RAYUWAR MATASHI

YAN UWANA MATASA!!! MU KOMA GA ALLAH

Mu kula da Rayuwa Zata Kai Tabaro mu

  Rayuwar Matashi abin tausayine, Kana fama da Quruciya Ga kuma bakin Aluma akanka. Idan zaafadi Damuwar Aluma dubu, Kaso ´Dari Tara da Hamsin (950) Na Matasa ne.
Qalubale Garemu Matasa, Ban cire kainaba domin nima cikin Quruciya nake.
Tabbas Muna Fuskantar Qalubalen rayuwa daga ´Bangaren zamantakewa, Har da Ibada. Saidai Raunin zuciya kuwa ya danganta da Yadda mutum yataso, Wahala ko Qunci, Tarbiyya ko Akasin hakan (Garari), Riskar iyaye da Rai ko Tashin Maraici. Idan Kasamu yin Makaranta Fani’ima (Haka akeso) In MA bakasamu ba Kaidai kada Kabar Neman ilimin Addini Domin Shidin Yalwatacce NE. Ako Ina akwaishi Amma kayi Takatsan_tsan Maluman da Kake Saurara. KADA kabi Maison Zuciya.
Dukkan Wadannan Matsololin Rayuwa ce, Kirata Agaremu Shine, Mugane inane hanyar tsira kuma mecece mafita ta rayuwar mu, Ina Muka fito, Ina Zamuje, Me zamu Riska, Ina Tafiyar zata Tiqe?


MATASA BAYIN ALLAH NE✍️👇


Kada Mushagaltu da Rudin Rayuwar duniya, Ko kuma Yanayin juyin Rayuwa yasanya Mu ´Bata Rayuwar mu da Shaye_shaye, ko Taaddanci, ko Daba, Da zamaYan Iskan gari.
Mugyara Rayuwarmu tahanyar kaucewa hadarurrukan da Suka shafi aikata Munanan Laifuka, Mutuna Cewa Allah yake bada arziki, kuma Shike bada lokaci dakuma damar Amfanar Arzikin namu. Zamu iya tarawa ahanyar 'Barna (Haram) Amma mu mutu, bamu ciba kuma Hisabinta Nanan Akan mu. Zamu iya shiga Matsalar Rayuwa, Mugur´bata Rayuwar mu da Shaye_shaye ko garari Sanadiyyar wani, ko wata Mattsala, Mun manta cewa ga Allah za a koma kuma akwai hisabi, Shifa Allah ako ina Mukayi kuka Yana jinmu. Idan Ka Shiga Mummunar Hali Mu tuna da ALLAH. Sannan Mu dunga Yawan Ambaton Allah din kada Muce zamu Sha kwaya, ko Mu Kunna Sigari, Yi Hakan kamar An watsa maka Kashine ka Wanke da Kwata. ‘Barna bata Kawar da ‘Barna.
Mu waita yin Istigfari, Wata Qila Jarrabawace ta Yawan zunubin mu, Allah yakeso ya kankare mana. Allah ya yafe mana Yakuma ´Dauramu akan Shiriyar Addininsa, Yakuma Tseratar damu daga Tabewa da Halaka, Allah ka Albarkanci Iyayenmu, da Malumanmu, da Yayunmu, da Kannen mu, Damu kanmu, Wadanda Suka Rasu a Gafartamasu Musamman Mahaifina Allah kajikansa Da Rahama.
Sakon Barka da SALLAR ADHHA ( Eidin Layya) Kutayani Yad’a wannan Sa’kon.
daga ✍️Alqalamin Ismail Hussaini Alpholtawy

BIYAYYA GA IYAYE

WAJIBCIN BIYAYYA GA IYAYE        ➖➖➖➖➖➖➖➖➖                 FITOWA TA ‘DAYA

Da Sunan *Allah* Mai *Rahma* Mai *Jinqai* Abinda Ake Nufi da *Biyayya* Shine Kyautatawa Da Aikata Alheri da Kuma Bayar da Kyauta. A Takaice, *Biyayya* Suna ne da ya Kunshi Aikata Dukkan Wani Alheri. Kalmar *Birru* (Biyayya) Suna ne Daga Cikin Sunayen *Allah Madaukaki*, Ubangiji Yana Cewa: *{ﺇِﻧَّﺎ ﻛُﻨَّﺎ ﻣِﻦْ ﻗَﺒْﻞُ ﻧَﺪْﻋُﻮﻩُ ﺇِﻧَّﻪُ ﻫُﻮَ ﺍﻟْﺒَﺮُّ ﺍﻟﺮَّﺣِﻴﻢُ ﴾ ‏[ ﺍﻟﻄﻮﺭ :٢٨ ‏] .}* Ma’ana: *“Lallai Mun Kasance a Baya Muna Kiransa (Bauta Masa) Lallai Shi (Allah) Mai Kyautatawa ne (Ga Bayinsa), Mai Jinqai”.* (Dur: 28). Abinda Ake Nufi da Kyautatawa Iyaye Kuma Shine: Kyautatawa Zuwa Garesu ta Hanyar Zance da Aiki da Kuma Kusanta Zuwa ga *Allah* Madaukaki. *Ubangiji* Yayi Mana Wasici da Yiwa Iyaye Biyayya a Ayoyi Masu Tarin Yawa a Cikin Alqur’ani, Wanda Hakan Kawai Ya Isa Mu Fahimci Girma da Kuma Qimar Iyaye Wadanda Sune Sila ta Zuwan Mu Gidan Duniya. *Allah ﷻ* Yana Cewa: *{ﻭَﺍﻋْﺒُﺪُﻭﺍ ﺍﻟﻠَّﻪَ ﻭَﻟَﺎ ﺗُﺸْﺮِﻛُﻮﺍ ﺑِﻪِ ﺷَﻴْﺌًﺎ ﻭَﺑِﺎﻟْﻮَﺍﻟِﺪَﻳْﻦِ ﺇِﺣْﺴَﺎﻧًﺎ ﴾ ‏[ ﺍﻟﻨﺴﺎﺀ : ٣٦]}* _Ma’ana: *“Ku Bautawa Allah Kada Ku Hadashi da Kowa (A Cikin Bauta), Kuma Iyaye Ku Kyautata Musu”*. (Nisa’i: 36)._ A Cikin Wannan Ayar Mai Albarka, Ubangiji Ya Gwama Kira Zuwa ga Kadaitashi da Bauta da Biyayya ga Iyaye da Kyautatawa Zuwa Garesu. Kuma Sau da Yawa Haka Ubangiji Yake Hada Kansa da Iyaye a Cikin Aya ‘Daya. Kamar Inda Yake Cewa: *{ﺃَﻥِ ﺍﺷْﻜُﺮْ ﻟِﻲ ﻭَﻟِﻮَﺍﻟِﺪَﻳْﻚَ ﺇِﻟَﻲَّ ﺍﻟْﻤَﺼِﻴﺮُ ﴾ ‏[ ﻟﻘﻤﺎﻥ : ١٤]}.* Ma’ana: *“Ka Godemin Sannan Ka Godewa Iyayenka Gareni Makoma Take”*. (Luqman:14). Har Wayau *ﷻ Allah* Yana Cewa: *{ﻭَﻗَﻀَﻰ ﺭَﺑُّﻚَ ﺃَﻟَّﺎ ﺗَﻌْﺒُﺪُﻭﺍ ﺇِﻟَّﺎ ﺇِﻳَّﺎﻩُ ﻭَﺑِﺎﻟْﻮَﺍﻟِﺪَﻳْﻦِ ﺇِﺣْﺴَﺎﻧًﺎ ﺇِﻣَّﺎ ﻳَﺒْﻠُﻐَﻦَّ ﻋِﻨْﺪَﻙَ ﺍﻟْﻜِﺒَﺮَ ﺃَﺣَﺪُﻫُﻤَﺎ ﺃَﻭْ ﻛِﻠَﺎﻫُﻤَﺎ ﻓَﻠَﺎ ﺗَﻘُﻞْ ﻟَﻬُﻤَﺎ ﺃُﻑٍّ ﻭَﻟَﺎ ﺗَﻨْﻬَﺮْﻫُﻤَﺎ ﻭَﻗُﻞْ ﻟَﻬُﻤَﺎ ﻗَﻮْﻟًﺎ ﻛَﺮِﻳﻤًﺎ * ﻭَﺍﺧْﻔِﺾْ ﻟَﻬُﻤَﺎ ﺟَﻨَﺎﺡَ ﺍﻟﺬُّﻝِّ ﻣِﻦَ ﺍﻟﺮَّﺣْﻤَﺔِ ﻭَﻗُﻞْ ﺭَﺏِّ ﺍﺭْﺣَﻤْﻬُﻤَﺎ ﻛَﻤَﺎ ﺭَﺑَّﻴَﺎﻧِﻲ ﺻَﻐِﻴﺮًﺍ *ﺭَﺑُّﻜُﻢْ ﺃَﻋْﻠَﻢُ ﺑِﻤَﺎ ﻓِﻲ ﻧُﻔُﻮﺳِﻜُﻢْ ﺇِﻥْ ﺗَﻜُﻮﻧُﻮﺍ ﺻَﺎﻟِﺤِﻴﻦَ ﻓَﺈِﻧَّﻪُ ﻛَﺎﻥَ ﻟِﻠْﺄَﻭَّﺍﺑِﻴﻦَ ﻏَﻔُﻮﺭًﺍ ﴾ ‏[ ﺍﻹﺳﺮﺍﺀ :٢٣-٢٥}* Ma’ana: *“Ubangijinka ya Hukunta Kada a Bautawa Wani Sai Shi Kadai Kuma Iyaye a Kyautata Musu; Idan ‘Daya Daga Cikinsu Girma Yazo Masa a Wurinka Ko Duka Biyun (Mahaifi da Mahaifiya), Kada Kace Masu Tir, Kuma Kada Kayi Musu tsawa, Ka Fada Musu Zance Mai Girma (Me Dadi)……………..”.* (Isra’i: 23-25). A Wata Aya Kuma *Ubangiji* Yana Cewa: *{ﻭَﻭَﺻَّﻴْﻨَﺎ ﺍﻟْﺈِﻧْﺴَﺎﻥَ ﺑِﻮَﺍﻟِﺪَﻳْﻪِ ﺣُﺴْﻨًﺎ ﴾ ‏[ ﺍﻟﻌﻨﻜﺒﻮﺕ : ٨]}.* Ma’ana: *“Munyi Wasici ga Mutum da Ya Kyautatawa Mahaifansa”.* (Ankabut: 8). *Imam Ibn Kathir (rh)* Yana Cewa: “Ubangiji Ya Umurci Bayinsa da Kyautatawa Mahaifa Bayan Ya Kwadaitar da Kadaitashi da Bauta. Domin Mahaifa Sune Sababin Zuwan Mutum Duniya, Saboda Haka Sune Sukafi Dacewa da a Kyautata Musu. Mahaifi ta Hanyar Ciyar Dashi Ita Kuma Mahaifiya ta Hanyar Tausaya Mata”. *(Tafseer Ibn Kathir: v6/ p238)*. *BIYAYYA GA IYAYE SIFFAR ANNABAWA NE* ➖➖➖➖➖➖➖➖➖➖➖ Hakika *Ubangiji* Madaukaki Ya Siffanta Wasu Daga Cikin Annabawansa da Kasancewarsu Masu Matukar Biyayya ga Iyayensu Inda Yake Cewa a Cikin Littafinsa: *{ﻳَﺎ ﻳَﺤْﻴَﻰ ﺧُﺬِ ﺍﻟْﻜِﺘَﺎﺏَ ﺑِﻘُﻮَّﺓٍ ﻭَﺁﺗَﻴْﻨَﺎﻩُ ﺍﻟْﺤُﻜْﻢَ ﺻَﺒِﻴًّﺎ * ﻭَﺣَﻨَﺎﻧًﺎ ﻣِﻦْ ﻟَﺪُﻧَّﺎ ﻭَﺯَﻛَﺎﺓً ﻭَﻛَﺎﻥَ ﺗَﻘِﻴًّﺎ * ﻭَﺑَﺮًّﺍ ﺑِﻮَﺍﻟِﺪَﻳْﻪِ ﻭَﻟَﻢْ ﻳَﻜُﻦْ ﺟَﺒَّﺎﺭًﺍ ﻋَﺼِﻴًّﺎ * ﻭَﺳَﻠَﺎﻡٌ ﻋَﻠَﻴْﻪِ ﻳَﻮْﻡَ ﻭُﻟِﺪَ ﻭَﻳَﻮْﻡَ ﻳَﻤُﻮﺕُ ﻭَﻳَﻮْﻡَ ﻳُﺒْﻌَﺚُ ﺣَﻴًّﺎ ﴾ ‏[ ﻣﺮﻳﻢ : 12 – 15 ‏]}.* Ma’ana: *“Ya Yahya ka Riqe Littafi da Karfi Mun Bashi Hukunci Yana Karami# Yana Mai Biyayya ga Iyayensa be Kasance Me Girman Kai  me Sa6awa Ubangiji ba# Aminci Ya Tabbata a Gareshi Ranar da Aka Haifeshi, da Ranar da Zai Mutu da Ranar da Za’a Tasheshi Yana rayayye”.* (Maryam: 12-15). Ubangiji* Yana Cewa Game da Annabi *Isah (as): *{ﻗَﺎﻝَ ﺇِﻧِّﻲ ﻋَﺒْﺪُ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺁﺗَﺎﻧِﻲَ ﺍﻟْﻜِﺘَﺎﺏَ ﻭَﺟَﻌَﻠَﻨِﻲ ﻧَﺒِﻴًّﺎ * ﻭَﺟَﻌَﻠَﻨِﻲ ﻣُﺒَﺎﺭَﻛًﺎ ﺃَﻳْﻦَ ﻣَﺎ ﻛُﻨْﺖُ ﻭَﺃَﻭْﺻَﺎﻧِﻲ ﺑِﺎﻟﺼَّﻠَﺎﺓِ ﻭَﺍﻟﺰَّﻛَﺎﺓِ ﻣَﺎ ﺩُﻣْﺖُ ﺣَﻴًّﺎ * ﻭَﺑَﺮًّﺍ ﺑِﻮَﺍﻟِﺪَﺗِﻲ ﻭَﻟَﻢْ ﻳَﺠْﻌَﻠْﻨِﻲ ﺟَﺒَّﺎﺭًﺍ ﺷَﻘِﻴًّﺎ * ﻭَﺍﻟﺴَّﻠَﺎﻡُ ﻋَﻠَﻲَّ ﻳَﻮْﻡَ ﻭُﻟِﺪْﺕُ ﻭَﻳَﻮْﻡَ ﺃَﻣُﻮﺕُ ﻭَﻳَﻮْﻡَ ﺃُﺑْﻌَﺚُ ﺣَﻴًّﺎ * ﺫَﻟِﻚَ ﻋِﻴﺴَﻰ ﺍﺑْﻦُ ﻣَﺮْﻳَﻢَ ﻗَﻮْﻝَ ﺍﻟْﺤَﻖِّ ﺍﻟَّﺬِﻱ ﻓِﻴﻪِ ﻳَﻤْﺘَﺮُﻭﻥَ ﴾ ‏[ ﻣﺮﻳﻢ :٣٠ -٣٤]}* Ma’ana: *“Yace Ni Bawan Allah ne An Bani Littafi Kuma an Sanyani Na Zamo Annabi# Kuma Aka Sanyani Me Albarka a Duk Inda Na Kasance Akayimin Wasici dayin Sallah da Bayar da Zakkah Matukar Ina Raye# Kuma Me Biyayya ga Mahaifiyata be Sanyani Me Taurin Kai Mara Rabo ba# Aminci Ya Tabbata a Gareni Ranar da Aka Haifeni da Ranar da Zan Mutu da Kuma Ranar da Za’a Tasheni Rayayye# Wannan Shine Isah ‘Dan Maryam, Zance Né Na Gaskiya Wanda Suke Musu”* (Maryam: 30-34). Anan Zan Dakata Sai Mun Hadu a Rubuta Na Gaba *سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن الإله إلا أنت أستغفرك وأتوب إليك*   WAJIBCIN BIYAYYA GA IYAYE        ➖➖➖➖➖➖➖➖➖                   FITOWA TA BIYU _Da Sunan *Allah* Mai *Rahma* Mai *Jinqai*_ _*KWADAITARWAR MANZON ALLAH (ﷺ) GAME DA BIYAYYA GA IYAYE*_ _Hakika *Manzon Allah(ﷺ)* Ya Kwadaitar da Wannan Al’ummah Lada da Kuma Falalar Biyayya da Iyaye Hatta Iyayen da Musulmai ba, Sannan Kuma Ya tsoratar game da Sa6a Musu, Kamar Yanda Zamu Gani a Hadisai Masu Zuwa:_ *{ﻋﻦ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﺑﻦ ﻣﺴﻌﻮﺩٍ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ ﻗﺎﻝ : ﺳﺄﻟﺖ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻗﻠﺖ : ﻳﺎ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ، ﺃﻱ ﺍﻟﻌﻤﻞ ﺃﻓﻀﻞ؟ ﻗﺎﻝ : )) ﺍﻟﺼﻼﺓ ﻋﻠﻰ ﻣﻴﻘﺎﺗﻬﺎ (( ،ﻗﻠﺖ : ﺛﻢ ﺃﻱ؟ ﻗﺎﻝ : )) ﺛﻢ ﺑﺮُّ ﺍﻟﻮﺍﻟﺪﻳﻦِ (( ،ﻗﻠﺖ : ﺛﻢ ﺃﻱ؟ ﻗﺎﻝ : )) ﺍﻟﺠﻬﺎﺩ ﻓﻲ ﺳﺒﻴﻞ ﺍﻟﻠﻪ (( ؛ ‏( ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ﺣﺪﻳﺚ ٥٢٧ / ﻣﺴﻠﻢ ﺣﺪﻳﺚ ٨٥)}* _An Kar6o Daga *Abdullahi bn Mas’ud (ra)* Yace: Na Tambayi *Manzon Allah (ﷺ)* Nace: Ya Annabin Allah, Wane Aiki ne Yafi Falala? Sai Yace: *“Sallah Akan Lokacinta”.* Sai Nace Sannan Me? Sai Yace: *“Sannan Biyayya ga Iyaye”*. Sannan Nace Sai Mene? Sai Yace: *“Jihadi don ‘Daukaka Kalmar Allah”*. (Bukhari:257, Muslim:85)._ _Ya Dan Uwa Ka Duba Girman Jihadi don Daukaka Kalmar Allah, Wanda Duk Wanda Ya Mutu a Halin Jihadi Bashi da Sakamakon da ya Gaza Shiga Aljannah, Sannan Ko Hisabi Baza’ayi Musu ba Saboda Falalar Abinda Suka Mutu Akai. Tare da Haka *Manzon Allah (ﷺ)* Ya Gabatar da Biyayya gareshi._ *{ﻋﻦ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﺑﻦ ﻋﻤﺮﻭ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻬﻤﺎ ﻗﺎﻝ : ﺟﺎﺀ ﺭﺟﻞ ﺇﻟﻰ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻓﺎﺳﺘﺄﺫﻧﻪ ﻓﻲ ﺍﻟﺠﻬﺎﺩ،ﻓﻘﺎﻝ : )) ﺃﺣﻲٌّ ﻭﺍﻟﺪﺍﻙ؟ (( ، ﻗﺎﻝ : ﻧﻌﻢ،ﻗﺎﻝ : )) ﻓﻔﻴﻬﻤﺎ ﻓﺠﺎﻫِﺪْ (( ؛ ‏( ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ﺣﺪﻳﺚ ٣٠٠٤ / ﻣﺴﻠﻢ ﺣﺪﻳﺚ ٢٥٤٩)}.* _An Kar6o Daga *Abdullahi bn Amru (ra)* Yace: Wani Mutum Yaje Wurin *Manzon Allah (ﷺ)* Yana Neman Ayi Masa Izinin Fita Jihadi, sai *Manzon Allah (ﷺ)* Yace: *“Shin Iyayenka Suna Raye?”* Sai Mutumin Yace Eh. Sai *Manzon Allah (ﷺ)* Yace: *“Kaje Kayi Jihadinka a Wurinsu”.* (Bukhari: 3004, Muslim: 2549)._ _*Imam Ibn Hajar Al-Asqalany (rh)* Yayi Karin Bayani Game da Wannan Hadisin Inda Yake Cewa: “Jihadi Yana Haramta Matukar Iyaye Basu Amince da Fitar ba, Amma da Sharadin Iyayen su Zamo Musulmai. Domin Yi Musu Biyayya Farillah ce ta Ainihi (Wajibi), Fita Jihadi Kuma Farillah ce ta Kifaya (Mustahabbi)”. *(Fathul Bary: V-6, p163)*_ *{ ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﻫﺮﻳﺮﺓ، ﻗﺎﻝ : ﻗﺎﻝ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ : )) ﻻ ﻳَﺠﺰﻱ ﻭﻟﺪٌ ﻭﺍﻟﺪًﺍ ﺇﻻ ﺃﻥ ﻳﺠﺪَﻩ ﻣﻤﻠﻮﻛًﺎ ﻓﻴﺸﺘﺮﻳَﻪ ﻓﻴُﻌﺘﻘَﻪ (( ؛ ‏( ﻣﺴﻠﻢ – ﺣﺪﻳﺚ ١٥١٠)}* _An Kar6o Daga *Abi-Hurairah (ra)* Yace: *Manzon Allah (ﷺ)* Yace: *“’Da Bazai Iya Sakawa Mahaifinsa ba Sai fa Idan Ya Samu Mahaifin ne a Matsayin Bawa, Sai Ya Siyeshi Sannan Ya ‘Yantashi”*. (Muslim: 1510)._ *{ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﺳﻌﻴﺪٍ ﺍﻟﺨﺪﺭﻱ : ﺃﻥ ﺭﺟﻠًﺎ ﻫﺎﺟﺮ ﺇﻟﻰ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻣِﻦ ﺍﻟﻴﻤﻦ، ﻓﻘﺎﻝ : )) ﻫﻞ ﻟﻚ ﺃﺣﺪ ﺑﺎﻟﻴَﻤﻦ؟ (( ، ﻗﺎﻝ : ﺃﺑﻮﺍﻱ،ﻗﺎﻝ : )) ﺃَﺫِﻧﺎ ﻟﻚ؟ (( ، ﻗﺎﻝ : ﻻ،ﻗﺎﻝ : )) ﺍﺭﺟِﻊْ ﺇﻟﻴﻬﻤﺎ ﻓﺎﺳﺘﺄﺫﻧﻬﻤﺎ، ﻓﺈﻥ ﺃﺫﻧﺎ ﻟﻚ ﻓﺠﺎﻫِﺪْ، ﻭﺇﻻ ﻓﺒَﺮَّﻫﻤﺎ (( ؛ ‏( ﺣﺪﻳﺚ ﺻﺤﻴﺢ ‏) ‏( ﺻﺤﻴﺢ ﺃﺑﻲ ﺩﺍﻭﺩ ﻟﻸﻟﺒﺎﻧﻲ ﺣﺪﻳﺚ ٢٢٠٧)}.* _An Kar6o Daga *Abi-Sa’eedil Khudry (ra)*, Lallai Wani Mutum Yayi Hijirah Daga Yaman Zuwa Wurin *Manzon Allah(ﷺ)* Sai *Manzon Allah(ﷺ)* Yace Dashi: *“Shin Kanada Wani a Yaman?”*. Sai Mutumin Yace: Eh Inada Iyaye na. Sai *Manzon Allah(ﷺ)* Yace: *“Shin Su Sukayi Maka Izini?”* Sai Yace: A’a. Sai *Manzon Allah(ﷺ)* Yace Dashi: *“Ka Koma Zuwa Garesu Ka Nemi Izininsu, Idan Sukayi Maka Izini Sai Kazo Kayi Jihadi. Idan Kuma Sukaqi Amincewa, to Kayi Musu Biyayya”*. (Abi-Daud: 2207)._ _An Kar6o Daga *Jabir bn Abdullah (ra)* Lallai Wani Mutum Yace: Ya *Manzon Allah (ﷺ)* Lallai Inada Dukiya da Yaro, Kuma Mahaifiya Yanason Ya Kwace Dukiyata. Sai *Manzon Allah (ﷺ)* Yace: *“Kai da Dukiyarka Ai Na Mahaifinka ne”.* (Ibn-Majah:1855)._ _*Imamud ‘Dahãwy (rh)* Yana Cewa: “Wani 6angare Na Malamai Suna Cewa: “Duk Abinda Yaro Zai Samu Nashi ne Shi Kadai Banda Mahaifinsa. Zancen da *Manzon Allah (ﷺ)* Yayi ba Yana Nuna Cewa Duk Abinda Yaro ya Mallaka Mallakin Ubansa Bane. Abinda Yake Nufi Shine Baya Kamata Ga Yaro Ya Sa6awa Mahaifinsa Saboda Wani Abu, Wajibine Yayi Masa Biyayya Gwargwadon Iko”. (Sharhu Ma’anil Ãthar Lid ‘Dahãwy: Vol. 4, P. 169)._ _Anan Zan Dakata Sai Mun Hadu a Rubuta Na Gaba_ *سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن الإله إلا أنت أستغفرك وأتوب إليك*  WAJIBCIN BIYAYYA GA IYAYE        ➖➖➖➖➖➖➖➖➖                 FITOWA TA UKU _Da Sunan *Allah* Mai *Rahma* Mai *Jinqai*_ _*ZANTUKAN MAGABATA NA KWARAI*_       _*GAME DA BIYAYYA GA IYAYE*_ _Idan Bamu Manta ba, a Rubutu Mu Daya Gabata Mun Fara Kawo Maganganun Magabata Na Kwarai Game da Yiwa Iyaye Biyayya. A Yau Idan Allah Ya Yarda Zamu Cigaba daga Inda Muka tsaya._ *{ﻗﺎﻝ ﻟﻘﻤﺎﻥ ﺍﻟﺤﻜﻴﻢ ﻻﺑﻨﻪ : ﻳﺎ ﺑﻨﻲ، ﻣَﻦ ﺃﺭﺿﻰ ﻭﺍﻟﺪﻳﻪ ﻓﻘﺪ ﺃﺭﺿﻰ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦَ، ﻭﻣﻦ ﺃﺳﺨَﻄﻬﻤﺎ ﻓﻘﺪ ﺃﺳﺨَﻂ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦَ؛ ‏( ﺑﺮ ﺍﻟﻮﺍﻟﺪﻳﻦ – ﻷﺑﻲ ﺑﻜﺮ ﺍﻟﻄﺮﻃﻮﺷﻲ ﺹ – ٣٧)}* _*Luqman* Yana Cewa ‘Dansa: *“Yakai ‘Dãna! Duk Wanda Ya Yardar da Mahaifansa, Hakika Ya Yardar da Me Rahama. Kuma Duk Wanda Ya Fusatasu, Hakika Ya Fusata Me Rahama”*. (Birrul Walidain Na Abi-Bakar ‘Dardushy: P. 8)._ _Hakika Wannan Zance Na Luqman Yayi Daidai da Zancen *Annabi* Da Yake Cewa: *“Yardan Allah Yana Cikin Yardan Iyaye, Kuma Fushin Ubangiji Yana Cikin Fushin Mahaifa”*. Saboda Haka Idan Kana Bukatar Ubangiji Ya Yarda Dakai, to ka Kyautatawa Mahaifansa Har Su Yarda Dakai. Idan Kuma Kafi Bukatar Fushin Ubangiji da Uqubarsa, to Ka Cigaba da Wulakantasu Lallai Ubangijin Shi Kuma Yana nan a Madaka._ *{ﻗﺎﻝ ﻟﻘﻤﺎﻥ ﻻﺑﻨﻪ : ﻳﺎ ﺑﻨﻲ، ﺇﻥ ﺍﻟﻮﺍﻟﺪﻳﻦِ ﺑﺎﺏٌ ﻣﻦ ﺃﺑﻮﺍﺏ ﺍﻟﺠﻨﺔ، ﺇﻥ ﺭﺿﻴَﺎ ﻋﻨﻚ ﻣﻀﻴﺖَ ﺇﻟﻰ ﺍﻟﺠﻨﺔ، ﻭﺇﻥ ﺳﺨِﻄﺎ ﺣُﺠِﺒﺖ؛ ‏( ﻛﺘﺎﺏ ﺍﻟﺒﺮ ﻭﺍﻟﺼﻠﺔ ﻻﺑﻦ ﺍﻟﺠﻮﺯﻱ – ﺹ – ٨٠)}* _Har Wayau *Luqman* Yana Fadawa ‘Dansa Cewa: *“Lallai Mahaifa Kofa ne Daga Cikin Kofofin Aljannah, Idan Suka Yarda Dakai Zaka Zarce Aljannah. Idan Kuma Sukayi Fushi Dakai, Za’a Shamakanceka Daga Shiga Aljannah”*. (Kitabul Birr Was Sila Na *Ibn Jauzy* p. 80)._ *{ﺭﻭﻯ ﻋﺒﺪﺍﻟﺮﺯﺍﻕ ﻋﻦ ﻃﺎﻭﺱ ﺑﻦ ﻛﻴﺴﺎﻥ ﻗﺎﻝ : ﻣِﻦ ﺍﻟﺴﻨَّﺔ ﺃﻥ ﻳﻮﻗَّﺮَ ﺃﺭﺑﻌﺔ : ﺍﻟﻌﺎﻟﻢ، ﻭﺫﻭ ﺍﻟﺸَّﻴﺒﺔ، ﻭﺍﻟﺴﻠﻄﺎﻥ، ﻭﺍﻟﻮﺍﻟﺪ، ﻗﺎﻝ : ﻭﻳﻘﺎﻝ : ﺇﻥ ﻣِﻦ ﺍﻟﺠﻔﺎﺀ ﺃﻥ ﻳﺪﻋﻮَ ﺍﻟﺮﺟﻞُ ﻭﺍﻟﺪَﻩ ﺑﺎﺳﻤِﻪ؛ ‏( ﻣﺼﻨﻒ ﻋﺒﺪﺍﻟﺮﺯﺍﻕ – ﺝ – ١١ – ﺭقم ٢٠١٣٣)}* _*Abdulrazak* Ya Ruwaito Daga *’Dawus bn Kaisãn* Yace: *“Yana Daga Cikin Sunnah a Girmama Mutane Hudu: Malami, da Mutum Me Furfura, da Shugaba da Kuma Mahaifi”*. Ya Kasance Yana Cewa: “Yana Daga Cikin Jafa’i Mutum Ya Kira Mahaifinsa da Sunansa”. (Musannaf Abdulrazaq: Vol. 11 No. 20133)._ *{ﻟﻤﺎ ﻣﺎﺗﺖ ﺃﻡ ﺇﻳﺎﺱ ﺑﻦ ﻣﻌﺎﻭﻳﺔ ﺑﻜﻰ، ﻗﻴﻞ ﻟﻪ : ﻣﺎ ﻳﺒﻜﻴﻚ؟ ﻗﺎﻝ : ﻛﺎﻥ ﻟﻲ ﺑﺎﺑﺎﻥِ ﻣﻔﺘﻮﺣﺎﻥ ﺇﻟﻰ ﺍﻟﺠﻨﺔ، ﻭﻏُﻠِّﻖ ﺃﺣﺪُﻫﻤﺎ؛ ‏( ﻛﺘﺎﺏ ﺍﻟﺒﺮ ﻭﺍﻟﺼﻠﺔ – ﻻﺑﻦ ﺍﻟﺠﻮﺯﻱ – ﺹ – ٧٢)}* _A Yayin da Mahaifiya *Iyyas bn Mu’awiya* Ta Rasu Yayita yin Kuka. Sai Akace Dashi Menene Yake Sakaka Kuka? Sai Yace: *“Na Kasance Inada Kofofi Guda Biyu Budaddu Zuwa ga Aljannah, A Yau An Kulle Guda ‘Daya”.* (Kitabul Birri Was Silah Na *Ibn Jauzy*: P. 72)._ *{‏ﻗﺎﻝ ﻣﻜﺤﻮﻝ ﺍﻟﺸﺎﻣﻲ : ﺑﺮُّ ﺍﻟﻮﺍﻟﺪﻳﻦ ﻛﻔَّﺎﺭﺓٌ ﻟﻠﻜﺒﺎﺋﺮ؛ ‏( ﺷﺮﺡ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻟﻠﺒﻐﻮﻱ ﺝ – ١٣ ﺹ – ١٣)}* _*Makhul Ash-Shamy* Yana Cewa: *“Biyayya ga Iyaye Yana Kankare Manyan Zunubai”*. (Sharhu Sunnah Na Bagawy: Vol. 13, p. 13)._ *{ﻗﺎﻝ ﺳﻔﻴﺎﻥ ﺑﻦ ﻋﻴﻴﻨﺔ : ﻣَﻦ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﺼﻠﻮﺍﺕِ ﺍﻟﺨﻤﺲَ ﻓﻘﺪ ﺷﻜﺮ ﻟﻠﻪ، ﻭﻣﻦ ﺩﻋﺎ ﻟﻮﺍﻟﺪﻳﻪ ﻋﻘﺒﻬﺎ ﻓﻘﺪ ﺷﻜﺮ ﻟﻬﻤﺎ؛ ‏( ﻓﺘﺢ ﺍﻟﺒﺎﺭﻱ – ﻻﺑﻦ ﺣﺠﺮ ﺍﻟﻌﺴﻘﻼﻧﻲ – ﺝ – ٢ – ﺹ – ١٠)}* _*Sufyãn bn Uyaina* Yana Cewa: *“Duk Wanda ya Sallaci Sallolli Biyar, Hakika Ya Godewa Allah. Wanda Duk Yayiwa Iyayensa Addu’a Bayan Sallolin, Hakika Ya Godewa Iyayensa”*. (Fathul Bary: Vol. 2, P. 10)._ *{ﻗﺎﻝ ﻣﺤﻤﺪ ﺑﻦ ﻣﺤﻴﺮﻳﺰٍ : ﻣَﻦ ﻣﺸﻰ ﺑﻴﻦ ﻳﺪَﻱْ ﺃﺑﻴﻪ ﻓﻘﺪ ﻋﻘَّﻪ، ﺇﻻ ﺃﻥ ﻳﻤﺸﻲ ﻓﻴﻤﻴﻂ ﻟﻪ ﺍﻷﺫﻯ ﻋﻦ ﻃﺮﻳﻘﻪ، ﻭﻣﻦ ﺩﻋﺎ ﺃﺑﺎﻩ ﺑﺎﺳﻤﻪ ﺃﻭ ﺑﻜﻨﻴﺘﻪ ﻓﻘﺪ ﻋﻘَّﻪ، ﺇﻻ ﺃﻥ ﻳﻘﻮﻝ : ﻳﺎ ﺃﺑﺖِ؛ ‏( ﺍﻟﺒﺮ ﻭﺍﻟﺼﻠﺔ – ﻻﺑﻦ ﺍﻟﺠﻮﺯﻱ – ﺹ – ١١٧)}* _*Muhammad bn Muhairiz* Yace: *“Duk Wanda Yake Tafiya a Gaban Mahaifinsa, Hakika Ya Sa6a Masa; Sai fa Idan Ya Shiga Gaban Nasa ne Domin Kauda Abinda Zai Cutar Dashi ne. Kuma Duk WanKumYa Kira Mahaifinsa da Sunansa ko da Alkunyarsa Hakika Ya Sa6a Masa, Sai Dai Idan Zaice Ya Mahaifina”.* (Al-Birri Was Silah Na *Ibn Jauzy*: 117)._ *{ﻗﺎﻝ ﻣﺠﺎﻫﺪُ ﺑﻦ ﺟﺒﺮٍ : ﻻ ﻳﻨﺒﻐﻲ ﻟﻠﻮﻟﺪ ﺃﻥ ﻳﺪﻓﻊ ﻳﺪَ ﻭﺍﻟﺪﻩ ﻋﻨﻪ ﺇﺫﺍ ﺿﺮﺑﻪ، ﻗﺎﻝ : ﻭﻣَﻦ ﺷﺪ ﺍﻟﻨﻈﺮ ﺇﻟﻰ ﻭﺍﻟﺪﻳﻪ ﻓﻠﻢ ﻳَﺒَﺮَّﻫﻤﺎ، ﻭﻣَﻦ ﺃﺩﺧﻞ ﻋﻠﻴﻬﻤﺎ ﺣﺰﻧًﺎ ﻓﻘﺪ ﻋَﻘَّﻬﻤﺎ؛ ‏( ﺍﻟﺒﺮ ﻭﺍﻟﺼﻠﺔ – ﻻﺑﻦ ﺍﻟﺠﻮﺯﻱ – ﺹ – ١١٧)}* _*Mujãhid bn Jubrin* Yana Cewa: *“Baya Dacewa ga Yaro Ya Ture Hannuna Mahaifinsa a Lokacin da Yake Dukansa. Wanda Duk Ya tsananta Kallo ga Mahaifinsa, be Girmamashi ba. Duk Wanda Ya Sanyasu Damuwa, Hakika Ya Sa6a Musu”*. (Albirru Was Silah Na *Ibn Jauzy*: 117)._ _Dan Uwa Ka Duba Kaga Yanda Magabata Suke Girmama Sha’anin Mahaifa, Yanda Suke Ganin Sa6a Musu da Fusatasu Tamkar Yankan Tikitin Jahannama ne._ _Yanzu Ya Rage Gareni Dakai Mu Duba Alaqar Dake tsakanin mu da Mahaifan Mu, Shin Akwai Kyakkywan Alaqa tsakanin Mu Dasu? Idan Akwai Sai Mu dage Wajen Kara Kyautata Musu. Idan Kuma Babu Kyakkyawar Alaqa a tsakaninmu, Sai Mu Koma Mu Roqesu Gafara Kafin Lokaci Ya Qure Domin Samun tsira Anan Duniya Da Gobe Qiyama._ _*Allah Ka Sakawa Iyayenmu da Alkhairi, Wadanda Suka Rasu Kuma Ka Gafarta Musu Kasa Aljannah Ce Makomarsu*_ _Anan Zan Dakata Sai Mun Hadu a Rubuta Na Gaba_ *سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن الإله إلا أنت أستغفرك وأتوب إليك* WAJIBCIN BIYAYYA GA IYAYE                        FITOWA TA HUDU _Da Sunan *Allah* Mai *Rahma* Mai *Jinqai*_ _*ADDU’AR IYAYE NAGARI KARBABBA CE*_ _Lallai Yana Daga Cikin Girmamawa da Ubangiji Yayiwa Iyaye Nagari Shine Amsar Addu’arsu Nagari da ma Wanda ba Nagari ba ga ‘Ya’yansu, Musamman a Lokacin da Girma Yazo Musu. Wannan Kuma Abu ne da Yake Aukuwa Akan Idanun mu a Wannan Rayuwar Tamu ta Duniya. Hakika *Manzon Allah (ﷺ)* Ya Fadakar Damu Akan Haka a Cikin Hadisai Masu Yawa, ga Kadan Daga Cikinsu:_ *{ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﻫﺮﻳﺮﺓ، ﻋﻦ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻗﺎﻝ : ”ﺛﻼﺙُ ﺩﻋﻮﺍﺕٍ ﻣﺴﺘﺠﺎﺑﺎﺕ : ﺩﻋﻮﺓ ﺍﻟﻤﻈﻠﻮﻡ، ﻭﺩﻋﻮﺓ ﺍﻟﻤﺴﺎﻓﺮ، ﻭﺩﻋﻮﺓ ﺍﻟﻮﺍﻟﺪ ﻋﻠﻰ ﻭﻟﺪﻩ“. ‏(صحيح في أدب الهفرد:٤٨٨)}* _An Kar6o Daga *Abi-Hurairah (ra)*, Daga *Annabi (ﷺ)* Yace: *“Addu’ar Guda Uku Kar6a66u ne: Addu’ar Wanda Aka Zalunta; da Addu’ar Matafiyi; da Kuma Addu’ar Mahaifi Akan ‘Dansa”.* Hadisi ne Ingantacce (Sahih Adabul Mufrad: 488)._ _*Hasanul Basary* Yana Cewa: “Addu’ar Mahaifa Tana Tabbatar da Dukiyar Yaro. Sannan Addu’ar Mahaifa Tana Sadar da Dukiya Yaro”. (Al-Birru Was-Sila Na *Ibn Jauzy*: 120- 123)._ _*YARDAN IYAYE NAGARI TANA DAGA YARDAR ALLAH*_ _Wajibi ne Mu Sani Cewa Lallai Akwai Dangantaka tsakanin Yardan Ubangiji da Kuma Amincewar Mahaifa. Saboda Hakane Ya Zam Wajibi Akan ‘Ya’ya da Su Kwadaitu Wajen Neman Yardan Mahaifansu ta Hanyar Yi Musu Biyayya a Cikin Abinda Be Sa6awa Mahalicci ba, Domin Samun Yardan Allah Anan Duniya da Gobe Kiyama. Hakika Annabin Mu Ya Shiryar Damu Haka a da Dama Daga Cikin Haidisansa:_ *{ﻋﻦ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﺑﻦ ﻋﻤﺮٍﻭ ﺑﻦ ﺍﻟﻌﺎﺹ، ﻋﻦ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻗﺎﻝ : ”ﺭﺿﺎ ﺍﻟﺮﺏِّ ﻓﻲ ﺭﺿﺎ ﺍﻟﻮﺍﻟﺪ، ﻭﺳﺨَﻂ ﺍﻟﺮﺏِّ ﻓﻲ ﺳﺨﻂ ﺍﻟﻮﺍﻟﺪ“. ‏(ﺣﺪﻳﺚ ﺻﺤﻴﺢ ‏) ‏( ﺻﺤﻴﺢ الترمذي:١٥٤٩)}* _An Kar6o Daga *Abdullahi bn Amru bn Ass (ra)*, Daga *Annabi  (ﷺ)* Yace: *“Yardar Ubangiji Tana Cikin Yardan Mahaifa, Kuma Fushin Ubangiji Yana Cikin Fushin Mahaifa”*. Hadisi ne Ingantacce (Sahih Tirmizi: 1549)._ _Wannan Hadisi Dalili ne Akan Falalar Kyautatawa Mahaifa da Kuma Wajibcin Yin Hakan. Domin Aikata Hakan Shine Sababin Samin Yardan Ubangiji. Sannan Har Wayau Hadisin Yana Razanarwa Akan Sa6awa Mahaifa da Kuma Haramcin Sa6a Musu. Domin Sa6a Musun Yana Sabbabawa Mutum Haduwa da Fushin Ubangiji._ *{ﻋﻦ ﻋﺒﺪﺍﻟﻠﻪ ﺑﻦ ﻋﻤﺮ ﺑﻦ ﺍﻟﺨﻄﺎﺏ ﻗﺎﻝ : ”ﻛﺎﻧﺖ ﺗﺤﺘﻲ ﺍﻣﺮﺃﺓ ﻭﻛﻨﺖ ﺃﺣﺒﻬﺎ، ﻭﻛﺎﻥ ﻋﻤﺮ ﻳﻜﺮﻫﻬﺎ، ﻓﻘﺎﻝ ﻟﻲ : ﻃﻠِّﻘْﻬﺎ، ﻓﺄﺑﻴﺖُ، ﻓﺄﺗﻰ ﻋﻤﺮُ ﺍﻟﻨﺒﻲَّ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻓﺬﻛﺮ ﺫﻟﻚ ﻟﻪ، ﻓﻘﺎﻝ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ : ﻃﻠِّﻘْﻬﺎ“. (ﺣﺪﻳﺚ ﺻﺤﻴﺢ ‏)( ﺻﺤﻴﺢ ﺃﺑﻲ ﺩﺍﻭﺩ ﻟﻸﻟﺒﺎﻧﻲ ﺣﺪﻳﺚ: ٤٢٨٤)}* _An Kar6o Daga *Abdullahi bn Umar bn Khaddab (ra)* Yace: *“Na Kasance Inada Mata Kuma Ina Matukar Sonta, Umar Kuma Ya Kasance Baya Sonta, Sai Yace Dani: “Na Saketa,  Sai Naqi Sakinta. Sai Umar Yaje Wurin Manzon Allah (ﷺ) Ya Ambata Masa Abinda Ke Faruwa, Sai Annabi Yace Ya Saketa”*. (Abi-Daud: 4284)._ _*Fa’idah Mai Muhimmanci:* _Yakamata Iyaye Su Fahimci Cewa Wanda Ya Nemi ‘Dansa da ya Saki Matarsa *Umar bn Khaddab* ne. Ba Kowane Uba Bane Yake da Ikon Aiwatar da Abinda *Umar* Ya Nemi ‘Dansa dayi ba. Musamman Ma Idan Aka Samu Sa6ani tsakanin Mahaifin Yaro da Matar Yaron Akan Abin Duniya, Mahaifin Yaro Kamata Yayi Ya Duba Mas’alar ta Hanyar Adalci, Idan Har Matarc da Gaskiya, Wajibi ne a Tabbatar Mata da Gaskiyarta Uban Kuma Yayi Hakuri Kada Yace Zai Tursasa ‘Dansa Akan Ya Saki Matarsa. Amma Idan Laifinta Ya Sa6awa Ubangiji ne Kamar Batayin Sallah, Ko Magulmaciya ce, Kuma Anyi Mata Nasiha Taqiji, Wannan Uban Miji Yanada Iko Akan Ya Umurci ‘Dansa da ya Saki Matarsa Kamar Yanda *Umar* Yayi. Kuma Wajibi ne ‘Dan Nasa Yayi Masa Biyayya._ _Wani Mutum Ya Tambayi *Imam Ahmad bn Hambal* Cewa: Lallai Mahaifinsa Ya Umurceshi da ya Saki Matarsa, Sai *Imam Ahmad* Yace: *“Kada Ka Sake ta”*. Sai Mutumin Yace: Shin ba *Umar* Ya Umurci ‘Dansa *Abdullahi* da ya Saki Matarsa ba? Sai *Imam Ahmad* Yace: *“Ka Bari Har Sai Mahaifinka Ya Zamo Kwatankwacin Umar”*. (Al-Adabush Shar’iyya)._ _An Tambayi *Imam Ibn Taimiyya (rh)* Game da Mutumin da Mahaifiyarsa ta Umurcesa da ya Saki Matarsa. Sai. *Ibn Taimiyya* Yace: *“Baya Halatta a Gareshi da Ya Saki Matarsa, Sai dai Wajibi ne Yayi Mata Biyayya, Amma Sakin Matarsa Baya Cikin Yi Mata Biyayya”*. (Adabush Shar’i: 447)._ *{ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﺍﻟﺪﺭﺩﺍﺀ : ﺃﻥ ﺭﺟﻠًﺎ ﺃﺗﺎﻩ ﻓﻘﺎﻝ : ﺇﻥ ﻟﻲ ﺍﻣﺮﺃﺓً، ﻭﺇﻥ ﺃﻣﻲ ﺗﺄﻣﺮﻧﻲ ﺑﻄﻼﻗﻬﺎ،ﻗﺎﻝ ﺃﺑﻮ ﺍﻟﺪﺭﺩﺍﺀ : ﺳﻤﻌﺖُ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻳﻘﻮﻝ : ”ﺍﻟﻮﺍﻟﺪُ ﺃﻭﺳﻂُ ﺃﺑﻮﺍﺏ ﺍﻟﺠﻨﺔ, ﻓﺈﻥ ﺷﺌﺖَ ﻓﺄﺿِﻊْ ﺫﻟﻚ ﺍﻟﺒﺎﺏ، ﺃﻭ ﺍﺣﻔَﻈْﻪ“. ‏( ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ: ١٥٤٨}* _An Kar6o Daga *Abi-Darda’i (ra)* Lallai Wani Mutum Yazo Masa Sai Yace: Lallai Inada Mata, Kuma Mahaifiyata ta Umurceni Dana Saketa. Sai *Abi-Darda’i* Yace: Dashi: Naji *Manzon Allah (ﷺ)* Yana Cewa: *“Mahaifa Sune Mafi Alkhairin Kofofin Aljannah. Idan Kaso Ka Tozarta Wannan Kofar, Ko Kuma Ka Kiyayeta”*. (Tirmizi: 1548)._ _Anan Zan Dakata Sai Mun Hadu a Rubuta Na Gaba_ *سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن الإله إلا أنت أستغفرك وأتوب إليك* IDAN KUNASO MUCI GABA SAI KUYI MANA MAGANA TA EMAIL

AHLUSSUNAH AYAU Posst No 1

MAFAKAR SUNNAH AYAU!!!

        Haqiqah Babu batun Sonkai, Salafawa da ‘yan izala sune ke da’awar sunnah Haqiqanin ta zallar madarar sunnah babu gauraye.

Dalilin wannan rubutu nawa:
Shine nuna mecece koyarwar aqeedar sunnah. Da manufar Izala da Salafawa akan sunna dakuma mecece asalin haqiqanin aqidar sunnah

  ********MECECE AQIDAH********

Aqidah:  amahangar Arufai (Malamai)_ wata hanyace wacce mutane suka kebance yadda zasu yi addini karkashin wata mazhaba bisa fahimtar magabata na farko, Bugu da kariaqidah takasance abace wacce take a aikace da furincin baka banda qudirin zuci. Ma’ana Azuci ni musulmine kuma nayarda da dukkan shika_shikan musulunci ina aikatasu amma bisa mazhabar malikiyya. To idan hakane madogarata bani da Ikon tilasta maibin mazhabar shafi’iyyah ko  ko hanafiyya. Bani damar cewa sai sunbi Hambaliyya
Idan mukayi duba danganeda yanayi nayanzu yadda rayuwa tashige rudani yadda Ake kawo abubuwa daban daban acikin addini. Dasunan addini.
Maluma na gaskiya suna iyakacin iyawarsu wajen wayar wa mutani kai dan ganeda hanyar tsira na addini, Amma saidai kuma akasi.
  Anasamun wasu miyagu da suke juya hankulan jama’ah suna b’ata Da’awar tasu.

Danganeda hakane Aka rarraba addini gida_gida aka kuma kirmiro aqidoji iri daban_daban hakika koda yahudu da nasarah suma abinda yararraba kawunansu kenan rabuwar kan maluma.

******Mafakar sunnah dai sune****
Marubuta da wa’azi da walima Wadannan sune hanyoyin da. Sunnah suke yada da’awarsu. Sabanin sufaye Shi’awa da ‘Yan dariqu. Su suna yada aqidun sune da sha’irai (mawaqa) da Majalisi dakuma Mawalid, idan akace mawaali shine jam’in maulidi.
   To A inda gizon ke saqa kuma, shine:   Akan samu sa’bani dan ganeda wasu al’amuran na Hanyoyin yada da’awoyin nasu.
Misali
  ‘Yan izala Da Salafawa sukan soki mauludi da zaman da’ira da Majalisi, dama kuma wake waken da yan dariqu sukeyi. Su kuma yan dariqu Basuda hanyar dasuke yada manufofi da da’awoyinsu sama da wadannan hanyoyi, Dan hakane suma suka sha AlwasAnfagdaura kambun yaqi da dukkannin wanda zai munantawa hanyar da’awarsu.

******Tasirin tarbiyyar aqidu******

***IZALAH SALAFAWA***

Yan izala da salafawa mafiya yawancin makarantunsu haddane da hadisai sai Tauhidi saikuma wasu littattafan addini a matakin farko kuma suna Anfanine da mashabobin makka da madina. Yawancin littattafansu wallafar can ne da sharhohin magabatansu.

***SHI’AH DA DARIQU**
Su kuma yawancinsu suna anfanine da mazhabobin iran da iraqi kuma afannin ilimin farko yawancinsu karatun tsangaya sukeyi. Sai agaba sunfi bada karfi wajen ilimin tarihi da baitoji yabo dana dafawa wannan dalilin ne ma yasa ake samun mawaka dayawa acikinsu.
*****“Nuni sananne dan gane da da’awar sunnah**””””””””
Maganar Gaskiya izala da salaf munada kyakkyawar manufa akan addinin musulunci kama daga maluman  mu dama marubutan mu dama Mu dalibai bakidaya . Burinmu  Azauna da juna lafiya da lumana.
Yan uwana masu  karatu kusani cewa manufar wannan rubutun nawa shine in bayyana mecece haqiqanin Sunnah
Kuma suwaye Ahlussunnah na gaskiya
Danhaka na rarraba rubutun kaso uku
Wannan shine nafarko agaba zakujini da wasu kamar haka:
        
           ******Haske Akansu******

### Suwaye Ahlussunnah?…………..)

Dukkan wanda yariqi sunnah ta annabi kuma yake kokarin dabbaqata kuma yake nesanta daga barna da rarraba kan al”umar musulmi.
      
                 ***Dakuma**

### *Sunnah ba Aqida bace!………….)

Ahlussunnah yana suffantuwane da kyawawan dabi’u baya neman ilimi domin muqabala ko dan.yakare aqidah ba.

BAYAN RAYUWAN DUNIYA AKWAI RAYUWA BAYAN MUTUWA

GASKIYA AKWAI MATTSALA!!!!


Sau nawa kake zama domin Bincike ko sauraron Yadda zaka gyara Ibadarka?????
         Sau dadama idan na kadaita sai nayita tunani dan ganeda lammarin gudanar addini agun wasun mu. Zakaji mutum nakiran kansa musulmi amma farillan alwala ma bai sani balle in ta ‘baci ya gyara farillan sallah ma bai saniba balle inyayi Rafkanuwa yagyara. Ko na wanka ballema ilimin gyaransu.
    Wayyoooni duniya ina zaki damune kowa kagani abinci kawai yake nema kokuma yadda zai huta ko yadda zaiji dadin duniya gaba. Saidai kash itakuma tafiyarnan da take gaban mu batta da rana. Kawai zuwa take kwatsam kara zube ba zato ba tsammani.
    To taya zamu tara guzirin komawa ga mahaliccin mu domin samun hujja garemu aranar sakamako?
    Ansa
    Mukoma munemi ilimin addini mugyara ibadu da mu’amalarmu kafinnan musami hanyar tsira. Wani abin ban takaici shine yawanci mukan jahilci lammarin addini bawai don rashinsaba sai don aqidanci. Mutum baida karatun komai jahilin kauye afagen addini amma saikaji na karyata abubuwan da malamai ke fada dan ganeda hukuncin halasci ko haramcin wani al Amarin addini. Dalili kuwa shine don aqidarsu ta banbanta, Alhali baida hujja ta aya ko hadisi data karyata al’amarin dalili kawai don malumansu basayi yan abiyari (inbasu wane bazamuyiba).
    Wannan shi ake kira da shi’anci ashari’ar musulunci ma’ana raba kan al’umar musulmi. Tahanyar sabawar fahimta ko mazhaba. Abubuwan da kejawo haka sune:
    _Jahilci
    _Son zuciya
    _Son shahara
    _Munafinci
          ***JAHILCI***
    Idan jahilci yayi naso (katutu) azuciyar mutun saikaga na karyata koma mene ne addini ni kuma in yayi shugabanci zai dinga shirme yayita kawo jahilci alammuran dasunan gyara daga karshe zaiyita kokarin fada da malamai idan suna fada masa gaskiya. Jahilci nasa girman kai da hassada matukar maishi na tare da masu ilimi kuma akayi rashin sa’ah yawuce su wata daukakaka tarayuwa.
       ***SON ZUCIYA***
Idan mutum nada son zuciya komai aka fada bazaibiba sidai yakowo tasa abi. Koda tasa hanyar me raunice zai toge yadage akan sai anbi tasa daga karshe in anki zai fara neman mabiya daga baya saikaji ya Fidda tasa sabon kungiyar daban ko juma yafandare yayi reshe akungiyarsa daban.
    ****SON SHAHARA****
    Mafiya yawanci anfi samu daga wanda suka ‘Danyi karatu amma bamai nisaba sunason taka hawa mai nisa amma kafarsu baikaiba. Burinsu dai komai zai wakana yazam anyishi harda furucinsu. Amma basuda cikakken ilimi abangaren irin wadannan ywanci akansamu masu kyakkyawar manufa amma rashin ilimi mai nisa yana wargaza manufar nasu.
    Yakai dan uwa shawarata gareka katsaya iya matsayin ka kabar abinda Bakasaniba.
    Masu hikima nacewa Bansaniba shima wani yankin ilimine.
   
      *****MUNAFINCI****
    Akwai wasu burinsu kawai azagi musulunci da musulmai. Zasu tsaya kai da fata su tabo wannan aqidan da wata ta daban, Harsu haddasa wata rigima tsakanin musulmai wadannan basuda wata kyakkyawar manufa akan musulmai wasunma bamusulmai bane burinsu su wargaza wata shiri ko wata tanadi wacce musulmai sukeyi, ko don su raba kawunan al’umar musulmi.
    Allah katsaremu daga sharrin makirai da fajiran munakan addini.
    Allah yamayar da makircin garesu dasu da wanda suke sasu.
    Allah kabudemana kwakwalenmu don gujewa afkawa rudanin addini.
    Allah  kabawa maluman mu damar isar mana da gaskiyar koyi na Addini.
   

AQEEDAH TA ITACE MUSULUNCI

AQEEDATA

Dasunan ALLAH MAI RAHAMA MAI JINKAI

      Wasallahu Alaa man Laa Nabiyya ba’adahu Muhammadun bn Abdullah .(ﷺ) Salawatullahi Alaihi, wa Alaa Aalihi wasahbihi wasallama tasliiman khasira.

Waba’ad;
Assalamu alaikum warahmatullahi warahmatullahi wabarkatuhu, Mai karatu idan baka manta ba ada nayi Alqawwarin fadawa mai karatu mecece aqedata, dakuma matsayata dangane da halascin wakokin yabo da kirari da Haramcin kida Amusulunci.

Ⓜ Mashaa ALLAH Alkawwari yacika;
     Ni Ismail Hussaini Basalafene (Assalafy) Ne. Sala ba Kungiyace ta Aikin addini bawai Shi`anci bane. Wata al umace dake aiki akan Hani ga barna dakuma umarni da aikin Alkhairi. wacce take kuma koyi da magabata. Ainihin Kalmar Salaf tana nufin Magabata.

Salagiyya kuma tana nufin Bin tafarkin magabata. Wannan itace Al umar damuke koyi dasu na kwarai din cikinsu. Amma mu musulmaine kamar Sauran musulmi. Kuma munyi imani da Alqur`ani da hadisai kuma manzon mu shine مُحَمَّد ﷺ

Shi muke kwaikwayo a hali dakuma ayyukan.
Basai nayi bayani akan ko mene aqidah ba. Domin abaya nayi bayani akai karin bayani dan ganeda aqidar salafawa shine { (Aqeedadussalafussalih bi muwafaqati Sunnatin_nabawiyya wa Ashabuhum) (Ma ana aqidar bin tafarkin annabawa da sahabbansu) }.
   Aqidar itama Ahlussunnah ce akarkashinta akwai izala kamar yadda akasani, wadda suke da manufa iri daya dan ganeda da`awa da tsarukan karantarwa iiri daya saidai ita salafiyya kuma tafi yada da awarta ta social media fiye dana izala. ma`ana tafi dukufa wajan rubuce rubucen tarihi ta hanyar wayar da kai ga addinin musulunci da musulmai bisa yadda Zamani yakasance.  Dawayar da kan mutane Dan ganeda rayuwarsu dazamantakewarsu da Ladaftar dasu da koya masu dabarun rayuwa dawayar dasu Ga addini suyishi sukuma dabbakashi dayadashi a duniya.  Dukka sune Aikin salafawa.
Kar nazurfafa atakaice wannan itace aqidata. saikuma magana akan maulidi da kasidu masu kida da da marasa kida.

WAKOKIN YABON ANNABI
Haqiqa wakokin yabon annabi babu Kida ya halasta kaidai dolene yazama duk yaren dazakayi wakan yabon annabi dashi. yazamana kana da ilimi akan yaran sosai domin kiyaye kalmomin da zakayi amfani dosu, donyin yabon kuma dolene ka koyi ilimomi aka yaran kamar haka: ilimin balaga, Qaamusu, Ka`idojin rubutu, Ilimin Grammar, Dakuma tarihim annabin dama mawakansa  nada, domin azamanin annabi  ﷺ Anyi masa waqoqi dayawa harma ayari yake dasu na mawaka Ammafa su basuyi da kida bakuma yi sukeba Dan holewarsu ba ssunayine domin maida martani wa kafirai sai kuma domin dafawa Ga fiyayyen halittaﷺ kutambayi malamai zasu baku karin bayani akai.
    To awannan zamani namu akwai mawakan dake waqoqi nayabo amma da kida ko nace kayan sauti mabanbanta. wallahi! Tallahi!! Billahillazi La ilaha illahuwa wuce gona a kayan kida sautin shaidanune!!!

Me karatu kayi shari ah ta adalci٠
Masu wakokin yabo ayanzu musan man agun maulidi shin kaso hamsin cikin dari suna tantance me suke fada kafin su fada awakokinsu? babu shakka Amsar itace a`a.
   Muyi wa kanmu adalci waqa na ilimi wanda ba kida nayabon Annabi yahalasta amusulunci, ko muma a Tafiyarmu ta salafawa munada mawaqan yabon annabi amma basuyi da kida kuma sai an karantaddasu kuma littafai suke bugawa akuma tantancesu agaban malamai kafin suje subayar ga masu hazakar furuci su rera wakokinsu ba cinzarafi da zagi ko aibata wani ko wata aqida da ace ´yan d`ariqun sufaye da ´yan Shi`ah suma zasuyi adalci wa kawunansu dasai suma su rage msu hankalin cikinsu yakamata su daina waka da kida suyi waqa tsarkakakkiya da yabo wanda yadace da tunani mai kyau da koyarwar Addinin musulunci.
 

 BIKIN MAULIDI 

Bashakka bikin Maulidi Bai ingantaba koda ahadisine mai raunine babu, ba  ko wata yarjeniya ta wata ayari namaluman sunnah danayanzu dana da duk sun daidaita akan bai ingantaba. Hasalima suna kirantane da bidi´ah muhadatha ma`ana bidi`ah kirkirarriya. Batada tushe ko asali daga magabata, akwai hadisai dayawa wadanda suke tsawatarwa danganeda kirkira a addini. Arufai na tsawatarwa danganeda kirkira a addini. Ayanzu acikin maulidi allah ﷻ Shine kawai yasan bidi`o`in da aka kirkiro.
  Banso Raba rubutun  ba amma dolene ta saka `yan uwa kuyi hakuri muhadu arubutu nagaba mai Taken Aqeedata