu tarbiyyantar damu tarbiyya ta Addinin musulunci, ALLAH kajikan maifina kahaskaka qabrinsa.

AKAFA DAULAR MUSULUNCI DOMIN A TACE MASU SON ZICIYA A ADDINI

MUSULMI ATASHI AKAFA DAULA DAN SAMUN INGANTACCEN RAYUWA

inji Shahararren malamin salafiyyannan Sheikh Muhammad Adam Albany Zaria.
   Hakika shugaba yayi wadannan maganganu da shawarwarin agurare Ma bambanta da majalisai dadama. Domin nuni garemu ga hanyar tsira. Dakuma koyi da magabata. Don samun rayuwa Mai inganci, da zamantakewar rayuwa Mai tsafta. Ba kamar yadda wasu ke daukar zancen awata mahanga. Da tunani irinta miyagun mutani ba.
Ga zancen malam;
Tsokaci kan batun malam:
    Saidai haryanzu banji wani shahararren mutum daga cikin malamai ko shugabanni daga cikin musulmiba wanda ke karfafa Zancen. Duk da cewar maganan maganice na ciwon dayake damun musulmin duniya baki daya. Saidaima wasu daga cikin miyagun mutane dasuke fassara zancen da wani salo nadaban, tayadda suke kokarin cire ma’anar maganan na hakika su shigoda wani al’amari nadabam.
    Gadai Maganan da malam yayi;
Mal. Yace ”Yakamata musulmi su kafa daula Dan gujewa hadarin dake gabansu, na miyagun hare_haren yahudawa”
Abinda malam ke nufi anan shine.
Shi cigaban addini dole saida kafa  daula dakuma tabbatar da Shari’ah. domin tabbatar da Shari’ah shiyake saukakewa mutani  hanyar rayuwa Mai inganci. Shi Kuma kafa daula shine hanya mafi sauki Wanda zai tabbatarwa da mutani yancinsu. Tayadda gudanarwar rayuwar Musulmi zaizamto tsararrene, Ga Shugabanninsu. Koda aharkar da’awace da karantarwa, zai kasancene karkashin wannan hukumace, matukar lamarin addini za’a karantar.
   Ko kataba tunanin meyasa Turawan yamma suke gaba da Musulunci? To ga ansarka;
  Burinsu aduniya yazamto babu Mai iko saisu, tayadda zasuyi dukkan abinda sukeso batareda wani yayi musu inkariba.
   Shi kuma musulunci akodayaushe Adalci yake tabbatarwa ga mutane. Haka kuma idan akace za’a kaddamar da Shari’ah za agusar da Al’adunsu asanya abinda Allah yahukunta Wanda kuma yasha bamban da son Zuciyarasu. Kuma Shine ainihin adalci, duk mai inkari akan haka yadauki Alqur’ani yakaranta, Zaiga tsagwaran adalci. Sa’banin son zuciya dakuma Zalincin turawa na constitution, wanda muke anfani dashi amatsayin hukunci ayanzu. Dashi suke amfani su saka dukkan wata son zuciyar na burin dasuke so su cimma akasanku saisu fake dacewa sunkawo muku tsarin hukuman, dana shugabanci kuma wai Afadinsu shine dokokin kasa wadanda za’ayi amfani dasu. Wanda ahakikanin gaskiya akwai duk abinda muke bukata acikin Alqur’ani da Bible. Nadaga tsarin rayuwa dana shugabanci, domin wannan shine dokar Allah wanda ya shinfidasu ga bayinsa.

Idan mukayi dubi ga maslahar kafa daula kuwa. Misali mafi sauki Shine Inda zamuyi dubi ga Al’umomin damuke rayuwa acikinta.
        Abinda zamu lura anan dai shine Kowace kasa tanada sojoji dasuke karkashinta tareda shugabanni mabambanta. Shugabannin nan sune ke tsara dukkannin doka da tsarukan cigaban kasar. To inaga musulunci. Wanda danshi mukazo duniyar kuma yatara makiya kota ina. Inbabu shugabanci bazamu Taba sanin ina muka dosaba. Saidai muta dimuwa da fagabniya tayadda zasu cigaba da kashemu dakuma kiranmu dasunan yan ta’adda. Idan da zakayi bincike kashi saba’in da biyar cikin Dari (75%) Na mutanen da yan ta adda ke kashewa ayanzu Musulme ake kashewa. Amma kuma musulmi ake daura wa Alhakin kisan, dakuma Kiran musulunci da Sunan addinin ta’addanci da ‘yan ta’adda. Domin Akan samu wasu lalatattu da basusan mecece hakikanin addiniba, Suna fakewa da sunan jihadi Suna ta’addancinsu abisa son zuciyarsu. Don wata maslahar rayuwarsu ta duniya. Kuma suna kiran kansu musulmi, Sabida Musulmi basuda manya hukumance waanda dazata karyata wannan al’amarin yasaka, ake tafiya ahaka batare da angyaraba.

     Indagaske musulmaine yan ta addan danme za ake kashemu Kamar kisan kiyashi. Adasa boma_bomai akona masallatanmu dasunan ta addanci. Kawai Rashin Tabbatar da daulane dakuma Rashin samar da daularma gabaki daya. Tayadda wasu zasu fake dasunan jihadi suna kashemu sa’Annan akuma daura alhakin kisan agaremu. Don rashin samun wadanda zasuyi jagora gurin fada da Al’amarin acikin hukumomin duniya.
        Kada rayuwar holewa na turawan yamma yaburgeka ka manta da addininka ko police kasamu amatakin hukuma, Matukar kai musulmine kaji aranka aikin musulunci zakayi. Inzamu dukufa dakawunanmu duk yawan kafiran duniya koda sun nunkamu sau dubune basu isa suyimana abinda Allah bai So Ba, Sai abinda Allah yanufa akanmu shine zai samemu. Kada abin duniyarsu ya tsole maka ido har ka aminta da wani mummunar manufarsu akan Al’umar musulmi. Koda Kai ba musulmi bane to inba ayankinsu kakeba to hakika Kai abin Hari ne garesu kuma sai sunyakeka ta kowani bangare na rayuwa.
   Abin Lura garemu musulmi.
Allah yafada mana acikin Alqur’ani. Wadannan mutane bazasu gusheba suna yakarmu ta kowani ‘bangare harsai munyi ridda munbar addininmu. Kuma kada mumanta da Cewa Su wadannan kosu kyautata ko Akasin Hakan, Allah yayi alkawarin basu duniya Don ita duniya ta kowace, Lahirace ta Wanda Allah yazaba. Kuma duk Wanda yanemi duniya zaisamu. Amma abinda muka sani Su musulmi sunada iyaka awajen nemansu. ba nema mukeyi ta kowani bangareba. Tayadda mukan bambance halal da Haram wannan yasa arzikin musulmi yasha bamaban da turawan yamma dama sauran Al’umomin duniya. haka tsarin rayuwarmu shima ya bambanta dasauran wasu addinai.
Daga Alqalamin
✍️Ismail Hussaini Adam Assalafy
Whatsapp: 09047958802
Instagram: ismailhussein511
Email: hussainiismail257@gmail.com
     ALLAH kadaukaka musulunci da musulmi, ka qasqantar da kafirci, da kafirai, ka dirkake maqiyanka maqiya addininka kataimaki bayinka na qwarai.
4/Ramadhan/1442 Hijiri
16/April/2021 Miladi