HADIN KANMU HANYAR TSIRARMU

💾📱📚

Ismail Hussaini Alpholtawy

  Rayuwa ta ishemu Wa’azi
Malamai kuji tsoron Allah wajen Karantarwa kada kusa Son Zuciya. Domin tsira da mutuncinku aduniya da tsira da imani aran Qiyama

Dalibai muji tsoron Allah, Mufahimci junananmu Yayin Sa’bani, Kada Muce komai Malam  wane yafada Gaskiya ce, Binciken Yafi Sauraron Mu yawa.

Muyi riko da Tsarin Allah Mugirmama junan mu kada Murarraba, Rabuwa A Al’uma fitinace, Yawan jayayya yanasanya Masu Son zuciya yad’a ‘Barna kuma yakan sa Wasu gaba da juna Bisa Rashin Dalili.

Mukula Da amanar junan mu gun jaddada Sa’bani, Muyawaita zantawa da juna domin warware Sa’bani mukula da Wadanda ke son tada fitina a Addini Sud’in wawayene kuma jahilai, danganeda Harkokin Addini Basusan komai ba Sai musu da Cinzarafin Malamai.

Akowace aqeeda akan iya Samun masu mummunar manufa da Kuma Son zuciya. Babbar matsalar rayuwa Shine aiki da Jahilci, dakuma Son Zuciya.

Mu Janye Gaba da juna danganeda bambamcin aqeedah. Meyin hakan Bai fahimci addini ba Son duniya da Son zuciya Shiyake sa Mutum yakasa Barin Mummunar Aqeeda da Mummunar halaye a rayuwa da Addini.

Addinin mu yatanadar mana komai, Bamu Bukatar wata hujja idan Nassi ya inganta. Maluman mu nada da Yanzu Sun mana gata.

daga Matsala ta Kunno kai Sai mubude littafi. Idan muka Zauna Kushe littafan mu da muzantashi. Zamu wayi gari Muna Qauracewa gareshi. Har yazamto mun Halaka kamar Yahudu da Nasara.

Idan Munji gyara Muntabbata gyara ce to yazama wajibi mugyara, Kada Mutsaya Sauraron Ra’ayin Wane ko Matsayar wani Malami, Kowani ‘Dan adam ajizine, Malam Wane Ba Annabi bane Yakan iyayin Kuskure Ko Qarancin Tunani.

Addini dayace Sa’bani Sharri ce kuma fitinace, Hanyar gujemata Shine bincike da Neman Ilimi. Da Gujewa Rudin Duniya dakuma Komawa ga Allah ﷻ.

Idan kai ba malami bane kadaina katsalandan aharkar Fatawa ko Matsayar malamai, Yin hakan Shike janyo d’alibi yaraina Hatta malamin dake karantar dashi.

Malamai Su hada kansu Domin kaucewa yawan Sa’bani, Rashin Zantawa da juna shikesa malamai Sa’bani wani abinma labari kakeji daga ‘Dalibanka wani kuma Baka gama jin Kammalallen saba. Yazama dole Dole muyi Bincike.

Idan kasabawa Maluman dakake tare dasu kadauka kaine akan Kuskure, Ko baka fahimcesuba Kuma kana kyutatamasu zato amma ayimaka gamsasshiyar bayani. Amma idan Kaki kuwait Shaid`an Zai Rinjayeka Ko da akan Gaskiya kake. Domin Kurama takan Cinye Dabbar da ta Ke´bene.

Laifin Wani baya shafan wani agun mu mu ‘Yan adam, Kada Wani wanda ba aqeedarku daya ba yayi magana kayanke hukuncin Dukka aqeedar haka suke. A`a Shidai haka yake amma akwai Wasu nakirki acikinsu.

‘Dalibai Mudunga Girmama maluman mu, Munemi ilimi ba Son shaharaba. Babu amfanin ilimi idan bai zamo hanyar Tsirarmu ranar Lahiraba.

Idan wani yahalaka Sanadinka kana da Kaso cikin Sakamakon da za’a Qaddamar masa.

Idan Hasashen Mutane gaskiyace! Tabbas akwai wadanda ke kar’bo kwangila domin ‘Bata Addini. Amma kuskurene muyi Jam’i, Dole akwai wadanda da gaske suke Kuma Sunada yaqinin Tabbatuwar su akan Gaskiya Suke.

Dole ne Mu martaba Magabatan mu, Idan Munga kuskurensu mu nema masu gafara. Mudaina Tonan Silili ga ‘Yan uwanmu, Idan za’ayi tonon silili wa kowa Babu mai tsira Gaban Allah.

Munbar koyarwar addini, Mundauki Al’adar yahudawa, Amaganganun Mu komai yazo furtawa Muke babu Tantancewa. Muna da Laifi amma hangen na wasu yahanamu neman Afuwar Namu.

Muyo ‘Da’ah Cikin umarnin Annabi nadaga abinda yazo cikin Alqur’ani da Hadisi, Muhanu daga abinda ya tsawatar, Mubautawa Allah cikin Koyarwarsa ﷺ.

Kada mu yarda da Munanan kalaman da ake furtawa ga Sahabbansa رضی الله عنهم ورضو عنه, Hakan zai iya taba darajarsa ﷺ, Mud’auka Cewa Ma’kiya addinine Suke Kokarin raba kawunan mu.

Inmunga Matsala a Alaqarmu ta Aqeeda Muzauna Muwarware mukoma ga Allah musamu mafita. Na tabbata rayuwar mu zata Sauya.

Bissalam Nine naku Ismail Hussaini Alpholtawy

***SA’KON FA’DAKARWA GA AL’UMAR MUSULMI ****

      **lokaci yaquremana** 

     Idan Har a kullum zamu dinga Nisantar Wa’azine dan ana fad’an abinda Yasha Bamban da Ra’ayinmu to Tabbas Zamu Rinqa Nesantar Haske muna Tutsa kanmu cikin Duhun Jahilci, da kafirci,

     Idan Har Sai abinda yayi daidai da Da Ra’ayoyin Mutane Za a Ayyadar aduniya, Tabbas da Wuta ba ayitaba Sai Aljannah inkuwa anyisuma Ko da anzo Duniya babu mai bin Allah.

    Yawancin Mutane Tunatarwa takan Zakke Musu, yayinda Suka tuno da Me zasu tarar a Filin hisabi, Sai imaninsu ga Allah yaqaru, Inkuwa ankoma Shagalin Duniya Kuwa, Allah ma Wasu mantawa suke da Wujudinsa.

   Idan har Zamuce Wai dan Malami yafadi Sabanin Ra’ayin mu, yazamo mutumin banza to Tabbas imani a azuciyar mu zatai wahalar dasuwa. Domin ayyukanmu munana sunfi Yawa, Sukuma Malamai burinsa mu rage.

    Bai zamo dole ace wai Dukkan abinda Zuciya ta natsu dashi yazama Alkhairiba Iyakar Allah shine abinda yahana, koman Jahilcin Dan Adam, daga yashigo Da’irar Allah ta Haramci, na abinda yaqetare iyaka, Yasanta Saidai ya zakkemata domin Son zuciyarsa.

    Kamar Kid’a ma aiya haramta amma muna Saurara kuma yanayi mana dadin ji. Ammafa haramunne. Kuma ma na sanyamu Shagala da Barin Aikin Alkhairi.
   
    Kowani dadi inhar zai hanamu, ko ya nesantamu da jin dadin Lahira Allah kamusanya mana Shi da Mafi alkhairi, Kaine masanin Sirrin asirin Sansanin Sararin Sababin Alkhairan Duniya da Qiyama.

    Mun manta da Yunqurin Shaid’anu akanmu, Muyi nazarin hakan cikin Rayuwa: Sau dadama abinda Allah yahanemu
Zuciyar mu tafison Mu’aikata, Bisa Rud’i da Rinjayar Shed’anun duniya.

      Bai zamo Lallai ba ace; ko Wani abinda Yayi mana dadi Yazama shine halal ba, Tabbas Halal shine abinda yazamo akwai yardar ubangiji acikinsa Babu Shakku bare kokonto.

      Yawan Fad’a da gaskiya yanasa Qeqashewar zuciya, Tabbas idan kaji Gaskiya koda abakin Abokin gabankane, yi kokari ka Kar’beta amatsayinta na Gaskiya, Inkuwa kaqita kuma kana so ka mayar da ita abin ‘kyama, to Tabbas  Zaka Sha Mamakin duniya, Domin Sunan Allah kake yaqa wato Al_Haqqu.

     Ai kuwa dama zaka Qaryata Gaskiyar MA ayarjemaka bisa yadda kake da iko cikin mutane, daga baya Idan gaskiya tabayyana zakasha Kunya, Idan ma Allah yasoka da Shiryuwa ne Saika gyara, inkuwa bakada da rabon haka, Kamutu Ayimaka Hisabi na ‘Batar da Mutane dakuma Aikata Mummunar aiki.

   Dama habaicinnan damuke yawanyi wa juna, da Zagin Juna A Social Media, Amatsayin Sa’banin Ra’ayi ko aqeeda, Da ayoyin Qur’ani muke yad’awa haka da babu ayar da zaka Duba baka Sametaba a Internet. Ko Hadisan Annabi.

     Muyi Tarayya daku wajen yada ilimi na Addinin Musulunci musamu lada sa’bani bazai ta’ba qarewaba A Addini matukar zamu dawwama cikin yiwa juna Raddi da Jahilci. Muyawaita yiwa junar mu NASIHA.

   Wai ko Munmanta da Cewar mu Musulmai ne, Akwai Ranar fa dazata zo Zamuyi Kewar inama adawo damu Duniya Muyi koda Tasbihi guda dayane Mumutu, Dakuwa Munso hakan. Amma babu dama ankulle kofar Nadama da Aiki, Sakamako kawai ake ba Qaqqautawa.

  Kamar Misalin Jarabawar Duniya ce; Sai Ranar raba Result Saikace Ka manta Maths da English baka Baka karasa Amsaba abaka dama kaje ka gyara aikuwa lokaci kam yakure.

    Allah ka Albarkanci Rayuwar mu da ayyukan Nagarta Dakuma zuciya mai imani da dawwama a imani Har mu samu Rabo Aranar Sakamako. Allah kajikan iyayenmu matattu.

    Naraye Allah ka qara Masu Lafiya da imani da Tabbatuwa Akan imanin Har Mu samu rabo na Lahira Mu dasu Muyi Tarayya cikin Samun  kyakkyawan Sakamako anan duniya da Gobe Qiyama.

** KYAWUN FATANA GA AL’UMAR MUSULMI**

    Nayi nazari cikin tsarin Rayuwar Malumanmu na Musulunci, acikin Kyautata zatona danayi Garesu da kyakkyawan Fata sai na hango Maluman mu na Najeriya acikin Da’irar Son Ma’ki da kishin Sahabbansa da Iyalan gidansa

   Inada Lissafin yatiqe dai Munrabene Cikin aqidu Domin Nuna Kishi ahalarar Soyayya
Tayadda ‘Dariqu Suke jaddada So da Girmama waliyyai da Shehunai da Sharifai da Sufaye Domin kasancewarsu Masoya kuma dangi Jinin Fadima Yar Ma’aiki

Sukuwa Ahlussunnah kishinasu ya Ta’allaqane Akan Hidimtawa wa Da’irar Ibada bisa Tafarkin Sunnah da gyara Ibadoji da kiyaye hakkin Annabi da Alqur’ani da Kore Shubuha a Addini

Haka masu jaddada kishin Ahlulbaiti (Ahlul Kusa’i) Suma dai Soyayyace Ragamar su cikin Nuna Hidimtawa wa Sayyada Fadima ‘Yar Ma’ki da Zuri’ar Gidanta Abangaren Sayyadina Ali Allah yakaramasa Yarda

Tabbas gida d’aya Muke karkashin inuwa guda Muke, Matsalar da faruwa acikinmu itace wasunmu na aiki da Jahilci da kuma Son zuciya bisa Siyasar Masu Neman Duniya da gurbata Addini. Masha Allah, Malamai na ya’kar tsarin da salon tsarin Tabbatar da Sunnah gami da kore  Shubuha da qarfafa Shari’ar Musulunci, Muma muzamto wakilan Musulunci kada musanya ido haka kurum muna kallonsu Kamar Telabijin, Ayi muji dadi dan anyi Nasara Akan Ma’kiya Muyi dariya,
    Idan an kore Kazantar wasu To mu abinda yakamata Muyi shine ina datti yake ajikinmu muma Muyi kokari mu wanke, Dan kuwa Malumanmu Tabbas zasu Shud’e kuma Duniya na kara Gur’bata ga kuma Mummunar nufin Yahudawa da Nasara. Muyi Kokarin gyarawa kuma mu ankarar da juna danganeda Zamantakewa da Ibadoji.
  Tabbas Malamai gatarin sarane agaremu kuma tsanin hawane mai qarfi bisa haryar tsira da Digar tono asiran ma’bb’bugar Alkhairai. Inhar mukayi sakaci suka Shud’e bamuda Masu maye Guraben su Tabbas Munyi Kuskure Mafi girma, Ina mukeda yaqinin Tabbatuwa, Yaushe Za’amaimaita Kamarsu Sheikh Ismail Idris da Kuma Ja’afar da Albani.
   Ya za’ayi Duniya tamance da ginshiqannanan namu watau Khulafa’Urrashidun, Ina za’ayi jagorori Kamarsu wadanda burinsu Kullum cigaban Addini. Akwai ire_irensu Wadanda ban ambata ba Ammafa Sun Shud’e Wadanda sukayi hidima ajanibin Ma’aiki da Halarar Tsaftace Al’uma daga Jahilci da Duhun kafirci.
    Saidai kuwa Jimamin mu Kullum Shine; Gamu karkashin inuwar Rumfa guda amma Wasu na Kokarin Jijjige rumfar ga barazanar Abokan Gaban dake tunkaran mu, hakan na faruwane ta silar Wasu wawayen cikin mu da bisa Siyasar Masu Son zuciya da marasa hankalinmu.
  
  ** Mecece mafita?**
   Mafita agaremu Shine komawa ga Allah dakuma hadin kai wajen aikin Alkhairi da ya’da Addini da bawa Addinin kariya takowace ‘Bangare tareda aiki da ilimi wajen da Yad’a ilimin, Malami kuwa Yatsaya amatsayin na Fannin dayasani. Allah ne Masanin komai, Bai aikin Musulmi bane Yanke hukunci da Jahilci ko Son zuciya.
    Wani Tunani dake Zuwa cikin zuciyata Mai cikeda mamaki gamida Amsarta, Itace;

     Anya Kiristoci? Yaya Sukeji ko kallon Al’amuran mu na yawan Sa’bani?
   Kwatsam Saina amsa da cewa, Ai mu Munada yaqinin munakan Gaskiya Saidai binta yayi mana wahala bisa Rinjayar Shed’anu da kuma kasawa ta Dan Adam. Su kuwa kullum wa Duniya kadai Sukewa hidima, Sunbar Addininsu ba tsari Matansu Na fita yawo tsirara ba Mutunci Kamar rayuwar dabbobi, Mukuma Kullum burinmu Ya’kar Irin Wadannan tsarikan mukeyi, Mamakin danake garesu Kullum Shine Rashin Kulawa dasukewa ‘Ya’yansu dasukeyi Shigar banza Kamar Basu da Addini Na Tabbata Addinin Kiristanci bai karantar da hakan ba.

**Godiyar mu ga Allah Musulmi **
Addinin mu yagamamana komai kuma mun riski ilimi da Dukkan wata falalar rayuwa da Tsarin Zamantakewa da ingantacciyar Rayuwa da tarbiyya dukkan mai akasin Kyawun hali da dabi’u tabbas yakauce ne wa koyarwar addini.

**Kira ga Dalibai matasa**

          Yan uwana Matasa Dalibai!!! Murabu da malamai Abangaren wa’azantarwarsu Muzauna amajalisi akoyar damu Ibadoji da Tsaftace Rayuwa gamida tarihohin Shiryarwa Mugujewa Shagalar Rayuwa da rudin Duniya Munemi halali kurum akasuwancinmu.
    Mukuma tayasu wajen Yad’a karatuttuka a Social Media tahanyar Recording and Sharing Audio da Video da Pictures quotes gamida Rubuce Nasihohi da Wallafa manhajoji da Websites  da Rubuta Text wa ‘Yan uwa da abokan Arziqi. Domin sanya ilimin Addini cikin duniyar Network da yaqar Shubuhar mutane da wautarsu na Zagin Malamai da Hauka.
    Sannan hakan zaisanya Mu tanadar babban Guziri wa Yan baya, Domin kada Su iske bamu bar musu kyakkyawan koyiba Sai tarin Shubuha gamida Sa’bani, hakan zaisa Masu raunin imani acikinsu Kokonta cikin imani dama Shakku a Addini matukar Basu tarar da abinda zai Qarfafesu na matsaya gudaba Abin koyi. Ya Allah Kaqaramana imani da Ikhlasi da Tabbatuwa Akan imanin Harmu sameka muna Sallamawa gareka Allah karabamu Da Riya da Son zuciya.
  Allah kajikan Magabatan mu Mukuwa Allah kabamu Shahada.

AHLUSSUNNAH MUFARKA

DA’ACE KISHIN QUNGIYANCIN MU NA ADDINI NE DA MUN WUCE HAKA ACIGABA

      Ahlussunnah Mufarka
Jiya kotu a Kaduna ta wanke Amirul Jaish na rundinar shi’ah (IMN) Ibrahim Yakubu Zakzaky daga tuhumar da Gwamnatin jihar Kaduna ta masa, biyo bayan abinda ya faru a Gazwatu Hussainiyyah Zaria da sojojin janar Buratai a 2015
Ni abinda na fahimta lokacin da Gwamnati ta gindaya masa ne kawai yayi ta sakeshi da kuma tasirin da Zakzaky yake dashi a cikin wannan Gwamnatin, amma ba wai don ta rasa hujjar da zata cigaba da tsareshi ba
Sannan bayan matakin da kotun Kaduna ta zartar, har ila yau inda ace Gwamnatin Kaduna tana da niyyar cigaba da garkame Zakzaky da tayi hakan ta hanyar daukaka kara a kotun tarayya dake Abuja, kamar yadda dokar kasa ta tanadar
Zakzaky yana da manyan mutane a Kasarnan wanda suna da tasirin da zasu iya nema masa alfarma har a gurin shugaban Kasa, idan baku sani ba Zakzaky yana da Manyan Ministoci har guda biyu a cikin wannan Gwamnatin wanda a baya har muzahara suna fita kafin a kafa Gwamnatin Buhari a 2015
Gareka Musulmi Ahlussunnah, ka sani cewa ba ruwan Gwamnatin Nigeria bane ta yaki wani mutum saboda yana dauke da akidar da ta saba da ra’ayinta, shi tsarin kundin Constitution da yake rike da tsarin gudanarwan Kasa, fada ma yake da kowace irin akida ta Musulunci
Duk abinda ya faru da Zakzaky bai da nasaba da addini ko akida, zallar siyasa ce kawai, zargi ne marar tushe da ake cewa Kasar Saudiyyah cibiyar Ahlussunnah tana da hannu a abinda ya faru da Zakzaky
Jama’ar Musulmi da muke kiyayya da shi’ah ku sani cewa akwai babban kalubale a garemu idan bamu gyara, yawan da muke dashi ba zai taba amfanar mu ba, Ya ku Ahlussunnah me zai hana kuyi irin tsarin da Zakzaky yayi har ya samu karfi da kuma tasiri da ya mallaki manyan wakilai da yake dashi a kowace ma’aikata a Gwamnatin Nigeria?
Shin Ahlussunnah kuna da tsarin da kuke daukar nauyin karatun matasa masu fikra da basira a cikinku suna zuwa Kasashen turai suna karanta Medical Doctor, Pilot, Nuclear Physics, Astronomy, Mechanical Engineering, International Law, Computer Science, Ethical Hacking, Cyber Security da sauran fannonin ilmi masu tasiri a zamani kamar yadda Zakzaky yake yi?
Shin Ahlussunnah kuna da tsarin bangare a cikin da’awar Sunnah ko kungiyar Sunnah da yake da bangare na Likitoci Ahlussunnah, bangare na Malaman makarantar boko tun daga Primary har University, bangare na jami’an tsaro, bangare na siyasa, bangare na ‘yan kasuwa, bangare na ma’aikatan Gwamnatin tarayya da na jihohi da kananan hukumomi kamar yadda Zakzaky yake da wannan tsarin?
Ahlussunnah ba mu da wannan tsarin ko guda daya, an bar Ahlussunnah a baya, an bar Ahlussunnah da yiwa juna raddi da hassada, abinda ba za’a taba samu ba kenan a cikin da’awar shi’ah a Nigeria, idan kunga bangaren RAAF suna sukar IMN Taqiyyah ne, manufarsu daya ce
Tsarin da Zakzaky yayi ba shakka idan Allah Ya bashi tsawon rai sai ya kafa Gwamnatin shi’ah a Nigeria, domin Billahi yayi kafuwar da ya wuce tunanin duk wani mai nisan tunani, na rantse da Allah inda ace da’awar shi’ah abune mai kyau da na jima da zama ‘dan shi’ah, kuma da yanzu bana Kasarnan saboda girman gudunmawa da zan bayar a tafiyar, amma shi’ah ba abune mai kyau ba
Namu jagororin sun zama ‘yan duniya, sun fara nesanta kansu da da’awar Sunnah, tsarinsu ya koma irin na ‘yan duniya kawai, sun koma karya da yaudara da zakin baki, takaicin wannan abin yana matukar sanya ni kuka da zubar da hawaye
Halin da Musulmi Ahlussunnah muke ciki a yau ya kamata ya dinga hanamu bacci, ya zamto muna tunanin hanyar da zamu bi mu gyara kuskure domin mu tunkari abokan gaban mu
Yaa Allah Ka bamu mafita na alheri Amin Yaa Hayyu Yaa Qayyum
Daga Malam Datti Assalafiy

GWARGWADON IMANINKA GA ALLAH.



“Shi imani ga bawa yana tsufa kuma yana sabunta, yana raguwa kuma yana ƙaruwa”

“Yana tsufa ko raguwa da yawan saɓon Allah, sannan kuma yana sabunta ko ƙaruwa da biyayya ga Allah

“A lokacin da Allah ta’ala yaso nufarka da alkhairi, sai ya jarabceka a rayuwarka sannan kuma ya baka damar cin wannan jarabawar don ya sauƙaƙa maka hanyar shiga aljannah”

“Gwargwadon imaninka ga Allah gwargwadon jarrabawarsa gareka, bawa baya zama mai cikakken imani ga Allah har sai sanda ya haƙurtar da kansa abisa jarabawowin da Allah buwayi yake jarabtarsa dasu a rayuwarsa ya kuma jure bai gaza cin wannan jarabawar ba, lallai kada mu manta! Tabbas dukkanin girman wata jarabawa, tana tareda girman kyakkyawan sakamako a gurin Allah, ya Allah ka jarabcemu daidai imanin mu”

RAYUWAR MATASHI

YAN UWANA MATASA!!! MU KOMA GA ALLAH

Mu kula da Rayuwa Zata Kai Tabaro mu

  Rayuwar Matashi abin tausayine, Kana fama da Quruciya Ga kuma bakin Aluma akanka. Idan zaafadi Damuwar Aluma dubu, Kaso ´Dari Tara da Hamsin (950) Na Matasa ne.
Qalubale Garemu Matasa, Ban cire kainaba domin nima cikin Quruciya nake.
Tabbas Muna Fuskantar Qalubalen rayuwa daga ´Bangaren zamantakewa, Har da Ibada. Saidai Raunin zuciya kuwa ya danganta da Yadda mutum yataso, Wahala ko Qunci, Tarbiyya ko Akasin hakan (Garari), Riskar iyaye da Rai ko Tashin Maraici. Idan Kasamu yin Makaranta Fani’ima (Haka akeso) In MA bakasamu ba Kaidai kada Kabar Neman ilimin Addini Domin Shidin Yalwatacce NE. Ako Ina akwaishi Amma kayi Takatsan_tsan Maluman da Kake Saurara. KADA kabi Maison Zuciya.
Dukkan Wadannan Matsololin Rayuwa ce, Kirata Agaremu Shine, Mugane inane hanyar tsira kuma mecece mafita ta rayuwar mu, Ina Muka fito, Ina Zamuje, Me zamu Riska, Ina Tafiyar zata Tiqe?


MATASA BAYIN ALLAH NE✍️👇


Kada Mushagaltu da Rudin Rayuwar duniya, Ko kuma Yanayin juyin Rayuwa yasanya Mu ´Bata Rayuwar mu da Shaye_shaye, ko Taaddanci, ko Daba, Da zamaYan Iskan gari.
Mugyara Rayuwarmu tahanyar kaucewa hadarurrukan da Suka shafi aikata Munanan Laifuka, Mutuna Cewa Allah yake bada arziki, kuma Shike bada lokaci dakuma damar Amfanar Arzikin namu. Zamu iya tarawa ahanyar 'Barna (Haram) Amma mu mutu, bamu ciba kuma Hisabinta Nanan Akan mu. Zamu iya shiga Matsalar Rayuwa, Mugur´bata Rayuwar mu da Shaye_shaye ko garari Sanadiyyar wani, ko wata Mattsala, Mun manta cewa ga Allah za a koma kuma akwai hisabi, Shifa Allah ako ina Mukayi kuka Yana jinmu. Idan Ka Shiga Mummunar Hali Mu tuna da ALLAH. Sannan Mu dunga Yawan Ambaton Allah din kada Muce zamu Sha kwaya, ko Mu Kunna Sigari, Yi Hakan kamar An watsa maka Kashine ka Wanke da Kwata. ‘Barna bata Kawar da ‘Barna.
Mu waita yin Istigfari, Wata Qila Jarrabawace ta Yawan zunubin mu, Allah yakeso ya kankare mana. Allah ya yafe mana Yakuma ´Dauramu akan Shiriyar Addininsa, Yakuma Tseratar damu daga Tabewa da Halaka, Allah ka Albarkanci Iyayenmu, da Malumanmu, da Yayunmu, da Kannen mu, Damu kanmu, Wadanda Suka Rasu a Gafartamasu Musamman Mahaifina Allah kajikansa Da Rahama.
Sakon Barka da SALLAR ADHHA ( Eidin Layya) Kutayani Yad’a wannan Sa’kon.
daga ✍️Alqalamin Ismail Hussaini Alpholtawy