
Zamu Daura Guda Goma insha Allahu muna Kyautata Zaton Zakuci Moriyarsu.
.

Zamu Daura Guda Goma insha Allahu muna Kyautata Zaton Zakuci Moriyarsu.
.























AN BAMU ILIMI KYAUTA! MUN WATSAR! MUN SAYI JAHILCI DA KU’DINMU!
Shin Mecece Makomarmu?
Halaka, Tabewa, Ko Asara !!!
ALLAH ﷻ Katsaremu.
Shirmen Yahudu Muka Dauka Muka Shagaltu Da Abinda Ke Cutar da Rayukanmu, Na Shagaltuwa da Kida, Wakoki, da Kallace_Kallae, Mun Bar Da’irar Tsira Hanyar da Ake Rayar Da zuciyoyinmu Ana kashe Mana Kasala, Taskar Sani Dangujewa Jahilci Rumbum Asirai (Quran da Hadisan Annabi (S.A.W) }. Shiyasa Yahudu Ke Juya Zuciyoyinmu Yadda Sukaga dama
Zan Gina Wannan Rubutun Nawa Ta Hanyar Tuna baya, Atarihin Rayuwata Inda Abaya Na kasance Mai Sanin Darajar Kaina, Allah Ya Yassaremin Rayayyiyar Zuciya Tun Ina Karamina.
Afannin ilimi babu Bajimta da Dalibi Zaiyi Amakaranta wacce zata gagareni (Ilimin Addini Dana Zamani) Balle Tafi Karfina. Yadda na zamo Fitila Atsakaninmu Dalibai Yasa Rayuwata Ta Bunkasa, Duk da halin Rashin Dama Amma Ina Alfahari dakaina, Akanyi kuma Tunkaho dani Akowace Sansani.
Nakusan Yin Sakaci Bisa Samun damar Da ta Yanke min Buri, Alokacinda Ban Cika Hankaliba, Balle tunani Ya zakkemin. Kwatsam Sai Rauni Yafara Fisgata Bisa Ta’bar’barewar Zamani, Nakasar Shagaltuwa Yafara Tabin Jinina Yafara Samin Kasala, Dakyar Na farka Daga Baccina. Lokaci ‘Kalilan Naji Shagalar Tawa Amma Sai da Nad’auki Dogon Zango Kafin Na Gyara Saitin Akalata, Dayardar Allah Saitin Ma’ajin Bayanaina Ayanzu Sun Kankama Tunda Hankali Yakusa Fara Zuwa (22Yrs Ba Wasaba), Tabbas fa Ashe Kowa Nada Hankali, Amma Aiki da Hankali Sai Da Dafawar Ubangiji.
To Taya Ubangijin Zai Dafa Mana Bayan Mun Butulce Masa?
Nidai (Ismail) Yarone,
Ina Manyan Suke?
Kutayani Duba Ance Kunada Hangen Nesa
Ni na Tabbata Bin Tafarkin Ma’aiki Da Yawan Ibada Itace Ke Raya Zuciyar Dukkan Wani dan Adam, Ba Shagalin Duniya Da Sha’anonin Rayuwa Na Shagala Ba.
Inka Kauracewa Shirmen Duniya Komai Ka Nema Agun Allah kuwa, Abinda ka Nema da kansa Zai kawo Kansa Wallahi Basaika wahalar da Gangar Jikinka ba. ALLAH Ne Yasanar Damu Hakan.
Duba Hadisul_Qudsi, Zakaga Ga Hujjana.
Dalibi, Danuwa, Yaruwa, Aboki, Yana, Yayata, Iyayena, Yan Uwana Musulmi Ga Shawari Kyauta!!!
Mu Kauracewa Mummunar Dabiar Shagala Na Haukar Yahudawa Musamman Sauraron Kida Da Kallon Film Wai Domin Shagala Dan Cire Damuwa Abanzane, ‘ Wallahi ‘Karin Damuwa Nema’ Domin Acikinsa Ake Sauya Tunaninmu, Ake Kwashe Kaso Mafi Yawa Na Lokutan dayakamata Muyi Ibadojinmu Kuma Yana Disashemana Kaifin ‘Kwa’kalenmu, Ka dauki Littafan karatu Su Zamo Abinda kake Goge Hawayen Damuwoyinka Da Dawo Farinciki Idan ya gujemaka, Gamaiyin Hakan Kuwa Tabbas Ribarsa Babu Adadi.
Samun Sau’kin Rayuwa,
Gujewa halakar Yahudawa,
Raya zuciya da cire Damuwa,
Fayyace Dukkan Mattsala,
Barin Sansani Na Jahilci zalla,
Fidda Jinyar jiki dama Kalsala,
Cire wa Kai Son Duniya,
Tarewa Atafarkin Shiriya,
Kaji Zancen Gobe Yau har jiya,
Babu Cutar Rai Ba Tsangwama,
Zallar Gaskiya ba Gardama,
Asalin Zance ba tantama,
Ba Ra’ayi Ga Sirrin warwara,
Alkairine Ga Sanin Fikira,
Cire kwadayi da Takura,
Inkana Neman Zallar Tsarkaka,
Tarin lada Kuma Ga Haskaka,
Bi Islam Addininnannaka,
Wallahi Komai Akwai Amusulunci, Rashin Neman Na Addinine Yasa Muke Kwaikwayon Yahudu, Mutanen Da Dasu da Dabbobi Babu Maraba Mu’amalolinsu Kamar na Dabbobi,
Zina Agunsu Adoce,
Zubar da Jini Aikin sune,
Cin Hakikkin Wani Gatane,
Kin Bautar Allah Burinsune,
Raba Kan Mutane Halinsune,
Son Zuciya Agurinsu damane,
Shan Kayan Maye Dad’in sune,
Amma Annabinmu Ya Nesanta Kuma Yatsawatar Garemu Akan Irin Wadannan Munanan Ayyukan Nasu. Tsarkinsa Ta Tsarkaka da Tsaftar Tsammanin Tsular Tsiyar dasuke Tsalawa Domin Tsageranci, Tsafatar Tsarkin Tsarkakakken Tsariran damai Tsari Ya tsareshi Ta Tsarkaka daga tsiyar Tsokanar da Tsagerun Tsinannun Yahudu Suke Tsulamasa.
Muna Sonka Annabinmu!!!
Masani, Lamani, Tsani, Sansani,
Ma’aiki, Sadauki, Tafki,
Jagaba, Shugaba,
Annabi.
Sirrin Yahudu Kenan Daga Alpholtawy (IHSAN) Writer

ALAKAR SHEIKH DR AHMAD GUMI DA MASU GARKUWA DA MUTANE
Kada kayanke Hukunci Sai Ka karanta Dukka
Bayan da Gwamnatin Nigeria karkashin jagorancin Maigirma shugaban kasa Alhaji Muhammadu Buhari Maigaskiya ta dauke service network a jihar Zamfara domin sojoji su gudanar da aiki na musamman akan masu garkuwa da mutane da suka samo asali daga yankin Zamfara suka yadu zuwa wasu jihohin Arewa
Ance Sheikh Dr Ahmad Gumi yace bai kamata Gwamnatin Nigeria ta kyale sojoji suna ruwan wuta ta sama da kasa akan sansanonin barayin dajin Zamfara ba suna hallakasu mazansu da matansu da yaransu, Malam yace kamata yayi Gwamnatin Nigeria ta yiwa barayin afuwa kamar yadda ta yiwa tsagerun Niger Delta afuwa
Fadin wannan maganar naga jama’a suna ta kokarin cin mutunci da zagin Sheikh Dr Ahmad Gumi, har ma wasu suna kira cewa a kamashi, wai yana goyon bayan barayin bindiga, wannan ne ya bani karfin gwiwa domin nayi wannan rubutun
A hakikanin gaskiya duk wanda ya zargi Sheikh Dr Ahmad Gumi da alaka da ‘yan bindiga ko tarayya cikin ayyukansu na ta’addanci to mai wannan zargin idan har ba makiyin Musulunci bane idan ance yana da kwakwalwar jakuna ba laifi bane
Dr Ahmad Gumi sulhu yake jagoranta, kamar yadda aka taba samun wadanda ba Musulmai ba suka jagoranci sulhu tsakanin Gwamnatin Nigeria da tsagerun Niger Delta, aka taba samu har da turawa makiyanmu makiya addinin mu suka jagoranci sulhu tsakanin Gwamnatin Nigeria da ‘yan Boko Haram kan musayen ‘yan matan Chibok
Kowa ya tsaya yayi tunani, shin menene ya faru muka wayi gari fulanin jeji makiyaya suka dauki bindiga suka zama barayin jeji masu garkuwa da mutane?
Wanda bai san abinda ya faru ba to ga cikakken bayani
(1) Rashin adalci na wasu jami’an tsaron Gwamnatin Nigeria Azzalumai maciya amana shi ya tunzura fulanin jeji suka dauki makami suka zama ‘yan ta’addan dole
Wato idan wasu azzaluman jami’an tsaro suka shiga jeji neman barayin shanu, duk wani bafulatani da aka gani yana kiwo sai a kamashi ko a harbeshi a kora shanunsa, ana kashe iyayensu akan idon su, ana kama matansu ana musu fyade a kan idon su, wannan yasa sukace tunda bamuyi komai ba ana kashe mu ana kwace mana shanu to bari mu dauki makami muyi ta’addancin da tushe domin daukar fansa
Wallahi wannan shine farkon abinda ya jawo fulanin jeji suka zama ‘yan ta’adda, marigayi Alhaji Ali Kwara ya tabbatar da wannan a hiran da VOA Hausa tayi dashi, su kansu manyan Kwamandojin barayin daji sun tabbatar da wannan zalunci da wasu jami’an tsaron Gwamnati suka musu a farko, shi ya kaisu zama ‘yan ta’adda a yau
(2) Sannan sai sakaci da Musulmai sukayi: wato aka ki shiga jeji a karantar da fulani addini aka barsu cikin bakin duhu na jahilci, ‘yan bazata (Missionary) suka shiga suka canza musu addini, Faransa ta shiga ta karkashin kasa ta basu makami, Boko Haram da Ansaru suka hada kai dasu suka fara zubar da jinin al’umma ba gaira babu dalili
A takaice wannan shine abinda ya faru, sannan a ilmin tsaro an kasa nau’ukan ta’addanci gida hudu:
Cikin na’ukan ta’addanci guda hudu, uku daga cikinsu suna da saukin magancewa, kuma ilmin tsaro ya tabbatar da ana iya yin sulhu da su imbanda wanda suke ta’addanci akan akida ta addini wanda suke fatan su mutu a kai.
Fulanin jeji suna ta’addanci ne akan daukar fansa, ashe za’a iya yin sulhu da su idan sulhun za’ayi da gaske
An gwada yin sulhu da wasu barayin jeji amma ba’a sanya gaskiya a ciki ba, kuma rashin gaskiya yafi yawa daga bangaren Gwamnati, an sanya yaudara ne saboda ana da wata boyayyar manufa ga zaman lafiya da tsaron Arewacin Nigeria, wannan shine abinda Sheikh Dr Ahmad Gumi yake ta kokarin fahimtar da al’ummar mu
Ni da ku mun sani cewa Sheikh Dr Ahmad Gumi abinda yakeyi ba wai yanayi don biyan bukatar kansa da na iyalansa bane, shi a yadda yake yanzu har ya koma ga Allah Gwamnatin Nigeria zata bashi tsaro a duk inda zai je ya dawo, don haka yanayi ne saboda ni da kai ‘dan uwa talaka wanda bamu kai matsayin da za’a bamu sojoji da ‘yan sanda suyi gadin mu ba har karshen rayuwa
Idan akwai kuskure cikin kokarinnda Dr Ahmad Gumi yake na ayi sulhu to bai wuce guda daya ba, zanyi bayani a rubutu na gaba Insha Allah
Muna fatan Allah Ya tsare mana Sheikh Dr Ahmad Gumi, Allah Ya kawo mana sauki da mafita a tsaron Nigeria
Amin Yaa Hayyu Yaa Qayyum


SUWAYE KHAWARIJ???
Sune Mutanen da Banbancin Aqida Ko Maslahar Rayuwa Tasanya Suke Kafirta Shashin Wasu Bangare daga Cikin Musulmi Bisa Ko Da Ilimi Ko Babu Kuma Suna Kisa, Wacce takai Har Suka ‘Dauki Makami Suna Ya’kar Musulmi Suna Kashesu Kuma Suna Halartar da Jinanansu, Wanda hakan Yasamo Asaline: Daga Tsatson Wani Mutum Mai Suna Zul Khuwaisirah Attamimi.
Wanda Bayan Anyi Yakin Hunain
Bayan anyi Sulhul Hudaibiyya
Ansamu Ganima ayakin Hunain, Manzan Allah ﷺ Yazo Rabo, Sai Munafukai Suka Fara Gutsiri Tsoma Cikin Zancensu Suna zargin cewa Annabi ﷺ Bazaiyi Adalci ba, Suna Wannan Tattaunawar Tasu Cikin Ayarinsu na Munafukai Sai Wannan Mutum Mai Rashin kunya ( Zulkhuwaisirah Attamimi)
Yace: Shifa Saiyaje Yasameshi Danme Baza afadamasa Gaskiya ba Cewar Su Annabi ﷺBazaiyi Adalci ba.
Bayan Hakane Wannan mutumin Mara Mutunci Yazo Kan Annabi Cikin Yanayi na Rashin Kunya Yana Cewa: Da Annabin ”Kaji Tsoron Allah Kayi Adalci” Wa’iyazu Billah ALLAH Ka La’anci Khawarij Makasa Dangi da Sahabban Manzan ALLAH ﷺ.
Cikin Sanyin Murya Annabi Yace Dashi ”Yanzu Inbanyi Adalci ba Waye Zaiyi Adalci ” ﷺ.
Nan da Nan Sayyadina Umar Yazare Takobi Yace: Ya Rasulalllah Barni Insare Wuyarsa Sai Annabi Yace Dashi: ”Barshi Koka Kasheshi Yana da Tsatso, kuma Wasu Zasu Bayyana a Karshen Zamani Makamantansa, Wadanda Idan kaga Sallahr Su Saika Raina Taka, Komai Sukan yi Na Addini fiye da yadda kuke Zato, Amma kuma Suna Fita Daga Addinin Kamar Yadda kibiya Ke Fita daga cikin Baka, Annabi ﷺ Yayi ta Bada Misalinsu kafin Karshen rayuwar sa, Yadda Yakara da cewa Zakagansu Suna Da kananan Shekaru, Kuma Suna Karanta Alqur’ani Amma Bai Wuce Makoshinsu (Ma’ana Babu Alamun Sanyashi Cikin Ayyukansu).
Kuma Suna da Tsantsan Rashin kunya da Nuna Tsantsaini Akan Duniya, Sunada Wofantattun ‘kwa’kwale (Abu Kad’an Yakan iya Canza Tunaninsu).
Sannan Suna Kafirta Kowa Wanda Baibin Bayansu, Idan Fitinarsu Ta tashi Za Su rin’ka Kashe Musulmi Suna Barin Kafirai, Suna da Jayayya dakuma Rashin Amintaka da Yan uwansu Musulmi, Amma Ba Ruwansu da Kafirai, Burinsu Kullum inane Musulmi Yayi Ba Daidai ba (Bin Diddigin Musulmi).
Kuma Burinsu Akullum Nasu Itace Turba Inzaka zamo Mafi Tsoron Allah agun Kowa Inbaka Cikinsu Kai Ba Musulmi Bane agunsu Dan Haka Idan Sun Bayyana Ku Kashesu Ku kashesu Ku kashesu.
Bayan Zamani yayi Nisa Kuwa Sai Wadannan Mutane Suka Bayyana Danhaka Suka Fara Sa’insa da Gofnatin Musulunci Tun Azamanin Sayyadina Umar (R. A) Alamun Hakan Tafara Bayyana, Amma Basu Ware Kansuba, Sun Fara Bayyana kansune cikin Munanan Halayyar su Wanda Annabi ﷺ Ya Ambata, Ananne Suka Fara Nuna Adawarsu Da Tawayensu ga Gofnatin Musulunci Haryakai ga Sun Fara Gutsiri Tsoma Ga Shugabancin Gofnatin Na Sayyadina Umar.
Aganinsu Umar Yana Tsanantawa Gurin Hukunci Tayadda Akasamu Wani acikinsu Mai Suna: Abu Lu’uLu’il Majusi Ya Sokeshi Sayyadina Umar (R. A) Da Wu’ka Acikinsa, Wanda Wannan Itace tazamo Jinyar da Tayi Sanadin Shahadarsa.Bayan Shahadar Sayyina Umar (R. A).
Sai Sayyadina Usman Yacigaba Da Khalifanci, Wadda dama Annabi ﷺ yafada Wa Sayyadina Usman Cewa: Zaiyi Shahadane Tahanyar hakurin da Zaiyi Yayin Wata Musiba Da Zata Shafeshi, Hakurinsa Itace Maslahar Al’uma Sannan kuma itace Zata Kaishi Aljannah, Zaiga Musiba Akarshen rayuwarsa Dan haka Saiyayi hakuri, Inji Annabi Muhammad ﷺ Saboda haka: Bayan Ya Sami Nasarar Zamowa Khalifa, Sai ya Umarce Mutanen Sa cewa Kada Wani Ya Tunkari Mutanen da Duk Sukazo Domin Niman Ransa. Domin Tunawa Da Wasiyyar Manzan Allah ﷺ Domin Yasan Cewa Shahadace Karshen Rayuwar sa, Kuma Hakan Zai Farune Tahanyar Wasu Daga cikin Musulmi.
Dan Hakane Har Suka Samu Suka Hauro Katangar gidansa, Suka Sameshi na Karanta Alqur’ani Sukayita Saransa Harsai da Jininsa Ya Zuba Akan Alqur’ani Alhali Yana Azumi, Amma Ko Daga Kansa Baiyi ba Haryakai ga Yayi Shahada Sukuwa Suka Fice daga ciki Gidan Sukayi Tafiyarsu, Sunyi Masa Wannan Ta’addancine: Domin Aganinsu Suna Ganin Cewa Yana ‘Daura Danginsane Kad’ai Amuqaman Gofnatin, Kuma ‘Yan Qabilarsane Danhaka Dangoginsane da Gofnatin, Sukuma Sunfison Dangin Manzan ALLAH ﷺ.
Amma hakikanin Gaskiya itace Zalunci Ne kawai Da Tayarda Rikici wa Addinin Musulunci.
Sannan kuma Sai Wadannan Mutanen dake Inkarin Mulkin Na Sayyadina Usman (R. A): Suka Nemi Sayyadina Aliyyu (R. A) Daya Maye Gurbinsa, Acewarsu Yacigaba da Khalifanci Da Jagorancin Musulmi,
Sukayita Kurarashi Da Wasu Dadin Baki Amma Sayyadina Aliyu Yaki Amincewa, Domin Acewarsa Yanajin Kunyan ALLAH Akan Wannan Al’amari, Ankashe Wanda ALLAH da Mala’ikunsa sukejin Kunyarsa, Dan haka Shi Da’awa Yasaba Abarshi Yayi Da’awarsa Azabi Wani Yayi Shugabanci. Sai da Wasu Daga Cikin Manyan Masu Fad’a aji na Sahabbai Suka Sa Baki Sannan Sayyadina Aliyu Ya Amince.
Dalilin Daya’ki Amince wa Kuwa: Shine Yana Ganin Cewa Bayadda Za’ayi Ayi Wa Sayyadina Usman Wannan ‘Danyan Aikin Bai Dauki mataki ba, Sannan Kuma Ace Ya Zamto Anbashi Ragamar Shugabanci Kunsan Aliyyu Kadanga Ne: Kasar Yaki Dan Baffan Manzan ALLAHﷺ Aganinsa Ankatse Masa Dukkan Wata Damarsa ta Ganin Ya ‘Dauki Mataki Danganeda Al’amarin Matukar Aka Bashi Ragamar Mulki.

Bayan Ya amince da Yarjejeniyar Zama Khalifane: Domin magance dakuma daidaita Tsakanin Matsalar Musulmi Domin Khawarij Suna Sonsa Sannan kuma Sauran Sahabbaima Shine Za’binsu, Domin Su Wadannan Mutane Sunce Babu Wanda Zaiyi Jagoranci Awannan Lokacin Sai Shi Sayyidina Aliyyu. Kuma Wasu daga cikin Mutanen kirki acikin SAHABBAI Suma Sungoyi Bayansa. Awannan Lokaci Yaga Maslahar Al’umar kawai Itace Ya Rungumi ‘Kaddara Ya Cigaba da Khalifanci.
Bayan Ya Amince da Hakan Ya Kuma Samu Mubaya’ah daga Dukkan SAHABBAI, Sai Kuma Suka ‘Kara Kunna Wata Sabuwar Rigima, Ta Cewar Sai Ankamo Wadanda Suka Kashe Sayyadina Usman, Domin A Aiwatarwa Musu Da Hukuncin Alhali Kuwa Babu Wanda Yasan Su waye Suka Kasheshi.
Daganan Sai Suka Fara Rura Wutar Rigima Tsakanin Musulumi Na Yankin Madina, Har Rikicin Yafara Shafan Wasu Daga Cikin Sassan Sauran ‘kasashen Musulmi, Wanda Har Wasu Daga cikin SAHABBAI Masu Kyakkyawan Manufa Sanda Wannan Rikici Yaritsa dasu, Wasu Kuma Suka ‘Ki Sanya Baki cikin Rikicin, Wanda Harda da Matan Annabi ﷺ Wadda Dama Suna Madina aka Kashe Sayyadina Usman, Lokacin Sunzo Hajji ‘Kar’kashin Jagorancin Aishatu (R. A). Dasauran Matan Manzan Allah ﷺ Duk Sun Daidaita Akan Cewa Sayyadina Aliyu Yafara Bincike Ya Hukunta Wadanda Sukayi Wannan ‘Danyan Aikin. Shikuwa Sayyadina Aliyyu Burinsa Daidaita Al’amarin Shugabanci Kafin Tsara Yadda Gofnati Zata Gudana, Kafinnan Sai Ya Fara Bincike.
Daganan Bayan Haka Aka Kai Koken Zuwaga Mu’awuya Tahanyar Wadannan Munafukan, Wadda Shikuma Sayyadina Usman Yakasance ‘Dan Uwan Mu’awuya Ne najini, Sai Shima Mu’awuya Yace Bazai Yi Mubaya’a ga Aliyyu ba Harsai Ya Zartar Da Hukuncin ga Wadanda Suka Kashe Usman. Kasancewar Mu’awuya Shima Gofnane Agarin Basra A’kasar Sham Siriya Watau Iraqi Ayanzu.
ALLAHU Akbar Yau ga Ranar Manzan ALLAH ﷺ Ina Ma Ace yana Cikin Duniyar!!! Wallahi Nasan Wannan Ba Komai Bane Agunsa ﷺ Cikin Sakanni Zaiyi Maganin Matsalar ﷺ.
Daganan fa Sai Labari Ya Riski ‘Dalha Bn Ubaidullah, Cewa Akwai Matsala A Can Basra Inda Mu’awuya (R. A) Yake Mulki, Domin Mu’awuya (R. A) Shi da Mutanen sa Sunce Bazasuyi Mubaya’ah ba ga Aliyu.
Sannan Madina Tayi Zafi, Rikici Yayi Yawa, Aliyyu Kuma Yakoma (Kufa) Can Ta Yankin Da Mu’awuya Yake Mulki, Domin Mutanen Kufa Sunce Da Aliyyu Yazo Yankinsu Su Sun Aminta dashi, Kuma Sunada Babbar Daula Danhaka Yabar Madina Domin MadinaRikici Yayi Yawa, Yazo Gurinsu, Zasu Bashi Cikakken Goyon Baya Yakafa Daular Musulunci Awannan Yankin, Ya zamo Itace Cibiyar Musulunci Wanda Shugaban Musulmi Yake Cikinta Amaimakon Madina ta Asali Afarko.
Sannan Yacigaba Da Dukkan Wata Qudiri dakuma Aikin Shugabancinsa Zasu Dafa Masa Har abinciko Wadanda Suke Kokarin Rushe Daular.
‘Dalha Bn Ubaidullah da Zubairu Bn Awwam Manyane Daga Cikin Manyan Zaratan Sojojin Manzan ALLAH ﷺ Suma Suka Koma Makka Sai Suka Hadu Da Nana Aisha.
Domin Suma kansu Yayi Zafi Tunaninsu Ya Bambanta dana Sayyadina Aliyu (R. A) Cewar Suna Ganin Yakamata Sayyadina Aliyu yafara Kama Wadanda Sukayi Wannan Mummunar Aiki, Domin Yaji Dadin Mulkinsa Dakuma Magance Matsalar Munafukai dasuke i’kirarin Cewa Harda Hadin Bakinsa Aka Kashe Sayyadina Usman (R. A)
Bayan Sayyadina Aliyu Yakoma Kufa Kuma Ita Kufa Wata Babban Jihace Akasar Iraqi Wanda Har ayanzu Tana Cikin Manyan Daulolin Kasar, Ananma Sai Sayyadina Mu’awuya Yace Bazai Ta’ba Yarda da Khalifancin Sayyadina Aliyu (R. A) Ba Harsai ya Binciko Wadanda Suka Kashshi.
Akan hakan Kuwa Yasa Shi Mu’awuya Yakiyimasa Mubaya’a Domin Sa’banin Ra’ayin dake Tsakanin Su, Sannan Haryakai ga ‘Dalha Bn Ubaidullah Da Azzubair Bn Awwam Suka Taso Daga Makka da Nufin Cewa, Dole Ne Sai Sun Shiga Cikin Matsalarnan Tahanyar: Yin Sulhu Tsakanin Mu’awuya da Sayyadina Aliyu (R. A) Kafin Asamu Maslaha.
Bayan Sun sami Matsaya Danganeda Shawarwarinsu Saikuwa Suka Shirya Domin Zuwa Sulhu Kasar Iraqi Aisha Ma Tace Hankalinta Bazai Kwanta ba Ga Ahalin Gidan Annabi Muhammad ﷺ Cikin Wani Hali Danhaka Sai Yabisu, Sai Kuwa Suka Sauka A Basra Inda Mu’awuya Yake Mulki, Domin Neman Sa daya Janye Akan Yayi Mubaya’a Wa Sayyadina Aliyu, Awannan Lokaci Ne Munafukai Suka So Rura Wutar Gaba Tsakanin ‘Dalha, Aisha, da Zubair (R. A) Da Gulman Cewa Su AISHATU DA ‘DALHA DA ZUBAIR sunje Gun Mu’awuya Ne Domin Suna Goyon Bayan Mu’awuya.
Shikuwa Sayyadina Aliyu Ai Ba Wawa bane Rainon Manzan ALLAH ﷺ Ba Wasa Bane, Yafi Karfin Zugon Munafukai Kuma Ashe Yagane Akwai Munafukai Masu Rura Wutar Rigima, Saiya Aiki wani Daga Cikin Manyan Zaratan Kwamanadan Sojojin Manzan ALLAH ﷺ Qa’aqa’a Bn Attamimi.
Domin Ya Binciko Masa Menene ake ciki Domin Kada Ya Yanke Hukuncin ABisa Rashin Sanin Hakikanin Abinda yake Gaskiya, Sai Kuwa Yazomasa Da Labarin Cewar Ai Sunzo Yin Sulhu Ne.
Sai Sayyadina Aliyu Yace Aikuwa Baici tazama ba Dolene Yajema Kawai Caan Ayi Sulhun (Yaje Basra) Ayi Acan Domin Ga Manyan Mutanen dayake Jin Nauyin su Acan Basra. Agefe Guda Kuwa Wadannan Mutane Masu Mummunar Manufar Sunanan Suna ta Kullace_Kullacensu.
Lokacin da Suka Sami Labarin Cewa Sayyadina Aliyu Yatafi Zaije Sulhu Da Mu’awuya Kuwa: Sai Suka Fara Tunanin Yadda Zasu Wargaza Wannan Sulhun Yazamo Ba’ayi Shiba. Domin Sun Tabbatar dacewar Anayin Sulhu Kan Al’umar Musulmi Zai Hadu Kuma Za’akamosu Ahukuntasu. Shine Suka Rabu Gida Biyu, D’aya Sukaje Basra.
Bayan Sayyadina Aliyyu Yakama Hanya Tareda Rundunarsa Wadanda Sukace Bazasu Bari Yatafi Shidayaba Dole Sai sunbishi Domin kare Ransa da Lafiyarsa. Hakan Kuwa sukayi Suna tafiyane Sai Dare Yayi Musu Ahanya Sai Kuwa Ya Yada Zango Da Rudunar Mutane Dubu Ashirin A wani Guri domin Dare Yayi Dan Su Huta Sai Safiya Acigaba da Tafiya. Cikin Dare Sai Wadannan Munafukai Wadanda suka Kasu Gida Biyu: Domin Cimma Mummunar Manufarsu ta Wargaza Sulhu, Wani Bangaren Suka Zo wa Rundunar Sayyadina Aliyyu Suna Kashesu Suna Saransu Wasu Bangare kuwa Suka Je Ga Sayyadina Mu’awuya AKasarsa Suna Kashe Sojojin said Suna Cewa Ba Maganar Sulhu. Nanma Gun Rindinar Sayyadina Aliyu Suka Kama Saran Sojojin Sa Suna Cewa Babu Sulhu, Daganan Kuma Suka Hade Guri Guda Aka Kama Yaki Musulmi da Musulmi, Ana Kisan Juna ba tareda Ansan Dalilin Yin hakan ba Kowa Na Saran Dan Uwansa Amma Baisan Daliliba Sudai Sunsan Cewa Hari Aka Kawowa Kowanne daga cikin su.
Nagartattun Cikinsu Wasuma Basusaniba Wasu kuwa Sunki shiga Yakin Haka kuma Wadanda Suka shiga ma Sunayine Domin Kare Kansu Domin Su aganinsu Kamar Ankawo Musu Harine.
Awannan Rikicinne aka Kashe Zubair da Dalha Sannan Wasu daga Cikin Sojojin Aliyyu Sune Suka Kashesu Domin Rashin Sanin Hakikanin Me Yakawosu, Yankin Mu’awuya Aganinsu Sune Suka Ruruta Wutar Rigimar, Wani Daga Cikin Sojojin Aliyu Yasamu Azzubair Ibnl Awwam Yana bacci Yadauki Takobinshi Yakasheshi da Ita, Sannan Kuma Ya dauki Takobin Yakaiwa Sayyadina Aliyyu Domin Nuna Bajintarsa Ga Sayyadina Aliyyu,
Da Sayyadina Aliyyu Yaga Wannan Takobi Sannan Wannan Mutumi Yace Dashi Wannan Takobin Dan Awwam ne Da ita Na Kasheshi Dan Sune Suka ruruta Wutar Rigimarnan, Sai Sayyadina Aliyyu Ya Fashe da Kuka Yana Cewa Shin Kasan Hidimar da Wannan Takobi Tayi wa musulunci kuwa?
Da Wannan Takobine Akayi Gadin Manzan Allah ﷺLokacin da akayi Yakin Khandaq, Annabi ﷺ Baya Samun Bacci Azzubair Shike Gadin Annabi ﷺ Haryasamu Yin Bacci. Manzan ALLAH ﷺ Yakira Azzubair da Hawariyyinsa, Domin Yace dukkan Annabi Yanada hawariyawa Nikuwa hawariyina Shine azzubair.
Sannan Shima Dalha Ibn Ubauidullah Shima Awannan Yakinne aka kasheshi tahanyar Harbin Kibiya Da akayi masa, Sayyadina Aliyyu (R. A) Yafada wa Sayyadina Hassan (R. A) Yace dashi ”Lokacin da ‘Dalha Yazo Cikawa Yace Dani, Abin Baiyi Masa Dad’iba Domin Sunzo Sulhu Maimakon Sulhu Kuma Sai Ankama Kashe Juna.
Sayyadina Aliyyu Yana yaki yana kuka Yana Fadin wai Meyafarune!!!.
Bayan Anyi Wannan Yaqinne Sai Sayyadina Aliyyu yace: ”Zamu koma Kufa Domin Abin Baimana Dadin Ji da Ganiba” Aisha Kuwa Da taji Abinda Yafaru hankalinta yatashi Sai Tace Zata Koma Gida, sai Aka Sanya Wasu Rudina Karkashin Jagorancin Mu’awuya (R. A) Sukayi Rakiyarta Gamida Wasu Guziri.
Munafukai kuwa dasukaji haka Har Wani Yafara cewa Aidama Ance Kaza_kaza akanta, Da Sayyadina Aliyyu yaji Haka Saiyasa aka kama wannan Mutumin aka tubeshi akayimasa bulalan ‘Kazafi Na Haddi, Sannan Yace Dashi Wannan itace matar Annabi ﷺ Aduniya kuma Qiyama.
Dagananne Aka Samu Bangarorinnan Na ‘Yan Tawaye Ahlul Bagyi ‘Bangaren Su (Mu’awuya), Dakuma ‘Bangaren Masu Gofnati Su (Sayyadina Aliyyu), Da Munafukai Masu Fad’a Da Dukkan Tsarin Sune (Khawarij), wadanda Dama Annabi Yafadesu Cewa Akwai Wasu Bangarori Biyu Masu Gaskiya Zasu Yaki Juna, Sannan Wasu kuma Zasu Balle Sukuma dabam, Sunzamo Uku Kuma Duk yayi bayaninsu wanda Duk maihangen Nesa Cikin Sahabbai Yaganosu, Kuma Sune matsalar musulmi, Daman Annabi ﷺ yafada Insun Bayyana Akashesu Kada Abarsu Domin Sudin fitinace Ga Alumar Musulmi, Wadda kuma Aliyyu Ya Aiwatar da Wannan Aikin Na Yakarsu kamar Yadda Annabi ﷺ Yabada wasici, Cewar AYakansu Akwai Lada Mai Dumbin Yawa Daga Bakin Annabin ALLAH ﷺ Sannan Yace Idan Za Ayakesu Ayimusu Kisan Kiyashi (Ankashe Su Dukka) Danhaka Sayyadina Aliyu (R. A) Ya yakesu kuma Yakashe Kasho Casa’in Da Biyar Cikin Darinsu Saura Kuma Suka gudu.
Sunefa Masu Da’awa Akan cewa Babu Gofnati Babu Hukunci Saina ALLAH, Wanda Har Sayyida Aliyu Ya turamusu Abdullahi Dan Abbas, Domin Yayi Musu Wa’azi, Domin Sunce Aya Suke Nema Ba ruwansu da Shugabancin Wane Ko hukuncin Wane, Sannan Kuma Su Basa bin Wata Gafnati Tsakanin Aliyyu Ko Mu’awuya Ba ruwansu da Kowa.
Anyi Nasarar Wasu Sun Tuba Sun Amince Sun koma Rindinar Gofnati, Tayadda Wasu kuma Suka Tangare Suka Nuna Girman Kai daga Nanne Sayyadina Aliyyu Yaganefa Sune Wadanda Annabi Yake ta bada Misalinnan Fa, Dagananne Sayyadina Aliyyu Ya Daura Damarar Yaki dasu Domin Yagano Su Yakashe mafi Yawansu, Wasu kuma suka Gudu, Wadanda Suka gudu Suka Tsira Sune Sukayita Yakin Sunkuru Ga Musulmai, Snayimusu Dauki ‘Daid’ai Haryakaiga Sun Kashe Sayyadina Aliyu (R. A) Da Asuba Yafito Yana Tashin Mutane Su Fito Domin Suyi Sallahr Asubahi, Wanda Yakashe Shi Shine Abdullahi Bn Muljum Domin Suna Ganin Su Sayyidina Aliyyu sun kafirta Saikuma yakama Da’awar Cewa In ankasheshi Yayi Shahada.
Wannan Shine Matsalar Da Musulmi Suka taba Samu Gameda Shugabanci Kuma Shine Dalilin Shahadar Sayyadina Aliyyu Dakuma Dalha Da Zubair Rahmatullahi Alaihim Ajmain.
Kuma Siffar Khawarijawa Kenan: Tawaye wa Aqidar Mutane da Gofnati Da Daukan Makami Akan Al’umar Musulmi.

WAHABIYANCI DABAN DA MU’UTAZILANCI
WAHABIYANCI:
Shine Takaituwa Akan Tafarkin Sunnah, Da Bin Nassin Alqur’ani Da Hadisan Manzon ALLAH (ﷺ). Abisa Koyarwar Magabata Na kwarai, Da Kuma Nema Musu Gafara, Tareda Ayyadar da Hukuncin Tsarkake Zuciya Daga Hawan Nafsu (Bin Son Zuciya).
Mu Bama Kushe Dariqar Kowa, Inhar Basu Ta’ba Nassi Ba.
Kada Kabari Son Rai Yasa Kayi Abinda Zai Kaucewa Shari’ah, Abisa Furucine Ko aikin Ibada! Inkayi Haka Kazamo Mu’utazilah,
SAHABBAI SUNE MANYAN WALIYYAN ALLAH
Musulmin Kwarai Baya Gaba Da Waliyyai Kuma Waliyyai: Sune Mabubbugan Sanin Asiran Ulumu Nakara Fad’a Muku, Idan Sahabi Yayi Maka Sharhi! Saikaji kamar Kana Gurin Akayi Zancen, Kaji Waliyyin Gaskiya, Kuma Sahabbai Sun Tsarkaka daga Bin Son Zuciya, Da kuma Ikirarin ‘Kir’kira (Basayin Bid’a), Ko Shigoda Son Zuciyarsu Cikin Addinin Allah.
Subhanallah
Kaji Auliya’ULLAHI Masana Tasarrufin Harshen Masoyina Annabi ﷺ. Daku Muke Taqama Mu Kore Dukkan Wata ‘Barna Da Son Zuciyarmu, Mu Dasa Wa Zu’katanmu Koyi Da Shariar Manzon Allah ﷺ.
GA SIFFAR WALIYYAI AHADISI
عن أبي هريرة رضي الله عنه قال: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم: إن الله تعالى قال: من عادى لي ولياً فقد آذنته بالحرب، وما تقرب إلى عبدي بشئ أحب إلي مما افترضته عليه، ولا يزال عبدي يتقرب إلي بالنوافل حتى أحبه، فإذا أحببته كنت سمعه الذي يسمع به وبصره الذي يبصر به ويده التي يبطش بها ورجله التي يمشي بها، ولئن سألني لأعطينه، ولئن استعاذني لأعيذنه» . رواه البخاري.
An karbo daga Abu Hurairata Allah yakaramasa yarda, ya ce: Manzon Allah s.a.w ya ce: hakika Allah Madaukakin Sarki ya ce: Wanda ya yi gaba da masoyina (Waliyyi), to Ha’ki’ka na yi masa Shelan yaki da ni. Kuma bawana bai gushe ba yana neman kusanci a gare ni, da nafilfilu, Har sai na So shi. Idan kuwa na So shi, To Sai na kasance ni ne jinsa da yake ji da shi, da ganinsa da yake gani da shi, da kuma hannunsa da yake jim’ka (taba wani abu) dashi, da kuma kafafuwansa da yake tafiya dasu. Kuma wallahi idan ya rokeni, wallahi sai na bashi, kuma wallahi idan ya nemi tsarina, wallahi sai na tsareshi”. [Buhari ne ya rawaito shi]
‘KARIN HASKE
Kunga Kenan Waliyyi Shine wanda Yatsare Hukuncin Allah Cikin Ji da Gani, Gamida Sauran Ayyukansa Duk Zaiyi Koyine da Wanda ALLAH ﷻ ya Aminta Dashi. Wanda Yazo A Alqurani Ko Hadisan Manzon Allahﷺ,
‘Dauki Hadisai Kwafin Wahabiyawa Ba Sharrace_Sharracen Shi’awa Ba, Ka Kwashi Romon Ilimomi Afanni Mabambanta.
Yahudawan Dasuke Sa Wasu Suna Karyata Hadisai, Wallahi Suma Anan Su ka Samo Ilimomin Kimiyyar ‘Kira da Dana Yad’a Bayanai. Ya Isheka Misali: Dukkan Manyan Ka’idoji ( Principles Dakuma Law’s Da Theory’s Sanannu ) Na Cikin Ilimin Kimiyya (Science) Duk Zakasamu Na Musulmaine.
Muguntar Yahudu Shine: Mudaina Karanta Hadisai da Ayoyin ALLAH. Suna ‘Kyashin Kada Mun Wuce su Da Sanin Fasaha, Shine Sukeson Mu Kyamaci Littafan Namu, Domin Murasa Madafa.
AMATSAYINKA NA MUSULMI MENENE RIBARKA IDAN KA KUSHE WAHABIYAWA???
Idan Kaji Ana cewa Aikin Banza, Shine Wanda Ke Zagin Ahlussunnah da Wahabiyanci.
Dolenkane Bin Tafarkin Magabatan kwarai Amatsayin ka Na Musulmi , Domin Hanyar Ce Kadai Wacce Zata Sadaka Da Manzan ALLAH ﷺ﴿.
Wahabiyanci Tafarkin Tsira Ne Shine Bin Annabi dama Asahabu Rasulallahi ﷺ.
Domin Sahabbai ALLAH Yakara Musu Yarda: Sune Manyan Waliyyai, Arufai Masana Tarbiyyar Shiriya Ta Abal Qasim Nurun Ala Nurun ﷺ, Muhammadurrasulallah ﷺ.
Idan Kabisu Kabuta, Da ka Kauce Kuwa Ka Halaka.
Zaka Afkane Cikin Qiyayya da Gaba da ABOKANAN Annabin ALLAH ﷺ, Katabbata Cikin Halaka Da Ta’bewa, Ka Koma Yiwa Yahudawa Hidima, Idan Ka ‘Kyamaci Hadisan Annabi ﷺ Kuwa Zaja Girmama Maganganun Yahudu, Mai Cikeda Son Zuciya Da Halakarwa Dakuma Ta’bewa. Yahudu Kullum Kiransu ga Rushe Addinine Tahanyar Amfani da Masu Raunin Addini.
Mudage Mu Kaucewa Manhajinsu, Mu Cire Kamanceceniyar Siffantuwa dasu Cikin ayyukanmu Mai kama Da Tasu, Mu Bi Sunnah Ta Annabi ﷺ.
Itace Hanyar Tsira.
WAHABIYANCI BAIZAMO KHAWARIJANCI BA
INNA LILLAHI WA’ INNA ILAIHI RAJI’UN!!!
TABBAS AQIDANCI BISA JAHILCI ZAIKAI WASUNMU GA HALAKA!!!
Wa’iyazu Billah, Hasbunallahu Wani’imal Wakil.
Dalilin Wannan Ba’asin Nawa Shine: Yadda Naga ko Naji Wasu daga cikin, ‘Yan uwa Musulmi Suna Alaqanta Ahlussunnah da Khawarijawa, Sai Yanzu Nafahimci Dalilin Kisan Malaman Mu da’akeyi haka Kurum. Kuma akayi Shiru Musamman Ja’afar da Albani, Rahmatullahi Alaihim Ajma’in.
Subhanallah Mudai Ahlussunnah, Mun Barranta daga Khawarijanci da Sifofin dama kuke ambatowa, Duk dacewar Bahakan nema Annabi ﷺ Yamisalta ba, Mu Ke da Hadisan Kuma Munsan Sifar! Kuyi Ladabi Asanar daku Sirrikan.
Dan Allah Mudaina Amfani da abinda Ma’kiyan Musulunci ke amfani dashi, Muna Aibanta Junanmu, Domin Hakan Zai Jawo Rabuwar Kan Al’umar Musulmi, Nidai Nasan A Iya Fahimtata ‘Yan Ta’adda Masu Jihadinnan Na Gefen Gari! Damuke dasu Ayanzu Sune Ragowar Khawarij.
Tab ‘Di Jam Babban Magana Kai Mu Ko ‘Yan Shi’ar Najeriya Masu Sukarsu acikinmu Saidai Su Sokesu Dasunan: Ahlul bagyi ‘Yan Tawaye wa Governati Da Shari’ah Amma ba Khawarij ba A Bisa Adalci, Dalilin Kuwa Dayasa Muke Kiran Mafiyawan ‘Dariqu Da Mu’utazilawa Shine: Karbar Shari’a Daga Wasun SAHABBAI (R.A).
Sune ‘SUHUFAYE‘ Wad’anda Kuma Suna Daidai, Suna Kuskure Wasuma Sukan Sanya Ra’ayoyin Su Acikin Addini, Sukuwa SAHABBAI Adalaine, Shari’ar Abal Qasim Itace Shari’ar Su Hukmatan Wa Taufiqan Bi Qaulihi Amalihi ( A Hukumce da Manhaji Bisa Maganganunsa Da Ayyukansa ).
Kuma Akanta Muke ‘Karkashin Jagorancin Sheikh Muhammad Ibn Abdulwahhab, Shiyasa Ake Cewa Damu Wahabiyawa, Amma Shi Ibn Abdulwahhab Ba Shugaba Bane Shidai Mainuni Ne Ga Hanyar Aqidan Bin Sahabbai Dakaucewa Mu’utazilanci, Kuma ‘Mu Bama Zagin SAHABBAI Kuma Bama Kar’bar Shari’ar Da Batazo Daga Annabi ﷺ Ba.
Insha Allahu Agaba Zanyi Rubutu danganeda, Suwaye Khawarij? Da kuma Bambancinsu da Ahlul bagyi. Karkashin Wasu Lectures Na Malam Dr. Mansur Isa Yalwa.
Allah Yayimana Jagorancin.

You must be logged in to post a comment.