TARIHIN SHEIKH ISMA’ILA IDRIS BN ZAKARIYYA

TARIHIN SHEIKH ISMA’ILA IDRIS BN ZAKARIYYA !!!
     **Gwagwar mayarsa wajen Kafa Izala da Sunnah***

Sheikh Isma’ila Idris

yatasone cikin al’umar nan tamu ta Nigeria, ayankin Arewa inda awannan lokacin babu wata aqida a Qasarnan bayan Dariqar Tijjaniyya, Qarqashin jagorancin sheikh Ibrahim Inyas Alkaulahy.
     To dake zamani ya Nausa tafiya tayi nisa, Al’uma tasamu kanta cikin yanayi na Cakuda addini da Son zuciya. Ana samun Malamai masu Sanya Son ransu acikin addini suna anfani dasunan Addini Suna isarda Munanan manufofinsu ga Al’uma kalar Bokanci da Sihirin Duba dama wasu Tsubbace_tsubbace su na Son Zuciya da Neman duniya.
    Wanda yaci karo da koyarwar Addinin Musulunci. Dukkan mai irin wad’annan aiki Bai tabayinsu Saiya fita a addinin Musulunci, Yazamo dukkan wanda yayi Sunansa kafiri da Nassin Aya acikin Suratu baqarah. Haqiqah bayan Wannan Akwai wasu littattafai dadama wadanda Maluma suka shigo dashi ake karantasu na Labaran mafarki da Tatsuniyoyi dasunan Adddini, Irin wadannan abubuwa dakuma makamantansu Sune maqasudin Da’awar ta Sheikh Isma’il Idris, abisa fahimtar masu kyautata masa zato.
    Da’akwai wadanda suke ganin cewa kawai yafara da’awar izala ne kawai Don Neman Suna dakuma Zagin Wasu malamai (Shehunnan ‘Dariqu) dakuma Sufaye. Wanda kuma hakan kuskurene domin  Aikin Musulmi shine kyautatawa juna zato. Da Kuma nemawa juna gafara agunda akayi Kuskure danganeda Sa’banin Ra’ayi ko Fahimta.
    Zamu cigaba ta Tarihi.
    Bayan Malam Yabar aikin Soja wanda acikin Aikin nasa na Soja ya fara da’awa akan barin Tsubbu da Daura layu da makamantansu, Malam yasha tsangwama daga makiya dakuma wadanda basu da ilimi wanda basu fahimceshi ba. Ba awannan Lokaci malam yaga cewar Wannan Da’awa tasa bazata cigaba ba Har saida wata Qungiya Wacce zata Tallafa masa Danganeda samun cikar Qudirinsa na Farkadda mutane game da Sunnah Asali.
    Awannan lokacine malam ya Assasa wata Kungiya mai Suna; ”Jama’atu izalatul Bid’ah ” Ma’ana ( Gungiyar dake kawar da Bidi’ah ) Wannan Kungiya Tasa tasamu karbuwa hatta aciki ‘Yan uwa Sojoji na wannan lokaci, Saidai kuma tasamu naqasu Sosai daga Malaman wannan zamanin Musamman wadanda keda Wannan aqidar ta Tsubbace_tsubbace da Duba. Tayadda sukayita yimasa Tuggu da zagon kasa gurin Sun ga sun dakushe wannan aikin Nasa, Tare da Wargaza aikin Nasa tahanyar kirkiran karya akansa hadda cutar dashi domin Su samu Galaba akansa, Amma ahakan Allah ya Tserataddashi daga dukkan tarakunan nasu Allah ya kuma karfafa Wannan Da’awa tasa har ilayau Qugiyar izala tana nan kuma tana cigaba da aikinta wajen karantar da Al’uma bisa koyarwar magabata dakuma Tabbatar da Qur’ani da Hadisi sune tafarkin Tsira ga Bayi.
    Ahakan aka cigaba da kasancewa har takai yaje izuwa ga Malamin sa na Tauhidi Assheikh Abubakar Mahmud Gumi, Domin neman izini da Karin lamani dangane da Da’awar tasa. Awannan lokacine Sheikh Abubakar Mahmud Gumi ya nuna Bashi Cikakkiyar goyon baya gamida Cikatamasa Sunan Gungoyarsa da ” Wa’iqamatissunnah ”  ma’ana ( Dakuma Tsayar da Sunnah ) Wcce tazamo ” Jama’atu izalatul Bid’ah Wa’iqatissunnah ”
    Ma’an ( Qungiyar dake kawar da Bidi’a kuma take Tsayar da Sunnah )
    Domin acewarsa Sheikh Abubakar Mahmud Gumi; Babu Yadda za’ayi akawar da bidi’a abarta haka ba acike Gurbinta da wani abu ba, Shine Yace to sai Acike Gurbinta Da Sunnah.
    Kunga Ashe kenan ita Izala ba Fitina bace Sabanin Yadda wasu daga cikin maluman ma da basu fahimta ba, Kuma bawai Reshen addini bace kamar yadda wasu suke yimata Mummunar fahimta Har ma wasu ke ganin Cewa in baka ciki to baka cika musulmiba, wasu kuma ke Mata ganin Cewa inkan cikinta Musuluncinka da Gyara Haqiqa Dukkan Mai yiwa Wata Aqidah ta Musulunci ganin Wannan Al’amari, Alal hakika ya Jahilci Hakikanin Musulunci,
    Wannan kadan kenan daga Tarihin Sheikh Isma’ila Idris da Gwagwarmayarsa gurin kafa Izala, insha Allah Anan gaba Zan kawo muku Cigaban da iza ta Kawo Wa Musulunci da Kasarmu baki daya. In Allah mai Komai ya kaimu bayan Sallah.
    Nine naku Isma’il Hussaini Adam Alpholtawy
    Kuma Wannan Shine karshen Rubutuna danganeda Shafukan Tarihin na Bana A Hijira sheka ta 1442 Saikuma Allah ya Kaimu Almuharram Shekara ta 1443 Zan cigaba da Wannan Tarihi.
    Mai karatu ga Addu’a ta Katayani da Ameen.
    Ya ALLAH Kajiqan Mahaifina Hussaini Adam Jumba wanda Ya Rasu a irin Wannan wata Mai Alfarma kuma Aranar Idin Adhhaa, Idin Babban Sallah Allah Kajikansa Ka gafarta masa ka kai Harke Qabarinsa, Kabashi Aljannah Madaukakiya.
    Ya ALLAH Mu Zuri’arsa Da muka Rage a bayan Kasa Allah ka azurtamu da Dogora abisa Addininka, Kabamu Shahada irin tasa, kasanyamu Cikin Wadanda kake Yantawa Zuwa Aljannah.
    Ya ALLAH Ka Sitirtamu da Sutura ta Musulunci, Ka azurtamu da Arzikin imani, da Ikhlasi da Tabbatuwa akan imani, Har Mu Mutu muna masu imani Da Miqa wuya gareka Allah.
    Ya ALLAH ka daukaka musulunci da musulmai, ka Qaskantar da Kafirci da Kafirai kadirkake makiyanka makiyan addini Allah kataimaki bayinka Nagari.

AHLUSSUNNAH MUFARKA

DA’ACE KISHIN QUNGIYANCIN MU NA ADDINI NE DA MUN WUCE HAKA ACIGABA

      Ahlussunnah Mufarka
Jiya kotu a Kaduna ta wanke Amirul Jaish na rundinar shi’ah (IMN) Ibrahim Yakubu Zakzaky daga tuhumar da Gwamnatin jihar Kaduna ta masa, biyo bayan abinda ya faru a Gazwatu Hussainiyyah Zaria da sojojin janar Buratai a 2015
Ni abinda na fahimta lokacin da Gwamnati ta gindaya masa ne kawai yayi ta sakeshi da kuma tasirin da Zakzaky yake dashi a cikin wannan Gwamnatin, amma ba wai don ta rasa hujjar da zata cigaba da tsareshi ba
Sannan bayan matakin da kotun Kaduna ta zartar, har ila yau inda ace Gwamnatin Kaduna tana da niyyar cigaba da garkame Zakzaky da tayi hakan ta hanyar daukaka kara a kotun tarayya dake Abuja, kamar yadda dokar kasa ta tanadar
Zakzaky yana da manyan mutane a Kasarnan wanda suna da tasirin da zasu iya nema masa alfarma har a gurin shugaban Kasa, idan baku sani ba Zakzaky yana da Manyan Ministoci har guda biyu a cikin wannan Gwamnatin wanda a baya har muzahara suna fita kafin a kafa Gwamnatin Buhari a 2015
Gareka Musulmi Ahlussunnah, ka sani cewa ba ruwan Gwamnatin Nigeria bane ta yaki wani mutum saboda yana dauke da akidar da ta saba da ra’ayinta, shi tsarin kundin Constitution da yake rike da tsarin gudanarwan Kasa, fada ma yake da kowace irin akida ta Musulunci
Duk abinda ya faru da Zakzaky bai da nasaba da addini ko akida, zallar siyasa ce kawai, zargi ne marar tushe da ake cewa Kasar Saudiyyah cibiyar Ahlussunnah tana da hannu a abinda ya faru da Zakzaky
Jama’ar Musulmi da muke kiyayya da shi’ah ku sani cewa akwai babban kalubale a garemu idan bamu gyara, yawan da muke dashi ba zai taba amfanar mu ba, Ya ku Ahlussunnah me zai hana kuyi irin tsarin da Zakzaky yayi har ya samu karfi da kuma tasiri da ya mallaki manyan wakilai da yake dashi a kowace ma’aikata a Gwamnatin Nigeria?
Shin Ahlussunnah kuna da tsarin da kuke daukar nauyin karatun matasa masu fikra da basira a cikinku suna zuwa Kasashen turai suna karanta Medical Doctor, Pilot, Nuclear Physics, Astronomy, Mechanical Engineering, International Law, Computer Science, Ethical Hacking, Cyber Security da sauran fannonin ilmi masu tasiri a zamani kamar yadda Zakzaky yake yi?
Shin Ahlussunnah kuna da tsarin bangare a cikin da’awar Sunnah ko kungiyar Sunnah da yake da bangare na Likitoci Ahlussunnah, bangare na Malaman makarantar boko tun daga Primary har University, bangare na jami’an tsaro, bangare na siyasa, bangare na ‘yan kasuwa, bangare na ma’aikatan Gwamnatin tarayya da na jihohi da kananan hukumomi kamar yadda Zakzaky yake da wannan tsarin?
Ahlussunnah ba mu da wannan tsarin ko guda daya, an bar Ahlussunnah a baya, an bar Ahlussunnah da yiwa juna raddi da hassada, abinda ba za’a taba samu ba kenan a cikin da’awar shi’ah a Nigeria, idan kunga bangaren RAAF suna sukar IMN Taqiyyah ne, manufarsu daya ce
Tsarin da Zakzaky yayi ba shakka idan Allah Ya bashi tsawon rai sai ya kafa Gwamnatin shi’ah a Nigeria, domin Billahi yayi kafuwar da ya wuce tunanin duk wani mai nisan tunani, na rantse da Allah inda ace da’awar shi’ah abune mai kyau da na jima da zama ‘dan shi’ah, kuma da yanzu bana Kasarnan saboda girman gudunmawa da zan bayar a tafiyar, amma shi’ah ba abune mai kyau ba
Namu jagororin sun zama ‘yan duniya, sun fara nesanta kansu da da’awar Sunnah, tsarinsu ya koma irin na ‘yan duniya kawai, sun koma karya da yaudara da zakin baki, takaicin wannan abin yana matukar sanya ni kuka da zubar da hawaye
Halin da Musulmi Ahlussunnah muke ciki a yau ya kamata ya dinga hanamu bacci, ya zamto muna tunanin hanyar da zamu bi mu gyara kuskure domin mu tunkari abokan gaban mu
Yaa Allah Ka bamu mafita na alheri Amin Yaa Hayyu Yaa Qayyum
Daga Malam Datti Assalafiy

GWARGWADON IMANINKA GA ALLAH.



“Shi imani ga bawa yana tsufa kuma yana sabunta, yana raguwa kuma yana ƙaruwa”

“Yana tsufa ko raguwa da yawan saɓon Allah, sannan kuma yana sabunta ko ƙaruwa da biyayya ga Allah

“A lokacin da Allah ta’ala yaso nufarka da alkhairi, sai ya jarabceka a rayuwarka sannan kuma ya baka damar cin wannan jarabawar don ya sauƙaƙa maka hanyar shiga aljannah”

“Gwargwadon imaninka ga Allah gwargwadon jarrabawarsa gareka, bawa baya zama mai cikakken imani ga Allah har sai sanda ya haƙurtar da kansa abisa jarabawowin da Allah buwayi yake jarabtarsa dasu a rayuwarsa ya kuma jure bai gaza cin wannan jarabawar ba, lallai kada mu manta! Tabbas dukkanin girman wata jarabawa, tana tareda girman kyakkyawan sakamako a gurin Allah, ya Allah ka jarabcemu daidai imanin mu”

RAYUWAR MATASHI

YAN UWANA MATASA!!! MU KOMA GA ALLAH

Mu kula da Rayuwa Zata Kai Tabaro mu

  Rayuwar Matashi abin tausayine, Kana fama da Quruciya Ga kuma bakin Aluma akanka. Idan zaafadi Damuwar Aluma dubu, Kaso ´Dari Tara da Hamsin (950) Na Matasa ne.
Qalubale Garemu Matasa, Ban cire kainaba domin nima cikin Quruciya nake.
Tabbas Muna Fuskantar Qalubalen rayuwa daga ´Bangaren zamantakewa, Har da Ibada. Saidai Raunin zuciya kuwa ya danganta da Yadda mutum yataso, Wahala ko Qunci, Tarbiyya ko Akasin hakan (Garari), Riskar iyaye da Rai ko Tashin Maraici. Idan Kasamu yin Makaranta Fani’ima (Haka akeso) In MA bakasamu ba Kaidai kada Kabar Neman ilimin Addini Domin Shidin Yalwatacce NE. Ako Ina akwaishi Amma kayi Takatsan_tsan Maluman da Kake Saurara. KADA kabi Maison Zuciya.
Dukkan Wadannan Matsololin Rayuwa ce, Kirata Agaremu Shine, Mugane inane hanyar tsira kuma mecece mafita ta rayuwar mu, Ina Muka fito, Ina Zamuje, Me zamu Riska, Ina Tafiyar zata Tiqe?


MATASA BAYIN ALLAH NE✍️👇


Kada Mushagaltu da Rudin Rayuwar duniya, Ko kuma Yanayin juyin Rayuwa yasanya Mu ´Bata Rayuwar mu da Shaye_shaye, ko Taaddanci, ko Daba, Da zamaYan Iskan gari.
Mugyara Rayuwarmu tahanyar kaucewa hadarurrukan da Suka shafi aikata Munanan Laifuka, Mutuna Cewa Allah yake bada arziki, kuma Shike bada lokaci dakuma damar Amfanar Arzikin namu. Zamu iya tarawa ahanyar 'Barna (Haram) Amma mu mutu, bamu ciba kuma Hisabinta Nanan Akan mu. Zamu iya shiga Matsalar Rayuwa, Mugur´bata Rayuwar mu da Shaye_shaye ko garari Sanadiyyar wani, ko wata Mattsala, Mun manta cewa ga Allah za a koma kuma akwai hisabi, Shifa Allah ako ina Mukayi kuka Yana jinmu. Idan Ka Shiga Mummunar Hali Mu tuna da ALLAH. Sannan Mu dunga Yawan Ambaton Allah din kada Muce zamu Sha kwaya, ko Mu Kunna Sigari, Yi Hakan kamar An watsa maka Kashine ka Wanke da Kwata. ‘Barna bata Kawar da ‘Barna.
Mu waita yin Istigfari, Wata Qila Jarrabawace ta Yawan zunubin mu, Allah yakeso ya kankare mana. Allah ya yafe mana Yakuma ´Dauramu akan Shiriyar Addininsa, Yakuma Tseratar damu daga Tabewa da Halaka, Allah ka Albarkanci Iyayenmu, da Malumanmu, da Yayunmu, da Kannen mu, Damu kanmu, Wadanda Suka Rasu a Gafartamasu Musamman Mahaifina Allah kajikansa Da Rahama.
Sakon Barka da SALLAR ADHHA ( Eidin Layya) Kutayani Yad’a wannan Sa’kon.
daga ✍️Alqalamin Ismail Hussaini Alpholtawy