MU KIYAYE ALLAH NIDA KU

Ismail Hussaini Adam

Bazamu Kauce Shari`ah Ba
Duk Wuya Bazamu rabe ba
Kunci Bazaisa Mu Sarye ba
Balle Wuya ba Mutuwa ba
Duk Rintsi Bazamu Rabe ba

Dan Arzikinka Ga Bayi Allah Tabbatar Mana Alkhairinka

Duniya Ba`a Zauna ba
Rayuwa ba Mutuwa ba
Zamani Ba Namutum ba
Arzikin ba Nakun ba
Iyawuya Ninakine Zainaba

Ya Zul jalalu Kaduba Isarmu Kabamu  Iyawar dan Tasirinka

Dafamana ya Rabbana
Ka iyamana ya Jalla na
Da Isarka ne Khaliqa na
Rayuwarmu Arzuq Na
Bi Izzatuka Ya Ahya Na

Ka Nuna Isarka Cikin Ayyukan Bayi Ka Tabbatar Da Samuwarka

Ya Arhamrrahimina
Ya Alimul Alamina
Ya Khairul Munzalina
Ya Fatihul Raziqina
Ya Alimussirruna

Alhayyul Qayyumu Bamu ikon Tuba Kayima duniya da Lahirarmu Tsari Ya Mai Tsarkin Tsarkaka

MATAN ZAMANI AYI HATTARA

  Duk iya Gyaran Bakanike Bazai Iya Maida Tsoho Izuwa Sabo ba, Komai Zaiyi Lallabene.

“Babu wanda zai so siyan abu sabo a kwali sai yaje gida ya bude ya tarar duk ya koke ko kuma yaga wani alamu da ke alamta cewa wani yayiamfani da abun kafin shi.

Wani zai iya daurewa ya cigaba da amfani daabun a haka amma ba da daďin rai ba,wani kumazai fusata ya mayar da abun inda ya siyo ne donyaji dalilin da zaa sayar masa da second hand amatsayin sabo,

Kada a rudu da rudin zamani don shi dai mutunci madara ne, don haka sai a kula!
Allah Ya shirya mu da zuri’ar mu gaba daya.”

Aishatu Bint Shafili

19 June 2021

  • Nasarorin Ƙungiyar Arewa Media Writers
    Nasarorin Da Ƙungiyar “Arewa Media Writers” Ta Samu Cikin Shekaru… Read more: Nasarorin Ƙungiyar Arewa Media Writers
  • TARBIYYAR ‘YA’YA AMUSULUNCI
    ══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════TARBIYYAR ‘YA’YA AMUSULUNCI══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁… Read more: TARBIYYAR ‘YA’YA AMUSULUNCI
  • ZATIN UBANGIJI
    SHAUQI CIKIN AL AMARIN GAIBIYYA Kasantuwar Ubangiji A Buya Bai… Read more: ZATIN UBANGIJI
  • GODIYA TA GA ALLAH BUWAYI
    Ban Shan Sigari Ban Shan MoringaBan Shan 200 Kayan zamani… Read more: GODIYA TA GA ALLAH BUWAYI
  • KUJI TAUSAYIN MARAYAN ALLAH
    Bansan me Nayi mussu baNufata da Sharri suke basu barniba… Read more: KUJI TAUSAYIN MARAYAN ALLAH
  • FASAHAR ZAMANI
    Menene capacitor?  Dauki masu gudanar da wutarlantarki guda biyu (abubuwan da suka bari Wutarlantarki ta ratsa su) sai ka raba su da insulator(kayan da ba su barin wuta ya ratsa sosai) sai kayi capacitor: wani abu da zai iya adanamakamashin wutar lantarki. Kara makamashinlantarki ga mai iya aiki shi ake kira caji ; fitar dakarfin daga mai iya aiki shi aka sani dadischarging. Capacitor yana dan kama da baturiya, amma yanada wani aiki daban. Baturiya na amfani dasinadarai don adana makamashin lantarki da sake shi a hankalita hanyar zagaye; wani lokaci (a yanayin agogonkwata) zai iya daukar shekaru da dama. Mai iyaaiki yana sakin karfinsa da sauri-sau da yawa acikin sakanni ko kasa da haka. Idan kana daukanhoton flash, misali, kana bukatar kyamararka don samar da babban burst na haskea cikin fraction na sakan daya. Wani mai iko daaka hađe da bindigogin flash na ‘yan sakanni taamfani da makamashi daga batirin kyamararka.(Yana daukar lokaci kafin caji capacitor shi yasayawanoci dole ka jira kadan.) Da zarar an caji maikarfin, zai iya sakin duk karfin nan take ta hanyarxenon flash bulb. Zap! What is a capacitor?Take… Read more: FASAHAR ZAMANI
  • MU KIYAYE ALLAH NIDA KU
    Bazamu Kauce Shari`ah BaDuk Wuya Bazamu rabe baKunci Bazaisa Mu… Read more: MU KIYAYE ALLAH NIDA KU

RAYIWAR YAN MATA

📝 QALUBALE GA RAYUWAR ‘YAN MATA ✍️ ******* GABATARWA *******

Assalamu alaikum warahmatullahi wabarkatuhu mai karatu.

Zanyi wannan rubutunne don nuni zuwaga yan uwana maza, domin kusan wa zaku auro ku kawo cikin gidanku, amatsayin abokiyar zama. Mata kuma su san dawa zasuyi qawance don gudun faďawa akomar halaka. Inda hali kutsaya kukaranta gabaki ďaya, domin zaka/zaki k’aru kuma inshaa Allahu zaku rabauta da waďannan zantuka nawa.

Ina bukatan addu’arku Allah ya haskaka qabarin mahaifina, dana mai karatu idan kuma suna raye, Allah yasa mugama dasu lafiya yakuma basu rabon cikawa da imani. Allah ka albarkaci rayuwar lahaifiyata da ayyukan alkhairi daku mumaďin gabaki ďaya.

‘YAN MATAN JAMI’A

Allah sarki rayuwarsu gwanin birgewane, saidai kuma abin tausayine awani bangaren, tayadda zaka samesu mafi yawancinsu akwai tsaftar jiki dana tufi. sannan sun san yakamata matuka, Saidai wasu acikinsu suna son yin aure kuma Suďin sun kame kansu. amma rashin dama takansa wasu acikinsu afkawa izuwa ga zina, Allah yakare. Hakan yana faruwane don rashin samun dama daga iyayensu. Zasu fidda gwani amma sai suce sam sai kin kammala karatu, sun manta da wasiyyar manzon Allah (s.a.w). Wasu kuma suna sheke ayarsune kawai tahanyar biyan bukatarsu ga maza, aduk sadda sha’awarsu ta motsa. Wasu kuma na fama da jimamin rayuwa tayadda suke fama da fuskantar barazanar lecturers lalatattu, da yunkuri batamasu tarbiyya da fansar jarrabawarsu da mutuncinsu. Iyaye ayi hattara zaku iya shiga wuta akan hakkin ‘ya’yayenku don rashin sadaukar musu da hakkinsu daya rataya akanku

‘YAN MATAN LUNGU

Idan akace matan lungu: sune mata masu talle akan titi, dakuma lungu da sashen unguwanni da sakokin ma’aikata, da shaguna (Kwantinan) kasuwanni. irin wadannan matan, idan basu sami kulawar tarbiyyaba sunfi kowasu mata sharri. Domin awani bangaren sukan ‘boye kamarsu suyi kama da mutanen kikrki amma sam bahakan bane azahirance. Kuma mafi yawanci acikinsune ake samun masu sace_sace, da bin maza bayan sunyi aure. domin sun saba da rike kudi masu kauri ahannayensu, ayayin budurcinsu. Hakazalika wasu acikin sunma suna saida budurcinsu kafin aure, a son zuciyarsu kokuma ara’ayin iyayensu mata. Ko uwayen goyensu na bariki. tayadda sukan taradda wulakanci agun mazajensu, dalilin rashin budurci bayan sunyi aure, hakan yake tursasu fita karuwanci bayan aure, ko sata wa mazansu na aure.

‘YAN MATAN BARIKI

Irin wadannan matan basuda mutunci. wanda su kansu sun yadda da hakan, kuma suna iya furtawa da kansu cewa su marasa kunyane amma daga fitsararrun cikinsu. Irin wadannan matan sukan tasone aguri mai lalacewar tarbiyya.

A gunda iyayensu ke zaune babu tarbiyya kuma iyayen basu kulawa da tarbiyyarsu. kuma babu addini agunda suke zaune. Saidai holewa da sha’anin duniyanci dakuma ta’ada, da muta kabbaranci. Ga uwa uba rashin dattako don ko waye ‘yar bariki zata zaki asalinsa ko da kuwa shugaban unguwarsune ko sarkin gari. Wadannan matan ko acikin garine shigarsu daban take sune Manzon Allah (s.a.w) yayimanz ishara dasu acikin hadisi ruwayar bukhari da muslim ” Akwai wasu nau’in mutane da Annabi baigansuba amma zasuzo anan gaba yake fadawa sahabbansa. Yace dasu dukkan wadannan mutane ‘yan wutane. ” na farko dai shugabanni azzalumai yake nufi kokuma masu hukunci da zalinci. nabiyu kuma yace; wasu matane zaku gansu da kaya ajikinsu amma tsaraicinsu na waje suna tafiya suna karairaya jiki, sa’annan kawunansu kamar tozon rakumi, yace kuma bazasu shiga aljannaba, kuma bazasu ta’ba jin kanshin aljannah ba. Domin awani qaulin anajin kamshin aljanna a tsahon tafiyar shekaru dari biyu ko dari biyar.” Allah kakare ‘ya’yanmu da ‘ya’yan ‘yan uwanmu daga Gurbacewar tarbiya.

‘YAN MATAN ASALI

Allah sarki wadannan sune abin tausayi, kuma sune masu wahala, kuma sune masu rabauta duniya da lahira. Tayadda suke fitowa daga gida na mutunci, iyayensu nagartattune su kuma kamammune. Sukan rike budurcinsu iya jimawar da zasuyi gabanin suyi aure. dashi suke samun martaba da nagartar zamantakewarsu ta aure. Kuma kafin suyi aure basu koda cakuduwane cikin maza ballema suyi wani mummunr mu’amala da namiji, hartakai ga sun zubadda mutuncinsu da budurcinsu. Suna matukar Kula ha hakkokin dake kansu na addini dana zamantakewar rayuwa. sune Allah ya ambacesu acikin Alqur’ani yadda yake cewa a Suratul_ahzab. surah ta-33 Aya ta:35 ”Lalle, Musulmi maza da Musulmi mãtã da muminai maza da muminai mãtã, da mãsu tawãli’u maza da mãsu tawãlĩu mãtã da mãsu gaskiya maza da mãsu gaskiya mãtã, da mãsu haƙuri maza da mãsu haƙuri mãtã, da mãsu tsõron Allah maza da mãsu tsõron Allah mãtã, da mãsu sadaka maza da mãsu sadaka mãtã, da mãsu azumi maza da mãsu azumi mãtã da mãsu tsare farjõjinsu maza da mãsu tsare farjõjinsu mãtã, da mãsu ambaton Allah da yawa maza da mãsu ambatonsa mãtã, Allah Ya yi musu tattalin wata gãfara da wani sakamako mai girma.”

Hakika mata masu addini sune mafi dacewa ga dukkanin wani ďa namiji musulmi. Kuma sune zakasamesu masu kyakkyawan hallayya dakuma tsaftatacciyar budurcin wanda babu kazanta acikinsa.

Duk da cewar kwaciyar aure na rana daya tak, yana wanke dattin kazantar bariki, duk jimawar da akayi dashi. Amma kuma duk da hakan kazanta bariki, yakan sanya zargi atsakanin ma’aurata, Zargi na har abada. Musamman ma yazamanto shima mijin mutumin banzane.

Allah karabamu da danasanin duniya da hasarar lahira. Ameen Dukkannin wanda yakaranta wannan rubutun nawa ya sanya aransa shima zai bada gudun mawa wajen gyara yau da goben Al’umar mususulmi kusani acikin addu’arku dani da mahaifana. Albarkacin wannan wata mai albarka ta Raladhana.

MATAKAN TARBIYYA GUDA UKU


MATAKAN TARBIYYA
Daga. Alqalamin Ismail Smart
Dasunan ALLAH Mai RAHAMA Mai JINKAI.
Haqiqa tarbiyya dolece a addinin mu na musulunci musan man ma na iyalanka/ki
Domin ALLAH MADAUKAKI yana cewa:

یا أیهاالذین آمنو قو أنفسکم وأهلیکم نارا وقودها الناس والحجارة
        Awannan aya ALLAH yayi umarni ga Muminai dasu Kare kansu da iyalansu daga wata wutta Wanda yakasance makamashinta mutane ne dakuma duwatsu.
ALLAH UBANGIJI katsaremu amin  ya RABBI. Awannan ‘Bangaren Nakeson nayi rubutu  domin yan uwa musulmai su anfana.
ALLAH MADAUKAKIN SARKI ya dafamin
MATAKIN FARKO
(Neman Aure zuwa da yakai 5yrs)
Dole Akan kowa Idan yazo neman aure
Yanemi Mai addini Da hali nagari Da kakkyawar zuciya. Ba kawai kyawun fuskaba ko wani martaba ko nasabar Abokin zama ba. Kuma yazamto anyi auren tanasonsa yana sonta.
Domin hakanne Zaisa suji dadin zamantakewarsu ta Aure Kuma hakan Zaisa yayansu sutaso dason junansu Da Bin doka ko umarnin Da akayi masu. Domin kada yazamto uwa tace fari uba yace Bahakaneba Baki yake. Bayan haka
Yazama dole asakawa yaro kakkyawar suna alokacin dayake jinjiri. Yazama dole ka karantar Da matanka tsarin tarbiyyar addinin musulunci ko kasa akarantar da ita Awannan sahar kokuma MA kafin wannnan lokacin. Ma’ana kafin ta sami d’a (yara).
Domin kaso saba’in Cikin Dari (70%) Na Tarbiyyar cikin Gida maqasudinsa na uwace. Yazama dole takasance Mai Lura da Meke gudana me sukeso me yakamata suyi ko so Bari duk wadannan uwace takeda hakkin koyar da yaranta.
Dakuma koyardasu Ibaadaat Kamar Sallah Azumi Dakuma koyamusu karatun Alqur’ani da tilawarsa dama haddarsa. Har sukai 10yrs  Kafin daga bisani Sai Aturasu  Islamiya. Sucigaba da karatu daneman ilimin addini. Hakan zaisa sutaso da ganin girman iyayansu. Dama duk wanda yagirmesu tayadda basai ance ga malam waneba kafin sudaina abinda sukeyi.
MATAKI NA BIYU
(Daga 5yrs zuwa 15 to 18yrs)
Dolene akan iyaye su San abokanan yayansu, Susan Kuma menene alaqarsu dasu Domin duk kyawun tarbiyyar dakasamu agida abokai sukan wargazashi, matsawar dakayi abota da marasa tarbiyya koda baka zama tamkarsu ba. Zaka rudu da wani hali acikin munanan halayyarsu.
Yazama dole iyaye su bawa yayansu tarbiyyar addini da wayewar rayuwa tahanyar sanaddasu yadda zasuyi addini da hikimomin tsara rayuwa bisa kykkyawar tsari. Kamar koyamusu dabarun kare kai da addu’o’in neman tsari da kariya. Da sanardasu tarihohi Wanda zasu sami hikima da, wa’azozi acikinsa. Domin abinciken masana kwakwalwar dan adam sun yarda akan cewa kwakwalwar dan adam takan bude da adana bayanai alokacin da mutum yake dan shekaru takwas (8) zuwa Sha biyar (15) koda haddane mutum yafi nutsuwa dashi awannan lokacin Inhar kaga yaro ya natsu awannan lokacin to tabbas ana kyautata zaton shiryayye ne. Inkuma ya kangare kuwa yanada wuyar shiryuwa Yakamata iyaye sudunga zama da yaransu suna zantawa dasu domin suji damuwoyi da bukatunsu, Harsu san tahanyar da zasu bullo musu gurin bada shawara ko kore musu matsalarsu tarayuwa.
MATAKI NA UKU NAKARSHE
(Daga 15/18yrs. zuwa auraddasu)
Yakamata iyaye su lura da yayansu su san menene wane/wacce tafi/yafi kwarewa akai saisu dage gurin nema masu mafita ta hanyar basu tallafi ko jari domin samun damar gudanar da harkokin rayuwarsa cikin sauki batare da yana zauneba saidai kullum abashi.
      Domin hakan yana kashe zuciyar mutum yazanto baya iya kafuwa da kansa balle ma har yagina wasu. Saidai kullum a bani_bani sai kuma bin abokai da yawace yawacen banza da hofi, da bin bangar siyasa, wadda daga karshe ke jawo mutum yakoma ta’asa da ‘barna acikin al’uma kokuma ma yakama shaye_shaye da bin mugaye mutane. Duk adalilin rashin aikin yi. ALLAH ya tsaremu da zuri’armu baki daya.
       Rashin aikinyi na daya daga cikin abubuwa mafi girma wanda suke lalata  tarbiyya arayuwar mutane.
Allah ka bawa iyayen mu hakurin zama damu kasauke musu hanyar dazasu tarbiyyantar damu tarbiyya ta Addinin musulunci, ALLAH kajikan maifina kahaskaka qabrinsa.

BAYAN RAYUWAN DUNIYA AKWAI RAYUWA BAYAN MUTUWA

GASKIYA AKWAI MATTSALA!!!!


Sau nawa kake zama domin Bincike ko sauraron Yadda zaka gyara Ibadarka?????
         Sau dadama idan na kadaita sai nayita tunani dan ganeda lammarin gudanar addini agun wasun mu. Zakaji mutum nakiran kansa musulmi amma farillan alwala ma bai sani balle in ta ‘baci ya gyara farillan sallah ma bai saniba balle inyayi Rafkanuwa yagyara. Ko na wanka ballema ilimin gyaransu.
    Wayyoooni duniya ina zaki damune kowa kagani abinci kawai yake nema kokuma yadda zai huta ko yadda zaiji dadin duniya gaba. Saidai kash itakuma tafiyarnan da take gaban mu batta da rana. Kawai zuwa take kwatsam kara zube ba zato ba tsammani.
    To taya zamu tara guzirin komawa ga mahaliccin mu domin samun hujja garemu aranar sakamako?
    Ansa
    Mukoma munemi ilimin addini mugyara ibadu da mu’amalarmu kafinnan musami hanyar tsira. Wani abin ban takaici shine yawanci mukan jahilci lammarin addini bawai don rashinsaba sai don aqidanci. Mutum baida karatun komai jahilin kauye afagen addini amma saikaji na karyata abubuwan da malamai ke fada dan ganeda hukuncin halasci ko haramcin wani al Amarin addini. Dalili kuwa shine don aqidarsu ta banbanta, Alhali baida hujja ta aya ko hadisi data karyata al’amarin dalili kawai don malumansu basayi yan abiyari (inbasu wane bazamuyiba).
    Wannan shi ake kira da shi’anci ashari’ar musulunci ma’ana raba kan al’umar musulmi. Tahanyar sabawar fahimta ko mazhaba. Abubuwan da kejawo haka sune:
    _Jahilci
    _Son zuciya
    _Son shahara
    _Munafinci
          ***JAHILCI***
    Idan jahilci yayi naso (katutu) azuciyar mutun saikaga na karyata koma mene ne addini ni kuma in yayi shugabanci zai dinga shirme yayita kawo jahilci alammuran dasunan gyara daga karshe zaiyita kokarin fada da malamai idan suna fada masa gaskiya. Jahilci nasa girman kai da hassada matukar maishi na tare da masu ilimi kuma akayi rashin sa’ah yawuce su wata daukakaka tarayuwa.
       ***SON ZUCIYA***
Idan mutum nada son zuciya komai aka fada bazaibiba sidai yakowo tasa abi. Koda tasa hanyar me raunice zai toge yadage akan sai anbi tasa daga karshe in anki zai fara neman mabiya daga baya saikaji ya Fidda tasa sabon kungiyar daban ko juma yafandare yayi reshe akungiyarsa daban.
    ****SON SHAHARA****
    Mafiya yawanci anfi samu daga wanda suka ‘Danyi karatu amma bamai nisaba sunason taka hawa mai nisa amma kafarsu baikaiba. Burinsu dai komai zai wakana yazam anyishi harda furucinsu. Amma basuda cikakken ilimi abangaren irin wadannan ywanci akansamu masu kyakkyawar manufa amma rashin ilimi mai nisa yana wargaza manufar nasu.
    Yakai dan uwa shawarata gareka katsaya iya matsayin ka kabar abinda Bakasaniba.
    Masu hikima nacewa Bansaniba shima wani yankin ilimine.
   
      *****MUNAFINCI****
    Akwai wasu burinsu kawai azagi musulunci da musulmai. Zasu tsaya kai da fata su tabo wannan aqidan da wata ta daban, Harsu haddasa wata rigima tsakanin musulmai wadannan basuda wata kyakkyawar manufa akan musulmai wasunma bamusulmai bane burinsu su wargaza wata shiri ko wata tanadi wacce musulmai sukeyi, ko don su raba kawunan al’umar musulmi.
    Allah katsaremu daga sharrin makirai da fajiran munakan addini.
    Allah yamayar da makircin garesu dasu da wanda suke sasu.
    Allah kabudemana kwakwalenmu don gujewa afkawa rudanin addini.
    Allah  kabawa maluman mu damar isar mana da gaskiyar koyi na Addini.