Nasarorin Ƙungiyar Arewa Media Writers

Nasarorin Da Ƙungiyar “Arewa Media Writers” Ta Samu Cikin Shekaru Biyu, July 2020, Zuwa July 2022

Ga wasu daga cikin nasarorin shekarar farko July 2020 zuwa July 2021;

  • Ƙungiya ta samu karɓuwa a wurin al’ummar yankin Arewa.
  • Haɗin kan Marubutan yankin Arewa.
  • Magana da murya guda a madadin dukkannin Marubutan Arewa.
  • Kare martabar yankin Arewa, da al-ummar yankin, kan ƙalubalen da suka dinga fuskanto yankin.
  • Wayar da kan al’ummar Arewa game da abubuwan da zai amfane su, da wa ‘yanda ba za su amfane suba.
  • Wayar da kan al’ummar Arewa game da kin shiga zanga-zangar EndSars, da ‘yan kudancin Najeriya suka yi a shekarar 2020 wanda ya kusan zamowa fitina.
  • Daƙile manyan labaran ƙarya kafun su yi tasiri a cikin al’umma.
  • Nasarar da ƙungiya ta yi wajan tallata “Ranar Arewa” 20 July 2020 na kowace shekara, bayan wasu masu kishin yankin sun kirkireta, don tunawa tare da jawo hankulan manyan Arewa kan dukkannin kalubalen da yankin ke fuskanta.
  • Koyawa Marubuta yadda ake rubutu, tare da saka Gasa domin zaburar da Marubutan Arewa a wasu daga cikin jihohin Arewa.
  • Jawo hankalin hukumar WAEC a shekarar 2020 kan saka lokacin zana jarabawa a daidai lokacin da musulmai suke gudanar da Ibada a ranar Jumma’a, daga karshe hukumar ta gyara lokacin.
  • Jawo hankalin gwamnatin jihar Jigawa kan ƙalubalen da talakawa zasu fuskanta, idan aka daina karatu kyauta a Jami’a mallakar jihar (Free Education) bayan majalisar jihar ta yi yunƙurin mai da tsarin biyan kuɗi mai yawa ga dukkannin daliban jihar.
  • Jawo hankalin gwamnatin Tarayya da jihohi akan Tallafawa al’ummar da iftila’in ruwa ya shafa, a jihohi da dama na Arewa a shekarar 2020 da shekara ta 2021.
  • Jawo hankalin mahukunta dake da alhakin kunnawa manoman Rani ruwa a garuruwan Bunkure, Kura, Garin Mallan, Da Garin Karfi dake jihar Kano, bayan abinda suke nomawa ya fara bushewa saboda rashin ruwa.
  • Jawo hankalin gwamnatin jihar Adamawa wajan sasanta rikicin masu sana’ar adaidaita (Keke-Napep) a garin Numan dake jihar, duba da yadda dubunnan Al-ummarmu suka dogara da sana’an.
  • Jawo hankalin gwamnatin Najeriya da na jihohi game da halin rashin tsaron da ya addabi yankinmu na Arewa.
  • Jawo hankalin ‘yan kasuwa game da halin matsin rayuwa da al-umma suke ciki, sanadin tsadar Abinci.
  • Rubuce-rubuce tare da zaburar da matasa akan su tashi su nemi sana’a domin su dogara da kansu.
  • Tallafawa daliban makaranta da robobin cin Abinci guda 100 a jihar Zamfara.
  • Nasarar samun goyon bayan manyan Arewa Sarakuna, Dattawa, da sauran manyan dake kishin yankin Arewa, wurin gudanar da ayyukan kungiyar.
  • Gudanar da manyan taruka a wasu daga cikin jihohin Arewa da dama, domin haɗin kan Marubutan Arewa, tare da ƙarfafa zumunci a tsakaninsu don fuskantar duk wani ƙalubale da ya tunkaro yankin.
  • Jawo hankalin gwamnatin Najeriya kan ta gaggauta daukan mataki akan kisan kiyashin da ake yiwa ‘yan uwanmu ‘yan Arewa dake zaune a kudancin kasar.
  • Ankarar da gwamnati game da matsalar gurbacewar ilmi a cikin al’ummah.
  • Kira kirayen ƙungiya ga gwamnati kan a kawo ƙarshen satar yara a makarantu.
  • Jawo hankulan al’ummah kan muhimmancin ilimin ‘ya’ya mata.
  • Tunatar da al’ummah da faɗakar da su na tsawon kwanaki 30 na watan Ramadan a shekarar 2021.
  • Yunƙurin kawo ƙarshen bangar siyasa a kafofin sadarwar zamani.
  • Nasarar samun shiga gidajen Radio da Television a jihohi daban daban don bayyana manufar ƙungiya da kuma alfanun kungiyar.
  • Ƙungiya ta zaburar da dubban matasan Arewa kan su nemi basussukan da gwamnatin Tarayya take bayarwa domin dogaro da kai.
  • Ƙungiya ta samu nasarar ƙulla ƙawance da ƙungiyoyi mabanbanta don ciyar da yankin Arewa gaba.

SHEKARA TA BIYU

Nasarorin da ƙungiyar “Arewa Media Writers” ta samu a cikin shekara ta biyu da kafuwarta daga July 2021, zuwa July 2022.

Ga wasu daga cikin nasarorin;

  • “Arewa Media Writers” tayi nasarar kai koken al-ummar musulman garin Obajana dake Kogi, bayan ruwan sama ya lalata tsohuwar maƙabatarsu, har sarkin Obajana Kirista Engr. Dr Idowu Isenibi, Oba Of Obajana ya baiwa musulman garin Obajana makeken Fili Hetka 10 da samun gudumuwar kudi sama da miliyan daya da rabi.
  • Ƙungiya ta wayar dakan al-ummar Arewa, tare da kira ga al-ummar Arewa da su yi ragistar katin zabe a lokuta daban daban, duba da yadda ‘yan kudancin kasar suka yi mana fintinkau.
  • Ƙungiya ta dau nauyin horar da ‘ya’yan Ƙungiyar wajan koyar da su yadda ake rijistar katin zaɓe ta yanar gizo-gizo a wasu daga cikin jihohin Arewa.
  • Ƙungiya tare da hadin guiwar babban dakin karatu na jihar Kano ta yi nasarar bawa mutane 131 horo akan loyar da su ilimin na’ura mai kwakwalwa.
  • Jami’ar koyar da harsuna ta kasa da kasa “International University of Languages” (IOUL) dake jihar Sokoto ta dau nauyin koyar da membobin kungiyar “Arewa Media Writers” ilimin sanin aikin yaɗa labarai a zamanance “Social Media in ICT” tare da basu Certificate na shaidar karbar horo.
  • Kungiya ta ziyarci tsangaya tare da raba kayan tsaftace muhalli da kayan shayi a babban birnin Tarayya Abuja.
  • Ƙungiya ta bada gudummuwa wurin ganin an raunata jaridar “Sahara Reporters” kan batanci da ta yiwa Annabi (SAW) da yankinmu na Arewa, wanda har yau bata da wo cikin hayyacinta ba.
  • Ƙungiya ta jawo hankalin gwamnati kan gyaran asibitin garin Garun Babba, dake karamar hukumar Garun Malam a jihar Kano, wanda shugaban karamar hukumar ya dau nauyin gyarawa.
  • Ƙungiya ta wayar da kan al’ummar Arewa game da abubuwan da zai amfane su, da wa ‘yanda ba zai amfane suba akan rayuwar yau da kullum.
  • Ƙungiya ta yi tattaki zuwa Abuja, ta kaiwa shugabannin hukumomin tsaron Najeriya budaddiyar wasika kan halin da al-ummar Arewa suke ciki na rashin tsaron da ya addabi wasu yankunan dake yankin, tare da jawo hankalin su da su ƙara zage damtse don ganin an kawo ƙarshen rashin tsaron da ya addabi yankin.
  • Kungiya ta yi nasarar turawa shugaban kasar Najeriya buɗaɗɗiyar wasiƙa, ta gidajen jaridun DAILY Trust, Blueprint, VOA Hausa, da sauran manyan jaridun ƙasar, kan halin da al-ummar Arewa suke ciki na rashin tsaron da ya addabi wasu yankunan dake yankin, tare da jawo hankalin shugaban ƙasar da ya ƙara zage damtse don ganin gwamnatin shi ta kawo ƙarshen rashin tsaron da ya addabi yankin.
  • Ƙungiya ta yi Nasarar rubuta Littafi mai suna “RAYUWAR SAMARI DA ‘YANMATA A SOCIAL MEDIA” wanda aka yi bikin kaddamar dashi a watan junairun shekara ta 2022.
  • Ƙungiya tayi nasar gudanar da taron bita akan amfani da kafofin sadarwar zamani a jihar Filato.
  • Ƙungiya ta ja hankalin matasan Arewa a lokuta da dama, tare da wayar da kansu akan su guji bangar siyasa, don gobensu tayi kyau.
  • Ƙungiya tayi nasarar rubuta littafi mai suna “matar bahaushe” dake dauke da darusa iri-iri, anyi akayi bikin kaddamar dashi a jihar Jigawa.
  • Ƙungiya tayi nasarar horar da membobinta “Excos” reshen jihar Sokoto na tsawon kwanaki uku “3 Days Seminer” akan yadda ake rubutu.
  • Ƙungiya ta gudanar da rubuce-rubucen jan-hankali masu yawa a gidajen jaridu da kafofin sada zumunta, game da cin kashin da ake yiwa ‘yan uwanmu ‘yan Arewa dake zaune a kudancin Najeriya.
  • Kungiya ta yi nasarar horar da marubutan Arewa sama da 500 game da yadda ake aikin jarida da rubutu a kafofin sada zumunta, tare da basu takaddar shaidar karɓar horo (certificate) wanda yanzu haka yake gudana. Insha’Allah kungiyar “Arewa Media Writers” za ta gudanar da irin wannan seminar din a kowace jiha dake Arewacin Najeriya, don horar da dukkannin masu amfani da kafofin sada zumunta a kokarin kungiyar, na tsaftace harkar rubuce-rubuce a kafofin sada zumunta.
  • Ƙungiya ta gudanar da Rubuce-rubuce masu amfani ga al-ummar Arewa, da ba za su ƙirgu ba, tun daga watan July na shekarar 2020 da aka kafata har zuwa yanzu July shekarar 2022.

Mamallakin Wannan Kafa Tareda Alhakin Sanya Rubutu Gamida Hada Manhajar (Appllication).

Danna Maballin da Aka Sanya Manhajar Tarihi, Domin Saukewa Yanzu.

Edited by

(Paper Presentation Committee)

Abdulrahman Suleiman Zaria

Chairaman

Muhammad Kwairi Waziri

Secretary

@Coded Prints 08137556140

Ameera Yusuf Duguri

Treasurer

Huzaifa Ayuba

Member

Bashir Abubakar Gombe

Member

Walida Hussaini

Member


Shared By

ISMAIL HUSSAINI ALPHOLTAWY

Member

Hakkin Sanyawa Awannan Pejin tareda Mallakar Peijin

TARIHIN SHEIKH ISMA’ILA IDRIS BN ZAKARIYYA

TARIHIN SHEIKH ISMA’ILA IDRIS BN ZAKARIYYA !!!
     **Gwagwar mayarsa wajen Kafa Izala da Sunnah***

Sheikh Isma’ila Idris

yatasone cikin al’umar nan tamu ta Nigeria, ayankin Arewa inda awannan lokacin babu wata aqida a Qasarnan bayan Dariqar Tijjaniyya, Qarqashin jagorancin sheikh Ibrahim Inyas Alkaulahy.
     To dake zamani ya Nausa tafiya tayi nisa, Al’uma tasamu kanta cikin yanayi na Cakuda addini da Son zuciya. Ana samun Malamai masu Sanya Son ransu acikin addini suna anfani dasunan Addini Suna isarda Munanan manufofinsu ga Al’uma kalar Bokanci da Sihirin Duba dama wasu Tsubbace_tsubbace su na Son Zuciya da Neman duniya.
    Wanda yaci karo da koyarwar Addinin Musulunci. Dukkan mai irin wad’annan aiki Bai tabayinsu Saiya fita a addinin Musulunci, Yazamo dukkan wanda yayi Sunansa kafiri da Nassin Aya acikin Suratu baqarah. Haqiqah bayan Wannan Akwai wasu littattafai dadama wadanda Maluma suka shigo dashi ake karantasu na Labaran mafarki da Tatsuniyoyi dasunan Adddini, Irin wadannan abubuwa dakuma makamantansu Sune maqasudin Da’awar ta Sheikh Isma’il Idris, abisa fahimtar masu kyautata masa zato.
    Da’akwai wadanda suke ganin cewa kawai yafara da’awar izala ne kawai Don Neman Suna dakuma Zagin Wasu malamai (Shehunnan ‘Dariqu) dakuma Sufaye. Wanda kuma hakan kuskurene domin  Aikin Musulmi shine kyautatawa juna zato. Da Kuma nemawa juna gafara agunda akayi Kuskure danganeda Sa’banin Ra’ayi ko Fahimta.
    Zamu cigaba ta Tarihi.
    Bayan Malam Yabar aikin Soja wanda acikin Aikin nasa na Soja ya fara da’awa akan barin Tsubbu da Daura layu da makamantansu, Malam yasha tsangwama daga makiya dakuma wadanda basu da ilimi wanda basu fahimceshi ba. Ba awannan Lokaci malam yaga cewar Wannan Da’awa tasa bazata cigaba ba Har saida wata Qungiya Wacce zata Tallafa masa Danganeda samun cikar Qudirinsa na Farkadda mutane game da Sunnah Asali.
    Awannan lokacine malam ya Assasa wata Kungiya mai Suna; ”Jama’atu izalatul Bid’ah ” Ma’ana ( Gungiyar dake kawar da Bidi’ah ) Wannan Kungiya Tasa tasamu karbuwa hatta aciki ‘Yan uwa Sojoji na wannan lokaci, Saidai kuma tasamu naqasu Sosai daga Malaman wannan zamanin Musamman wadanda keda Wannan aqidar ta Tsubbace_tsubbace da Duba. Tayadda sukayita yimasa Tuggu da zagon kasa gurin Sun ga sun dakushe wannan aikin Nasa, Tare da Wargaza aikin Nasa tahanyar kirkiran karya akansa hadda cutar dashi domin Su samu Galaba akansa, Amma ahakan Allah ya Tserataddashi daga dukkan tarakunan nasu Allah ya kuma karfafa Wannan Da’awa tasa har ilayau Qugiyar izala tana nan kuma tana cigaba da aikinta wajen karantar da Al’uma bisa koyarwar magabata dakuma Tabbatar da Qur’ani da Hadisi sune tafarkin Tsira ga Bayi.
    Ahakan aka cigaba da kasancewa har takai yaje izuwa ga Malamin sa na Tauhidi Assheikh Abubakar Mahmud Gumi, Domin neman izini da Karin lamani dangane da Da’awar tasa. Awannan lokacine Sheikh Abubakar Mahmud Gumi ya nuna Bashi Cikakkiyar goyon baya gamida Cikatamasa Sunan Gungoyarsa da ” Wa’iqamatissunnah ”  ma’ana ( Dakuma Tsayar da Sunnah ) Wcce tazamo ” Jama’atu izalatul Bid’ah Wa’iqatissunnah ”
    Ma’an ( Qungiyar dake kawar da Bidi’a kuma take Tsayar da Sunnah )
    Domin acewarsa Sheikh Abubakar Mahmud Gumi; Babu Yadda za’ayi akawar da bidi’a abarta haka ba acike Gurbinta da wani abu ba, Shine Yace to sai Acike Gurbinta Da Sunnah.
    Kunga Ashe kenan ita Izala ba Fitina bace Sabanin Yadda wasu daga cikin maluman ma da basu fahimta ba, Kuma bawai Reshen addini bace kamar yadda wasu suke yimata Mummunar fahimta Har ma wasu ke ganin Cewa in baka ciki to baka cika musulmiba, wasu kuma ke Mata ganin Cewa inkan cikinta Musuluncinka da Gyara Haqiqa Dukkan Mai yiwa Wata Aqidah ta Musulunci ganin Wannan Al’amari, Alal hakika ya Jahilci Hakikanin Musulunci,
    Wannan kadan kenan daga Tarihin Sheikh Isma’ila Idris da Gwagwarmayarsa gurin kafa Izala, insha Allah Anan gaba Zan kawo muku Cigaban da iza ta Kawo Wa Musulunci da Kasarmu baki daya. In Allah mai Komai ya kaimu bayan Sallah.
    Nine naku Isma’il Hussaini Adam Alpholtawy
    Kuma Wannan Shine karshen Rubutuna danganeda Shafukan Tarihin na Bana A Hijira sheka ta 1442 Saikuma Allah ya Kaimu Almuharram Shekara ta 1443 Zan cigaba da Wannan Tarihi.
    Mai karatu ga Addu’a ta Katayani da Ameen.
    Ya ALLAH Kajiqan Mahaifina Hussaini Adam Jumba wanda Ya Rasu a irin Wannan wata Mai Alfarma kuma Aranar Idin Adhhaa, Idin Babban Sallah Allah Kajikansa Ka gafarta masa ka kai Harke Qabarinsa, Kabashi Aljannah Madaukakiya.
    Ya ALLAH Mu Zuri’arsa Da muka Rage a bayan Kasa Allah ka azurtamu da Dogora abisa Addininka, Kabamu Shahada irin tasa, kasanyamu Cikin Wadanda kake Yantawa Zuwa Aljannah.
    Ya ALLAH Ka Sitirtamu da Sutura ta Musulunci, Ka azurtamu da Arzikin imani, da Ikhlasi da Tabbatuwa akan imani, Har Mu Mutu muna masu imani Da Miqa wuya gareka Allah.
    Ya ALLAH ka daukaka musulunci da musulmai, ka Qaskantar da Kafirci da Kafirai kadirkake makiyanka makiyan addini Allah kataimaki bayinka Nagari.

HADIN KANMU HANYAR TSIRARMU

💾📱📚

Ismail Hussaini Alpholtawy

  Rayuwa ta ishemu Wa’azi
Malamai kuji tsoron Allah wajen Karantarwa kada kusa Son Zuciya. Domin tsira da mutuncinku aduniya da tsira da imani aran Qiyama

Dalibai muji tsoron Allah, Mufahimci junananmu Yayin Sa’bani, Kada Muce komai Malam  wane yafada Gaskiya ce, Binciken Yafi Sauraron Mu yawa.

Muyi riko da Tsarin Allah Mugirmama junan mu kada Murarraba, Rabuwa A Al’uma fitinace, Yawan jayayya yanasanya Masu Son zuciya yad’a ‘Barna kuma yakan sa Wasu gaba da juna Bisa Rashin Dalili.

Mukula Da amanar junan mu gun jaddada Sa’bani, Muyawaita zantawa da juna domin warware Sa’bani mukula da Wadanda ke son tada fitina a Addini Sud’in wawayene kuma jahilai, danganeda Harkokin Addini Basusan komai ba Sai musu da Cinzarafin Malamai.

Akowace aqeeda akan iya Samun masu mummunar manufa da Kuma Son zuciya. Babbar matsalar rayuwa Shine aiki da Jahilci, dakuma Son Zuciya.

Mu Janye Gaba da juna danganeda bambamcin aqeedah. Meyin hakan Bai fahimci addini ba Son duniya da Son zuciya Shiyake sa Mutum yakasa Barin Mummunar Aqeeda da Mummunar halaye a rayuwa da Addini.

Addinin mu yatanadar mana komai, Bamu Bukatar wata hujja idan Nassi ya inganta. Maluman mu nada da Yanzu Sun mana gata.

daga Matsala ta Kunno kai Sai mubude littafi. Idan muka Zauna Kushe littafan mu da muzantashi. Zamu wayi gari Muna Qauracewa gareshi. Har yazamto mun Halaka kamar Yahudu da Nasara.

Idan Munji gyara Muntabbata gyara ce to yazama wajibi mugyara, Kada Mutsaya Sauraron Ra’ayin Wane ko Matsayar wani Malami, Kowani ‘Dan adam ajizine, Malam Wane Ba Annabi bane Yakan iyayin Kuskure Ko Qarancin Tunani.

Addini dayace Sa’bani Sharri ce kuma fitinace, Hanyar gujemata Shine bincike da Neman Ilimi. Da Gujewa Rudin Duniya dakuma Komawa ga Allah ﷻ.

Idan kai ba malami bane kadaina katsalandan aharkar Fatawa ko Matsayar malamai, Yin hakan Shike janyo d’alibi yaraina Hatta malamin dake karantar dashi.

Malamai Su hada kansu Domin kaucewa yawan Sa’bani, Rashin Zantawa da juna shikesa malamai Sa’bani wani abinma labari kakeji daga ‘Dalibanka wani kuma Baka gama jin Kammalallen saba. Yazama dole Dole muyi Bincike.

Idan kasabawa Maluman dakake tare dasu kadauka kaine akan Kuskure, Ko baka fahimcesuba Kuma kana kyutatamasu zato amma ayimaka gamsasshiyar bayani. Amma idan Kaki kuwait Shaid`an Zai Rinjayeka Ko da akan Gaskiya kake. Domin Kurama takan Cinye Dabbar da ta Ke´bene.

Laifin Wani baya shafan wani agun mu mu ‘Yan adam, Kada Wani wanda ba aqeedarku daya ba yayi magana kayanke hukuncin Dukka aqeedar haka suke. A`a Shidai haka yake amma akwai Wasu nakirki acikinsu.

‘Dalibai Mudunga Girmama maluman mu, Munemi ilimi ba Son shaharaba. Babu amfanin ilimi idan bai zamo hanyar Tsirarmu ranar Lahiraba.

Idan wani yahalaka Sanadinka kana da Kaso cikin Sakamakon da za’a Qaddamar masa.

Idan Hasashen Mutane gaskiyace! Tabbas akwai wadanda ke kar’bo kwangila domin ‘Bata Addini. Amma kuskurene muyi Jam’i, Dole akwai wadanda da gaske suke Kuma Sunada yaqinin Tabbatuwar su akan Gaskiya Suke.

Dole ne Mu martaba Magabatan mu, Idan Munga kuskurensu mu nema masu gafara. Mudaina Tonan Silili ga ‘Yan uwanmu, Idan za’ayi tonon silili wa kowa Babu mai tsira Gaban Allah.

Munbar koyarwar addini, Mundauki Al’adar yahudawa, Amaganganun Mu komai yazo furtawa Muke babu Tantancewa. Muna da Laifi amma hangen na wasu yahanamu neman Afuwar Namu.

Muyo ‘Da’ah Cikin umarnin Annabi nadaga abinda yazo cikin Alqur’ani da Hadisi, Muhanu daga abinda ya tsawatar, Mubautawa Allah cikin Koyarwarsa ﷺ.

Kada mu yarda da Munanan kalaman da ake furtawa ga Sahabbansa رضی الله عنهم ورضو عنه, Hakan zai iya taba darajarsa ﷺ, Mud’auka Cewa Ma’kiya addinine Suke Kokarin raba kawunan mu.

Inmunga Matsala a Alaqarmu ta Aqeeda Muzauna Muwarware mukoma ga Allah musamu mafita. Na tabbata rayuwar mu zata Sauya.

Bissalam Nine naku Ismail Hussaini Alpholtawy

***SA’KON FA’DAKARWA GA AL’UMAR MUSULMI ****

      **lokaci yaquremana** 

     Idan Har a kullum zamu dinga Nisantar Wa’azine dan ana fad’an abinda Yasha Bamban da Ra’ayinmu to Tabbas Zamu Rinqa Nesantar Haske muna Tutsa kanmu cikin Duhun Jahilci, da kafirci,

     Idan Har Sai abinda yayi daidai da Da Ra’ayoyin Mutane Za a Ayyadar aduniya, Tabbas da Wuta ba ayitaba Sai Aljannah inkuwa anyisuma Ko da anzo Duniya babu mai bin Allah.

    Yawancin Mutane Tunatarwa takan Zakke Musu, yayinda Suka tuno da Me zasu tarar a Filin hisabi, Sai imaninsu ga Allah yaqaru, Inkuwa ankoma Shagalin Duniya Kuwa, Allah ma Wasu mantawa suke da Wujudinsa.

   Idan har Zamuce Wai dan Malami yafadi Sabanin Ra’ayin mu, yazamo mutumin banza to Tabbas imani a azuciyar mu zatai wahalar dasuwa. Domin ayyukanmu munana sunfi Yawa, Sukuma Malamai burinsa mu rage.

    Bai zamo dole ace wai Dukkan abinda Zuciya ta natsu dashi yazama Alkhairiba Iyakar Allah shine abinda yahana, koman Jahilcin Dan Adam, daga yashigo Da’irar Allah ta Haramci, na abinda yaqetare iyaka, Yasanta Saidai ya zakkemata domin Son zuciyarsa.

    Kamar Kid’a ma aiya haramta amma muna Saurara kuma yanayi mana dadin ji. Ammafa haramunne. Kuma ma na sanyamu Shagala da Barin Aikin Alkhairi.
   
    Kowani dadi inhar zai hanamu, ko ya nesantamu da jin dadin Lahira Allah kamusanya mana Shi da Mafi alkhairi, Kaine masanin Sirrin asirin Sansanin Sararin Sababin Alkhairan Duniya da Qiyama.

    Mun manta da Yunqurin Shaid’anu akanmu, Muyi nazarin hakan cikin Rayuwa: Sau dadama abinda Allah yahanemu
Zuciyar mu tafison Mu’aikata, Bisa Rud’i da Rinjayar Shed’anun duniya.

      Bai zamo Lallai ba ace; ko Wani abinda Yayi mana dadi Yazama shine halal ba, Tabbas Halal shine abinda yazamo akwai yardar ubangiji acikinsa Babu Shakku bare kokonto.

      Yawan Fad’a da gaskiya yanasa Qeqashewar zuciya, Tabbas idan kaji Gaskiya koda abakin Abokin gabankane, yi kokari ka Kar’beta amatsayinta na Gaskiya, Inkuwa kaqita kuma kana so ka mayar da ita abin ‘kyama, to Tabbas  Zaka Sha Mamakin duniya, Domin Sunan Allah kake yaqa wato Al_Haqqu.

     Ai kuwa dama zaka Qaryata Gaskiyar MA ayarjemaka bisa yadda kake da iko cikin mutane, daga baya Idan gaskiya tabayyana zakasha Kunya, Idan ma Allah yasoka da Shiryuwa ne Saika gyara, inkuwa bakada da rabon haka, Kamutu Ayimaka Hisabi na ‘Batar da Mutane dakuma Aikata Mummunar aiki.

   Dama habaicinnan damuke yawanyi wa juna, da Zagin Juna A Social Media, Amatsayin Sa’banin Ra’ayi ko aqeeda, Da ayoyin Qur’ani muke yad’awa haka da babu ayar da zaka Duba baka Sametaba a Internet. Ko Hadisan Annabi.

     Muyi Tarayya daku wajen yada ilimi na Addinin Musulunci musamu lada sa’bani bazai ta’ba qarewaba A Addini matukar zamu dawwama cikin yiwa juna Raddi da Jahilci. Muyawaita yiwa junar mu NASIHA.

   Wai ko Munmanta da Cewar mu Musulmai ne, Akwai Ranar fa dazata zo Zamuyi Kewar inama adawo damu Duniya Muyi koda Tasbihi guda dayane Mumutu, Dakuwa Munso hakan. Amma babu dama ankulle kofar Nadama da Aiki, Sakamako kawai ake ba Qaqqautawa.

  Kamar Misalin Jarabawar Duniya ce; Sai Ranar raba Result Saikace Ka manta Maths da English baka Baka karasa Amsaba abaka dama kaje ka gyara aikuwa lokaci kam yakure.

    Allah ka Albarkanci Rayuwar mu da ayyukan Nagarta Dakuma zuciya mai imani da dawwama a imani Har mu samu Rabo Aranar Sakamako. Allah kajikan iyayenmu matattu.

    Naraye Allah ka qara Masu Lafiya da imani da Tabbatuwa Akan imanin Har Mu samu rabo na Lahira Mu dasu Muyi Tarayya cikin Samun  kyakkyawan Sakamako anan duniya da Gobe Qiyama.

** KYAWUN FATANA GA AL’UMAR MUSULMI**

    Nayi nazari cikin tsarin Rayuwar Malumanmu na Musulunci, acikin Kyautata zatona danayi Garesu da kyakkyawan Fata sai na hango Maluman mu na Najeriya acikin Da’irar Son Ma’ki da kishin Sahabbansa da Iyalan gidansa

   Inada Lissafin yatiqe dai Munrabene Cikin aqidu Domin Nuna Kishi ahalarar Soyayya
Tayadda ‘Dariqu Suke jaddada So da Girmama waliyyai da Shehunai da Sharifai da Sufaye Domin kasancewarsu Masoya kuma dangi Jinin Fadima Yar Ma’aiki

Sukuwa Ahlussunnah kishinasu ya Ta’allaqane Akan Hidimtawa wa Da’irar Ibada bisa Tafarkin Sunnah da gyara Ibadoji da kiyaye hakkin Annabi da Alqur’ani da Kore Shubuha a Addini

Haka masu jaddada kishin Ahlulbaiti (Ahlul Kusa’i) Suma dai Soyayyace Ragamar su cikin Nuna Hidimtawa wa Sayyada Fadima ‘Yar Ma’ki da Zuri’ar Gidanta Abangaren Sayyadina Ali Allah yakaramasa Yarda

Tabbas gida d’aya Muke karkashin inuwa guda Muke, Matsalar da faruwa acikinmu itace wasunmu na aiki da Jahilci da kuma Son zuciya bisa Siyasar Masu Neman Duniya da gurbata Addini. Masha Allah, Malamai na ya’kar tsarin da salon tsarin Tabbatar da Sunnah gami da kore  Shubuha da qarfafa Shari’ar Musulunci, Muma muzamto wakilan Musulunci kada musanya ido haka kurum muna kallonsu Kamar Telabijin, Ayi muji dadi dan anyi Nasara Akan Ma’kiya Muyi dariya,
    Idan an kore Kazantar wasu To mu abinda yakamata Muyi shine ina datti yake ajikinmu muma Muyi kokari mu wanke, Dan kuwa Malumanmu Tabbas zasu Shud’e kuma Duniya na kara Gur’bata ga kuma Mummunar nufin Yahudawa da Nasara. Muyi Kokarin gyarawa kuma mu ankarar da juna danganeda Zamantakewa da Ibadoji.
  Tabbas Malamai gatarin sarane agaremu kuma tsanin hawane mai qarfi bisa haryar tsira da Digar tono asiran ma’bb’bugar Alkhairai. Inhar mukayi sakaci suka Shud’e bamuda Masu maye Guraben su Tabbas Munyi Kuskure Mafi girma, Ina mukeda yaqinin Tabbatuwa, Yaushe Za’amaimaita Kamarsu Sheikh Ismail Idris da Kuma Ja’afar da Albani.
   Ya za’ayi Duniya tamance da ginshiqannanan namu watau Khulafa’Urrashidun, Ina za’ayi jagorori Kamarsu wadanda burinsu Kullum cigaban Addini. Akwai ire_irensu Wadanda ban ambata ba Ammafa Sun Shud’e Wadanda sukayi hidima ajanibin Ma’aiki da Halarar Tsaftace Al’uma daga Jahilci da Duhun kafirci.
    Saidai kuwa Jimamin mu Kullum Shine; Gamu karkashin inuwar Rumfa guda amma Wasu na Kokarin Jijjige rumfar ga barazanar Abokan Gaban dake tunkaran mu, hakan na faruwane ta silar Wasu wawayen cikin mu da bisa Siyasar Masu Son zuciya da marasa hankalinmu.
  
  ** Mecece mafita?**
   Mafita agaremu Shine komawa ga Allah dakuma hadin kai wajen aikin Alkhairi da ya’da Addini da bawa Addinin kariya takowace ‘Bangare tareda aiki da ilimi wajen da Yad’a ilimin, Malami kuwa Yatsaya amatsayin na Fannin dayasani. Allah ne Masanin komai, Bai aikin Musulmi bane Yanke hukunci da Jahilci ko Son zuciya.
    Wani Tunani dake Zuwa cikin zuciyata Mai cikeda mamaki gamida Amsarta, Itace;

     Anya Kiristoci? Yaya Sukeji ko kallon Al’amuran mu na yawan Sa’bani?
   Kwatsam Saina amsa da cewa, Ai mu Munada yaqinin munakan Gaskiya Saidai binta yayi mana wahala bisa Rinjayar Shed’anu da kuma kasawa ta Dan Adam. Su kuwa kullum wa Duniya kadai Sukewa hidima, Sunbar Addininsu ba tsari Matansu Na fita yawo tsirara ba Mutunci Kamar rayuwar dabbobi, Mukuma Kullum burinmu Ya’kar Irin Wadannan tsarikan mukeyi, Mamakin danake garesu Kullum Shine Rashin Kulawa dasukewa ‘Ya’yansu dasukeyi Shigar banza Kamar Basu da Addini Na Tabbata Addinin Kiristanci bai karantar da hakan ba.

**Godiyar mu ga Allah Musulmi **
Addinin mu yagamamana komai kuma mun riski ilimi da Dukkan wata falalar rayuwa da Tsarin Zamantakewa da ingantacciyar Rayuwa da tarbiyya dukkan mai akasin Kyawun hali da dabi’u tabbas yakauce ne wa koyarwar addini.

**Kira ga Dalibai matasa**

          Yan uwana Matasa Dalibai!!! Murabu da malamai Abangaren wa’azantarwarsu Muzauna amajalisi akoyar damu Ibadoji da Tsaftace Rayuwa gamida tarihohin Shiryarwa Mugujewa Shagalar Rayuwa da rudin Duniya Munemi halali kurum akasuwancinmu.
    Mukuma tayasu wajen Yad’a karatuttuka a Social Media tahanyar Recording and Sharing Audio da Video da Pictures quotes gamida Rubuce Nasihohi da Wallafa manhajoji da Websites  da Rubuta Text wa ‘Yan uwa da abokan Arziqi. Domin sanya ilimin Addini cikin duniyar Network da yaqar Shubuhar mutane da wautarsu na Zagin Malamai da Hauka.
    Sannan hakan zaisanya Mu tanadar babban Guziri wa Yan baya, Domin kada Su iske bamu bar musu kyakkyawan koyiba Sai tarin Shubuha gamida Sa’bani, hakan zaisa Masu raunin imani acikinsu Kokonta cikin imani dama Shakku a Addini matukar Basu tarar da abinda zai Qarfafesu na matsaya gudaba Abin koyi. Ya Allah Kaqaramana imani da Ikhlasi da Tabbatuwa Akan imanin Harmu sameka muna Sallamawa gareka Allah karabamu Da Riya da Son zuciya.
  Allah kajikan Magabatan mu Mukuwa Allah kabamu Shahada.

GWARGWADON IMANINKA GA ALLAH.



“Shi imani ga bawa yana tsufa kuma yana sabunta, yana raguwa kuma yana ƙaruwa”

“Yana tsufa ko raguwa da yawan saɓon Allah, sannan kuma yana sabunta ko ƙaruwa da biyayya ga Allah

“A lokacin da Allah ta’ala yaso nufarka da alkhairi, sai ya jarabceka a rayuwarka sannan kuma ya baka damar cin wannan jarabawar don ya sauƙaƙa maka hanyar shiga aljannah”

“Gwargwadon imaninka ga Allah gwargwadon jarrabawarsa gareka, bawa baya zama mai cikakken imani ga Allah har sai sanda ya haƙurtar da kansa abisa jarabawowin da Allah buwayi yake jarabtarsa dasu a rayuwarsa ya kuma jure bai gaza cin wannan jarabawar ba, lallai kada mu manta! Tabbas dukkanin girman wata jarabawa, tana tareda girman kyakkyawan sakamako a gurin Allah, ya Allah ka jarabcemu daidai imanin mu”