ZATIN UBANGIJI

SHAUQI CIKIN AL AMARIN GAIBIYYA

Kasantuwar Ubangiji A Buya Bai zama tawaya Ga Imanin Mai imani Sai dai Yana kara imanine ga Mai imani Yayin da Yake Halarto da Imani Azuciyar Mara shi Matukar ya Kasance Mai Nazarin Lissafin Hangen Nesa da tunani Mai Zurfi.

Imani Gatane  da Yanci na Samar da Sukuni Azucikatan Bayi gamida Samuwar Hasken Zuciya dana Ruhi, Wanda Yazamo Tasirin Samuwar Kyakkyawar Rayuwa Mai Inganci Aduniya dakuma Samun Kyakkyawar Sakamako Bayan Mutuwa.
Wannan Duk darajace da Muqami amma ga Wanda Ya Gasgata Ubangiji Kuma yake Tsoran sa, Shi kadai Baya Tsoron Sharri Sai abinda Ubangijiﷻ Yanufa Shi zai Iya faru Gareshi arayuwa.

Ubangiji ya Boye Zatinsa Na Wanzuwar Siffarnan tasa Madaukakiya, Yayi mana gata Ya Bayyana Mana ilimin Saninsa ta Hanyar Turomana Da Annabawa, Ya Rayamu bisa rayuwa Ingantacciyaya, Bamu kasance Cikin dimuwa da Makantacciyar Zuciya ba.

   Makauniyar Rayuwa itacee Rashin gane Waye Ubangiji Hakan ke tabbatar dakai Ahalaka da Tabewa Kasantuwar hakan zai sanya Maka Kaskantar da Kanka ga Abida Shine yakamata ya Girmamaka, Akasin Hakan Kuwa zai sana Ka koma kana Nema Agun Wanda Saika bashi kake kuma Rokonsa.

  Ka Kaskantar da kanka ga ubangiji da Qaramin Aikinka ga Mai Halittawa Kuma ka Rage burinka ga Duniya Domin Hidima da Bada lokaci cikin Bautawa Maqaginka domin Gyara wa  Rayuwarka na Gaba.

KUJI TAUSAYIN MARAYAN ALLAH

Bansan me Nayi mussu ba
Nufata da Sharri suke basu barniba

Nayi kukan Zuciya
Har na Ido Hawayena Basu fad’i ba

Ganinan na Sarqafe
Igiyar suce Suka ya’ban nashiga fargaba

Ba Mai Karni Ni
Inhar JALLAH bai Qadarinsa akaina Ba

Zasuyi dana Sani
Biyar Dasuke fatansu Bazai Cini ba

Natashi Da Safiya
Qadarin gobe Bazan Sanshi ba

Tafiyar Tayi Nisa
Garin danaje Basu Sanni ba

Nasamu Masauki
Agidan danake Ba’aso Ganina Agefe ba

Suna So Muyi Fira
Kuma Zancena Bazasu Suqi Jinta ba

Gareni Sun Tako
Mararina Suke Kullum basu Barniba

Ya Rabbi Ka nufa
Gani Zamanin da ake Gudun Mai gaskiya

Ya Mai Raya Rayayyen Marayan Daya Rayu Cikin rayuwa da Ruwayar Maruwaita Rayayyun Ruhi da Ra’ayin Ribar Rabauta A Ranar Ramawa Ramammun Ruhanan da suka Rayu Cikin Ramawa Rayayyen Rai Ra’ayinta Randa Ba’a Raina Rukunin Ribatar Raunin Ruwayar Rayayyu.

Ismail Hussaini Adam

Alpholtawy

JAWABAI MUHIMMAI

INGANCIN ZUQATAN BAYI

INGANCIN ZUCIYA!!! ***************************************** Hakika gyaran zuciya itace maqasudin kar´bar aiki. Da Akwai Ayoyi da hadisai ingantttu dake nuna jinjina ga ayyukan bayi amma dukkansu suna yabawane akan tsarkin zuciya domin shine (sababin karbar aikin). Hakazalika. ibadar da Allah yafisoma, ~Maqasudinsa zuciyace watau (Azumi).

Shi Azumi ALLAHﷻ (s.w.a) Shine kadai keda hakikanin gasgata maiyinsa, Saikuma Zuciyar maiyinsa, Sa`annan kuma ma ALLAHﷻ shi da kansa yake cewa yana son masu tuba damasu tsarki Ma´ana masu tsarkake zuciyoyinsu daga bari munanan ayyuka. Da ayyukan da aka kyamata. Gashinan in arabic text إن الله یحب التوابین ویحب المتطهری Manzon ALLAH ﷺyana cewa إن فی الجسد مضغة إذا صلحت صلح الجسد کله وإذا فسدة فسد الجسد کله علی وهی القلب Arufai kuyimin afuwa nai muku Shisshigi inda kuskere atusaddani. Dan Adam ajizine ALLAHﷻShine masani. dafatan anyi Juma`ah lafiya

MATAKAN TARBIYYA GUDA UKU


MATAKAN TARBIYYA
Daga. Alqalamin Ismail Smart
Dasunan ALLAH Mai RAHAMA Mai JINKAI.
Haqiqa tarbiyya dolece a addinin mu na musulunci musan man ma na iyalanka/ki
Domin ALLAH MADAUKAKI yana cewa:

یا أیهاالذین آمنو قو أنفسکم وأهلیکم نارا وقودها الناس والحجارة
        Awannan aya ALLAH yayi umarni ga Muminai dasu Kare kansu da iyalansu daga wata wutta Wanda yakasance makamashinta mutane ne dakuma duwatsu.
ALLAH UBANGIJI katsaremu amin  ya RABBI. Awannan ‘Bangaren Nakeson nayi rubutu  domin yan uwa musulmai su anfana.
ALLAH MADAUKAKIN SARKI ya dafamin
MATAKIN FARKO
(Neman Aure zuwa da yakai 5yrs)
Dole Akan kowa Idan yazo neman aure
Yanemi Mai addini Da hali nagari Da kakkyawar zuciya. Ba kawai kyawun fuskaba ko wani martaba ko nasabar Abokin zama ba. Kuma yazamto anyi auren tanasonsa yana sonta.
Domin hakanne Zaisa suji dadin zamantakewarsu ta Aure Kuma hakan Zaisa yayansu sutaso dason junansu Da Bin doka ko umarnin Da akayi masu. Domin kada yazamto uwa tace fari uba yace Bahakaneba Baki yake. Bayan haka
Yazama dole asakawa yaro kakkyawar suna alokacin dayake jinjiri. Yazama dole ka karantar Da matanka tsarin tarbiyyar addinin musulunci ko kasa akarantar da ita Awannan sahar kokuma MA kafin wannnan lokacin. Ma’ana kafin ta sami d’a (yara).
Domin kaso saba’in Cikin Dari (70%) Na Tarbiyyar cikin Gida maqasudinsa na uwace. Yazama dole takasance Mai Lura da Meke gudana me sukeso me yakamata suyi ko so Bari duk wadannan uwace takeda hakkin koyar da yaranta.
Dakuma koyardasu Ibaadaat Kamar Sallah Azumi Dakuma koyamusu karatun Alqur’ani da tilawarsa dama haddarsa. Har sukai 10yrs  Kafin daga bisani Sai Aturasu  Islamiya. Sucigaba da karatu daneman ilimin addini. Hakan zaisa sutaso da ganin girman iyayansu. Dama duk wanda yagirmesu tayadda basai ance ga malam waneba kafin sudaina abinda sukeyi.
MATAKI NA BIYU
(Daga 5yrs zuwa 15 to 18yrs)
Dolene akan iyaye su San abokanan yayansu, Susan Kuma menene alaqarsu dasu Domin duk kyawun tarbiyyar dakasamu agida abokai sukan wargazashi, matsawar dakayi abota da marasa tarbiyya koda baka zama tamkarsu ba. Zaka rudu da wani hali acikin munanan halayyarsu.
Yazama dole iyaye su bawa yayansu tarbiyyar addini da wayewar rayuwa tahanyar sanaddasu yadda zasuyi addini da hikimomin tsara rayuwa bisa kykkyawar tsari. Kamar koyamusu dabarun kare kai da addu’o’in neman tsari da kariya. Da sanardasu tarihohi Wanda zasu sami hikima da, wa’azozi acikinsa. Domin abinciken masana kwakwalwar dan adam sun yarda akan cewa kwakwalwar dan adam takan bude da adana bayanai alokacin da mutum yake dan shekaru takwas (8) zuwa Sha biyar (15) koda haddane mutum yafi nutsuwa dashi awannan lokacin Inhar kaga yaro ya natsu awannan lokacin to tabbas ana kyautata zaton shiryayye ne. Inkuma ya kangare kuwa yanada wuyar shiryuwa Yakamata iyaye sudunga zama da yaransu suna zantawa dasu domin suji damuwoyi da bukatunsu, Harsu san tahanyar da zasu bullo musu gurin bada shawara ko kore musu matsalarsu tarayuwa.
MATAKI NA UKU NAKARSHE
(Daga 15/18yrs. zuwa auraddasu)
Yakamata iyaye su lura da yayansu su san menene wane/wacce tafi/yafi kwarewa akai saisu dage gurin nema masu mafita ta hanyar basu tallafi ko jari domin samun damar gudanar da harkokin rayuwarsa cikin sauki batare da yana zauneba saidai kullum abashi.
      Domin hakan yana kashe zuciyar mutum yazanto baya iya kafuwa da kansa balle ma har yagina wasu. Saidai kullum a bani_bani sai kuma bin abokai da yawace yawacen banza da hofi, da bin bangar siyasa, wadda daga karshe ke jawo mutum yakoma ta’asa da ‘barna acikin al’uma kokuma ma yakama shaye_shaye da bin mugaye mutane. Duk adalilin rashin aikin yi. ALLAH ya tsaremu da zuri’armu baki daya.
       Rashin aikinyi na daya daga cikin abubuwa mafi girma wanda suke lalata  tarbiyya arayuwar mutane.
Allah ka bawa iyayen mu hakurin zama damu kasauke musu hanyar dazasu tarbiyyantar damu tarbiyya ta Addinin musulunci, ALLAH kajikan maifina kahaskaka qabrinsa.