MATSALAR TSARO A NAIJA New post 2

MATSALAR MANYANMUNE!!

Matsalar tsaro A’kasata Fitowa ta biyu (!!) ✍️Ismail Hussaini Adam

Matsalar tsaro akasar Nigeria abune mai matukar wuya amaganceta da hanzari, Domin Al’amuran Sun jima Da Cakud’ewa cikin mummunar qaddara da muka samu kanmu aciki musanman Mu Al’umar Arewa. Ansamu akasi tahanyar wasunmu suna goyon bayan ta’addanci aboye, bincki da akeyi ana kin bayyana gaskiya, Shine babban Al’amarin daya gur’bata Al’amuran tsaro A’kasarnan. Wai sai ace anrufa asiri akwai ‘yan Alfarma.

Shifa d’an ta’adda, ko mai goyon bayan ta’addanci, Koda uwarsace data haifeshine yasan zata fallasheshi, Wallahil aziim zai aikata lahira, komai Son da takemai, balle jami’an tsaro ko Masu fad’a aji na gari Wad’anda aganinsu sune Cikas d’insu aharkar dasuke ciki. Yazama wajibi akan hukumomi, Da Shuwagabannin Al’uma ta ayyadar da hukunci, akan dukkan wani mai laifi data kama, takuma yi bincike akan dukkan wanda take zargi da ta’addanci, ko goyon bayan ‘yan ta’adda. Idan Tayi bincike inya tabbata kuma tazartar da hukuncin daya dace.

Hakan shine hanya mafi sauki, Ta hanyar da za’a gyara matsalar tsaro acikin Al’uma.

WANI ABINDA MUKA MANTA

Wad’annan masu laifi da’ake kamawa da sunan ‘barayin gida da masu fasa shagunan, Idan ba’azartar masu da hukuncin daya daceba Sune ake Sayansu Su girmama, Abasu Makamai sucigaba da ta’addanci dakuma Kisan mutane, haka kurum ba gaira ba dalili.

Dole ne acire maganar Alfarma, Dukkan wanda hukunci ta haushi kawai azartar masa shine adalci. Allah yafi kowa son bayinsa Amma yana hukumtasu idan sun aikata ba daidaiba. Tayadda yakema ‘Kona wasuma domin mummunar aiki dasuka aikata. Kuma yayi umarni garemu akan mu zartar da hukunci da adalci akan dukkan wanda doka ta haushi.

Hakika Al’uma tana shiga firgici da mummunar yanayine tahanyar sakaci da’akayi da hukunta masu laifin cikinta. A Nigeria mun sami kanmu cikin wannan yanayi tahanyar Sakacin hukumominmu da shugabanninmu.

RASHIN AIKINYI GA MATASA MA QALUBALENE

Matasa babu aikinyi a kasarnan dalili kuwa Shine, manyanmu basu kishin kafa wadatattun masana’antu burinsu gina gidaje kawai da zuwa ‘kasashen waje. Taya ‘Kasan wajen suka sami Cigabane Bayan samun nagartattun Shugabanni masu kishi Suna kula da hakkin Talakawansu. Yakamata Asamarda wadatattun masana’antu tayadda za’arage masu zaman banza dakuma yan Fasa ‘kwauri akasarnan. A’kasarnan akwai arzi’ki wanda yagirmi lissafi amma kuma munfi kowa Talakawa, wannan yasamo asaline danganeda Rashin tallafin jari da aikinyi ga masu ‘karamin ‘karfi, Saudadama wasu na fara kasuwanci amma da zarar sunsami karayar arzi’ki shikenan yazama abin tausayi. Mai iyuwa ma wanin daganan yakan koma goyan bayan ta’addanci, domin yasamu dukiya koma yazamo member na ‘yan ta’adda.

ANA ZALUNTAR ‘DALIBAN KARATU

Harajin karatu awannan kasa nada wahalar Gaske, ga kuma ana matukar Cin dunduniyar ‘Dalibai tahanyar mugayen Lecturers. Kai harda keta alfarmar (Mutuncin) ‘yan mata. A iya Saninmu ga Manyanmu na yanzu Shine. Sunyi karatune akyauta kokuma cikin sauki, Amma donme suke musgunawa Mutane ayanzu? Mafiya yawan malaman yanzu burinsu shine su samu kudi Suma a’kirgasu acikin masu Arzi’kin ‘Kasa. Bawai su bada karatu ga d’alibai ba kamar yadda yake a hukunce. Wannan yasa suke neman Kudi ido rufe a governati domin cimma burikansu dakuma kirkiro wasu tsaruka mabambamta. wadanda suke da rauni da Da’kushe har’ko’kin ilimi akasarnan.

Strike da ake samu a jami’o’i da Colleges yasamo Asaline daga, Son duniyar wasu daga cikin Malamai. Dolene Govrenati tasan hanyar da zata shawo kan Wannan Al’amari. Mutane na kashe kud’ad’e masu yawa kuma Suna d’aukan dogon Zango kafin su kammala karatunsu. Duk asadin matsalar Yajin aiki (Strike). Kuma akarshe yazamo Sun gama karatu kuma sun rasa aikinyi, Tambaya anan itace, idan mutum mai raunin imani yasha wannan wahalar kuma yarasa aikinyi, Me kuke tunani Zai biyo baya?

MATSALAR ASAMACE

Manyanmu na sama Sune ke morar arzikin ‘kasarnan. Manyan Nigeria mutum daya na d’aukan ma’kudan kud’i a governatin tarayya fiyeda Lissafin mai tunani Amma Nakasansu kuwa suna shan wuya matu’ka, Amma abinda suke samu ko na man mota baya wucewa, ballema aje ga Masarufi, dakuma Suturar jikki da kayan ‘Kawar ado. Don me corruption bazai Existing atsakanin muba Alhali wasunmu naci da gumin wasu. Su kuma manta da Hakkin dake tsakaninsu na zamantakewa. A’ka’idar Zamantakewa ta mususukunci dolene kasan Ci da Shan ma’kocinka Kamar yadda zakasan na Iyalinka.

Amma ayanzu babu ruwan wani da Wani, Anyi watsi da karantarwar addini anbi yahudu kuma gashi an’bace ba akamo yahuduba kuma Ambar Allah. Wadannan ma Suna daga cikin Hanyoyi mafiya girma na sanadin Lalacewar Tsaro a Nigeria. Zanci gaba Insha Allah. Allah ya tabbatar damu akan gaskiya da shiriya.

SURATUL FATIHAT

1 – Al-Faatiha – الفاتحة 00:00 1:1 – Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.1:2 – Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu;1:3 – Mai rahama, Mai jin ƙai;1:4 – Mai nuna Mulkin Rãnar Sakamako.1:5 – Kai muke bauta wa, kuma Kai muke neman taimakonKa.1:6 – Ka shiryar da mu ga hanya madaidaiciya.1:7 – Hanyar waɗanda Ka yi wa ni’ima, ba waɗanda aka yi wa fushi ba, kuma ba ɓatattu ba.

MUSAN HUKUNCE_HUKJNCEN ADDININ MU

NEMAN AURE AMUSULUNCI

Dasunan Allah mai rahama maijinkai Haqiqa ANeman Aure yanada matukar amfani musan dokoki da ka idoji da hakkokin ta. AMUSULUNCI Dan kankanin Bincikena da kuma baiwar Da Allah yayi mani zanyi rubutu bisa abinda nake karantawa dakuma wadanda nake gani.

A Zamantakewarmu tayau da kullum. Neman aure. Muhimmin abune GA mutane musani kuma mukiyayesu. Zangina zantukana ne akan wannan muhimmin hadisi, ruwayar Bukhari da Muslim. Manzon Allah (s.a.w) yace “Ana Auren mace don abubuwa guda biyar 1:-kyawunta 2:-nasabar danginta 3:-addininta 4:-dukiyarta 5:-kyawu halinta Sai kuma yace kazabi ma abociyar addini zata zamomana. Yalwar hanu Abin ake cewa yalwar hanu shine zata zamo bata cutaddakai kuma bazata bari acucekaba. Dan uwa mai karatu kaga neman. Mace mai addinima nada matukar fa’ida, Idan kana Neman mace mai addini Zaka San halayenta kamar haka Haku, Kunya, Kaskantaddakai, tsoron Allah, Amana, Juriya, Kirki, mutunci da karamci. Wannan shine halayen mace mai addini, atakaice. Qa’idojin Neman Aure AMUSULUNCI :- Yazamto wacce zaka Neman tana da kamun kai. :- Yazamto tana kana sonta tana sonka son da babu tilastawa. :- Yazamto wacce kakeso tanada hankali da nutsuwa. :- Yazamto mai. Kyawun hali mai addini da tarbiyya. :- Ta zama wacce takeda nutsuwa da kamala da kyau. Ahaqiqanin gaskiya Wannan sune matakan Allah ubangiji ya daukaka musulunci da musulmi. da alkalamin Ismail Hussaini adam IHSAN Assalafy Alpholtawy Matakan Bayar da Tarbiyya Akwai matakai ko hanyoyi da ake bi wajen bayar da tarbiyya da suka haɗa da nuni, lura, umarni da kuma hani. Nuni: Abin da ake nufi da nuni a nan shi ne aikata aiki a aikace, wanda daga nan shi wanda ake tarbiyantarwa zai gani ya koya. Tirƙashi, masu iya magana sun ce; “Idan mutum ya ce zai baka riga, to duba ta jikinsa”. Wannan magana ta zo daidai da faɗin Larabawa cewa; “Maras abu baya bayar da shi”. Saboda haka dole ne mai bayar da tarbiyya ya zama mai tarbiyya. Wannan hanya ta bayar da tarbiyya ita ce mafi tasiri da kuma muhimmanci wajen bayar da tarbiyya. Saboda haka dole ne masu bayar da tarbiyya; iyaye, malaman makaranta da sauran jama’a suma su zama masu tarbiyya. Misali, dole iyaye su zama masu tsafta a aikace, kafin su dasa halin tsafta a zukatan ‘ya’yansu. Idan yaro ya tashi ya ga iyayensa suna share gida tsaf-tsaf, basa barin kwanon abinci da dauɗa, basa jefar da sutura ko’ina a ciki da wajen ɗaki, to a haka shi ma zai girma mai kula da tsafta. Kuma zai tashi shi tsafta ya sani bai san ƙazanta ba. Saboda haka da zarar ya fara zuwa makaranta malaman makaranta ba za su wahala da shi ba. Umarni da Hani (Kwaɓa): Umarni shi ne a riƙa gaya wa yaro yi kaza. Misali, idan yaro ya tsoma hannun hagu cikin kwanon abinci, ko ya riƙe abinci da hannun hagu zai kai bakinsa, sai a gaya masa cewa, wannan ba shi ne hannun cin abinci ba, ga na cin abinci nan. Da haka zai gane hannun dama dana hagu. Shi kuwa hani shi ne kore abu. A wannan gaɓar kuma yana nufin kare ko dakatar da yaro daga aikata aikin da ba mai kyau ba. A cikin wannan misalin dana kawo a sama, akwai gaurayen hani da kuma umarni. Yaro ya tsoma hannun hagu domin cin abinci, sai aka hana shi; wato aka dakatar da shi daga cigaba da amfani da hannun hagu. Sannan aka gaya masa; wato aka umarce shi da amfani da hannun dama. Lura/Kula: Lura ko kula, suna ɗaukar ma’anar saka ido a kan kai-komo na yaro; wato zirga-zirgar yara. Wannan hanya ta lura, cikamakonta shi ne kwaɓa. A nan, iyaye za su saka ido sosai game da zirga-zirgar ‘ya’yansu, duk lokacin da suka ga wata baƙuwar halayya maras kyau, sai su yi maza-maza su ɗauki matakin da ya dace tun kafin ta zama jiki. Da zarar yaro ya fara fita wajen gida domin zuwa makaranta; wato daga shekaru uku zuwa sama, to fa dole iyaye su riƙa lura da shi sosai, saboda yanzu kuma ya je ya gwamutsa da sauran yara daga gidaje barkatai. Saboda haka idan iyaye basu saka lura ba, to tarbiyyar ‘ya’yansu sai ta koma barkata TARBIYYA _Tarbiyya aba ce mai wahala, sai an dage an tashi tsayin daka sannan za’a dasa ta, ya ku Iyaye abu na farko daya kamata ku cusa a zuƙatan yaran ku, ko zuciyar yarinyar ku, ko kuma zuciyar ɗan ku Shine *TSORON ALLAH* domin samun nagartacciyar rayuwa a tare dasu da kuma tarbiyya mai kyau._ _Daga lokacin da yaro ya fara wayo, ya fara magana, yasan abincin da zai sanya a bakin sa, ko kuma abin sha to daga wannan lokacin ya kamata ku fara cusa masa jin tsoron Allah a zuciyar sa sannan su San Wane ne Manzon Allah S.W.A, Menene Matsayin sa a Wajen Al’ummar Duniya baki ɗaya da Wajen Allah.._ _ku cusawa yaran ku jin tsoron Allah ta hanyar sanar dasu ubangiji, abinda yayi umarnin a aikata da kuma abinda yayi hani a kai.kamin ku jefa yaran ku a makarantar boko ku fara tura su ta islamiya, malamai magada Annabawa nayin nasu kuma kuna yin naku to insha’Allahu tarbiyar yaran ku zata zamo mai sauƙi a wurin ku a lokacin da suka balaga suka gama mallakar hankalin kan su._ _Sa’annan ku cusawa yaran ku son ilimi na addini dana zamani Kasancewar ilimi Shine Ginshiƙin Rayuwa, hakkin kune iyaye ku bawa ƴaƴan ku ilimi wanda zai amfanar da su duniya da lahira, ba ƴaƴan ku kawai ba hatta ku iyaye yana da kyau ku samarwa kan ku ilimi. Shi ilimi haske ne mai haskaka rayuwar ɗan adam ta kowanne fanni ba kawai don neman aikin abin duniya ba..wanda mafi akasarin iyaye yanzu sun fi gina ilimin ƴaƴan su akan neman aikin abin duniya duk da cewar hakan ba laifi bane amma ya kamata mu nazartu muyi duba sose akan hakan, muyi faɗi tashi mu jajirce mu cije don ganin mun inganta rayuwar ƴaƴa da ilimi na addini domin da shine za’a tafi lahira saɓanin na duniya da inda muka same shi anan zamu bar shi._ _Sose muke tafka kuskure a rayuwar yanzu, an cusawa yara musamman mata son abin duniya, ku farka iyaye musamman iyaye mata, kin cusawa ɗiyar ki son abin duniya, kin cika rayuwar ƴar ki da burin abin duniya, kin ƙawata idanuwan ta da hangen abin cikin duniya an manta da mutuwa na tafe a kowanne lokaci. fatan ki, burin ki, mafarkin ki, jin daɗin ki, kwanciyar hankalin ki, tayi-tayi ta gama Secondary School ta Shiga Jami’a tayi degree tayi Masters Domin ta tara Muku Dukiya kuyi kuɗi duniya tasan da ɗiyar ku ko ɗan ku, ku huce takaicin duniya, hakan yana da kyau kuma ba laifi bane sai dai ta gefe guda a kwai illa, akwai matsala._ _Duk saboda wannan burin kun hana ƴar’ku aure, baku sashi a cikin lissafin da zai inganta rayuwar ƴar’ku, terming ɗin ku da terget naku shine kawai wancan duk saboda kada burdget naki ke uwa ya rushe (ga wasu iyayen). Shin idan anyi auren nan ba’a karatunne?, shin idan anyi auren nan ba’a aikinne?, shin idan tayi auren nan zai hanata dukkan muradin ki da kike son ya cika?. Kin Hanata yin Aure, ƴaƴayen mu ba duwatsu ba, b marasa lafiya, sha’awa na Damin ta, Samari kullum kawo mata hari suke, koda yaushe tana tare da su a makaran ta ko a waje, yau da gobe sai Allah ba fata ake ba, Allah ya tsare mu ya tsare mana ƴaƴayen mu._ _Mu riƙa kai zuciya nesa a kan yaran mu, duka da hantara da zagi da mummunar kalma basu zasu gyara yaro ba face ƙara lalata shi, ku dinga yawan yi masu adu’a a koda yaushe, kar ku faɗi kalma mara daɗi a kansu a lokacin da suka ɓata maku rai, don Allah iyaye mu iya bakin mu akan yaran mu, kar mu manta matsayin bakin mu akan su, fata na gari da adu’a ta gari a kansu shine dai-dai.._ _ku koyar da yaran ku da sabar masu yin sallah akan lokaci, ku koyar dasu adu’oin neman tsari da kariya kamar yanda ma’aiki ya koyar damu, ku zama masu lura da irin fina-finan da suke kallo domin kuwa shima kallo na ɓata tarbiyar yaro ya rusa duk ginin da kayi a baya, ku sabar masu da sauraran wa’azi kamar yanda ya kamata bakin ku ya saba wajen yi masu wa’azi._ _Haka Zalika ku kasance abin koyi ga yaren ku, kuyi ƙoƙarin aikata abu mai kyau tayanda zasu gani su ɗauka daga gare ku.. Ku zama masu zama da yaran ku kuna shiga cikin su domin jin matsalolin su, sannan ku zama masu sanya ido a duk abubuwan da yaran ku ke gudanarwa na yau da kullum tun kama daga kan ƙawaye, lura da irin abokan da yaro ke mu’amala dasu yana da kyau matuƙa da gaske, kuma hanya ce ta kiyaye yaron ki daga faɗawa ga miyagun abokai, idan har kun sanya ma yaro ido akan abokan tarayyar sa lalle tabbas zai ji tsoron zama da ɓata gari, zai yi duk yanda zai yi yaga yayi ƙoƙarin nisan ta da banzan abokai, fatan mu Allah ya kare mana zuri’a ya kuma shiryar dasu._ _mu guji kuma mu kiyaye bama ƙananun yaran mu da suka tasa wayar hannu, wannan waya da muke ganin ta haƙiƙanin gaskiya ba ƙaramar musiba bace, haɗari ce babba ga rayuwar ƴaƴa wallahi, don haka mu kiyaye basu waya musamman ta android a lokacin da suke da ƙarancin shekaru…. Ku zama masu sanya ido a kan shige da ficen ƴaƴan ku musamman ke uwa da kike zaune cikin gida koda yaushe, ba kowanne wuri ya kamata ku bar yaran ku suke zuwa ba, kuma ba’a koda yaushe ya kamata kuke barin su fita ba, duk da cewar rayuwar yanzu ta sauya yaran mu sunfi mu wayo da dabara… Idan dama ma da hali duk sanda ƴarki mace ta buƙaci zuwa wani wuri kiyi mata jagora, sannan ki hani yaran ki tarayya da ƙawaye barkatai._ _yake uwa ki zama mai sa’ido sosai da sosai akan ɗiyar ki mace wajen duban irin littafan hausa dana turan ci da take karantawa, ki tsoratar da ƴar’ki kiyi mata barazana da karanta littafin daya kauce hanyar kunya da tarbiyya, haka zalika idan ƴarki ta taso da sha’awar rubuta littafi shima ki tsoratar da ita ki mata baraza na ta yanda zata ji tsoro ta kuma kiyaye rubuta abinda ba shi da kyau, ki tunatar da ita cewa lalle ubangiji zai tsaida ita akan abinda ta rubuta, ki zama mai bincikar wayar ta akai-akai, ki zama ƴar jarida ga yaran ki, kisa musu ido akan duk abinda zasu samu, bi ma’ana dukkan abinda kika gani a hannun su ki sasu gaba ki titsiye su don jin daga ina suka samo shi?, taya suka same shi?, koda yaro zai ce maki ga wurin daya samu kuyi ƙoƙarin bin diddigin inda ya same su ɗin… Karku sabarwa yaron ku da riƙe kuɗi domin kuɗi na ɗaya daga cikin abinda ke rusa tarbiyar yaro._ _yake uwa ta gari, ki sanya ido akan fitar ƴarki daga gida wajen sanya sutura, ki tuna musulunci ki tuna faɗin Allah maɗaukakin sarki a cikin littafin sa mai tsarki mai girma, ki tilastata ki sabar mata da suturce jikin ta a yayin da zata fita… Idan mai sanya hijab ce ki sanya ido wurin ganin kayan data sanya aciki da kuma abinda ke ƙunshe cikin jakar hannun ta, domin wasu ƴaƴan namu kan yaudare mu da fuska biyu.. Ki hani yarinyar ki da amsar kuɗin hannun samari, ki kuma hani yaran ki da saurin miƙa hannu, ki hani yaran ki da kwaɗayi da son abin duniya._ _ya ku iyaye na gari, daga lokacin da kuka fahimci ƴaƴan ku na buƙatar aure, lalle kuyi gaggawar yi masu, kuyi gaggawar yi masu, kuyi gaggawar yi masu, hakan shi zai hana yaɗuwar ɓarnar dake faruwa a doron ƙasar mu, ba komi ke jefe ƴaƴan mu cikin baƙincikin rayuwa ba sai wajen tauye masu hakki da muke, musamman ƴaƴa mata, don Allah iyaye da zarar kun fuskanci ƴaƴan ku na son aure kuyi masu domin shine mafita kuma shine kariyar su daga faɗawa mummunar halaka, kuma shine yayewar damuwar da za’a shiga a gaba._ _Daga ƙarshe karmu manta zamu cimma kyakykyawan burin mu ne akan tarbiyantar da yaran mu wajen yawan tunsar dasu faɗin Allah da Ma’aikin Allah._ _Ya Allah kasa mu dace, Allah kuma ya bamu ikon sauke hakkin ƴaƴan mu da Allah ya ɗora mana domin Ƴaƴa Amana ce Allah ya bamu._ Daga *® MATSALAR FYADE GA “YA” YA MATA…. KALUBANE GA IYAYE…… idan kacire yara kanana wayanda basusan fari da baqi ba wallahi sauran yan matan wasu lefinsu ne Dana iyayensu saboda gurbatar tarbiyya. Akwai Hadith na manzon Allah (saw) annabi yake cewa …. Sayaqulu fi akirizzamani nisa’un kasiyatun ariyatun. Sai annabi yace il anu hunna fa inna hunna mal ulatu, subhanallah sai yasake cewa wallahi lajidanna rihal janna, alhalin wa inna rihaha la yujadu min masiratun kaza wa kaza. To gaba daya inka duba babban matsalar wannan zamanin yanzu shine wayewa tayi yawa haka kawai yarinya takai mace iya mace Amma saita bata wasanta. a farkon fari duk bikin daza ayi saitayi anko karasa a gidan ubanwa take samo kudin Kuma dinki me daukar hankali, kaga yarinya kullum bakinta abude washa da haqora farare tass tana sheqa dariya me daukar hankali, tana tafiya tana bada style kala kala, ko makaranta zataje saita qwalqwale jiki tayi wankan siga ana tafiya tsaraici yana fita kuma wallahi iyayen suna kallo su aganinsu lokacin wance fah yayi abarta kawai taci duniyar ta ai ansan dai tunda tanada kyau Dole a aureta. To wallahi muddin diyarka ko diyarki tana irin wannan tsiyar karma gayu su afka mata kayi kumfar baki tayi suka mayar tunda dayawanku aurenma in anzo sai kuce tafara level 100 saita kammala tukunna kokuma kuce mutum yaje saiya yi gini ku bakwason haya, kokuma kuce adaidaita yake ja bazai iyaba, ko ace waye babanka daga kace malam halliru me kwado da linzami za a durama ashar akoreka. kai wallahi wa tama kidan jogo zatabi takai kanta ayi mata shi Amma daga baya sai iyayen su juya kaset din suce ai fyade ne. Dabara taragewa iyaye kuyiwa yayanku tarbiya kuyimusu aure da wuri in ansamu fitacce kunga dai auren annabi (saw) da nana Aisha Kuma ahanasu kwadayi Adena Dora musu tallah. Allah yakaremu da zuriyarmu daga dukkan sharri amin amin.

YARANTA DA SON SUCIYA NA YAN SOCIAL MEDIA

BA’A ADDINI DA SON ZUCIYA !!! Ana addine da abinda yazo ashari’a Shi Hidimar Addini ba irinta Siyasa bace. Dan Allah idan baka saniba kadaina kutse acikin lamarin. Bana jin dadin irin wadannan abubuwan da mukeyiwa juna, Wallahil aziim idan wadanda ba musulmiba sukaga irin wadannan Musanya da Cin mutuncin da mukeyiwa junan mun, dadi sukeji. Idan kasan baka da ilimi awani zancen daka tsinkaya a Audio, na lamari addini ko A social media kada kace zakayi Raddi direct. Nasan baza ka rasa malamin da ka yadda dashi ba ayankinka, kamata yayi kaje ya warwarema lamarin, inda kuskuren yake saikayi Contact da mai Wannan jawabin. kuyi magana ta fahimta dashi Agunsa zakasami karin bayani, daga nan sai ka sam hujja. Haka ake magance mummunar zance kuma in yanada kuskurema me iyuwa ya koma kan wannan jawabin nasa yayi gyara kokuma ya warware abinda yashigewa duniya duhu. Wannan zai zamo ka kawar da barna, in barnanne inkuma rashin fahimtace To kaga kaima kasami Sabon ilimi Dan Allah Mutane mudunga kyautatawa junan mu zato. 📝#Dan_Arewa

MATSALAR TSARO A NAIJA new post 1

BABA YAKASA MATASALAR TSARO AKASATA

Leave the issue that he has doing well kawai muce Baba yakasa. Abin na Bu’katar Tunani ne. Idan zamuyi adalci wa kanmu kuma mufadi gaskiya, Wallahi matsalar tsaro a nigeria, kasawar kayan aikin Jami’an tsaron governati ce. bawai ina nufin bata da karfin yaqarsu ba, kawai taki tayi abinda yadacene dan ganeda lamarin. Tahanyar nazari dakuma bawa jami’ai kayan aiki dakuma da nauyi da bada tallafi ga iyalin duk wanda yarasa Ransa akan yaki da ‘Yan ta’adda. Kullum al’amuran kara rikicewa yakeyi, Tambayata anan itace: Waishin su ‘yan ta’addannankam aljanune, kokuma aljanune suke basu kayan aikine. Wadanda dasuke amfani dasu, Kama daga ci shansu har zuwa makamai dasuke amfani dasu, dakuma man da suke sakawa a ababen hawansu. da’akwai alamar tambaya anan gun! Shin anya acikinmu babu masu daukan nauyinsu? kokuma makiyanmu ne ke basu mafaka da tallafi? Idan akwai kuwa suwaye wadannan mataimakan nawu? Kuma a ina suke? Are the citizens of nigeria? Or they are in another countries? Shin nigeria anya batada makiyan boye na cikin gida da waje? In akwai to suwaye kuma a ina suke? Amsar wadannan maganganu nawa suna nan acikin wannan kalmomi guda uku. #BABA_A_BINCIKA Gadai ni abinda na bincika da kuma hasashen tunanina. Dafarko dai ina zargin Turawan yamma, bisa wasu kwararan dalilai guda biyar ( hudu ) danganeda dambaruwar dake faruwa a Arewa ( daya ) kuwa danganeda abinda ya faru na End Sers a kudu, ga dalilan kamar haka. 1. Kungiyoyin da addancin da ake jinginasu dasunan Musulmi, wadanda kuma ayankunan Musulmi suke. tayadda suke kashesu suna kuma korarsu daga gidaddajinsu. Idan musulmin gaskiyane ba dan gwangilaba, abinda zasuyi koyi dashi, shine Alqur’ani da hadisan manzon Allah. A alqur’ani da hadisi abinda ake nufi da hakikanin jihadi shine, yada addinin musulunci. Kuma ni naga arewa mafi yawansu musulmine. Idan gaskiyane kudanci ai shine guri mafi karancin musulmi, dan me ba’akai Jihadin can ba? Amsa Sharrine na turawan yamma inda suke amfani da masu raunin addini, suna ida nufinsu domin su samu damar samun hanyar shiga kasarmu. Nazari Duba abinda yafaru akasashen Gabas ta tsakiya, danganeda larabawa Sunnah, da kuma Sauran Qabilun Shi’awa, na yanki Fakistan, Iran da Iraqi .da kuma Cecenistan, Afghanistan, Dimashqi, dakuma wasu yankuna na Syria (Shaam) dama sauran kasashen na gabas ta tsakiya. Suma turawan yammane sukayi amfani dawasu bangare masu rauni acikinsu na (‘yan ta’adda). Suka wargaza kasan sa’annan suka lalata Arzikin dake cikinta, har wayau kasashen dukkansu alalace suke. Misalin kamar irin ta nigeria ce, suma daga rikicin kabilaci suka fara, saikuma rikicin yanki, akazo rikicin Aqeeda, daga karshe aka dawo dana yanki, har izuwa yau bala’i suke kan Tafkawa akasashennan nasu. 2. Dalilin na biyu dayasa nake zargin turawan yamma shine; Kashe maluman addinin musulunci da Pastoci masu gaskiya da akeyi, akan don suna wayar wa mutane kai dan ganeda Sharrukan yahudawa, Duk wanda yake karanta Bibble ko Qur’ani yanajin yadda Allah yake kiran yahudawa, dakuma zarginsu, akan sauya Littafi dakuma Nuna finkarfi da zalunci akan mutane. Acikin Alqur’ani Allah yanuna mana haqiqanin kiyayyar da sukeman dakuma son mallakar duniya, dasuke so akanmu da mamaya. yadda Allah yake cewa (s.w.a). ”Bazasu gusheba suna yakarku Tako wata ‘bangare harsai kun Ridda kunbar addininku” Wa’iyazu billah kokai Christa ne, kasani kaima basu barkaba inda suke batanci akan Nana Maryamu (Mary). dakuma sukarta da Qazafin zina, da kuma kisan gillah dasukeyiwa ‘Yan addinin Christa kafin zuwan Hitla. Wallahi matsalar duniya ayanzu sune yahudawa Allah kayimana maganinsu. 3. Dalili na uku kuwa shine: yadda ake ayyana wasu wadanda sune jigogin nigeria ayanzu Cikinsu harda Ministan Sadarwa da Tattali ta kasa watau Isah Ali Ibrahim fanmi. Ana ayyadasu amatsayin wadanda za’a hara nan gaba. tareda hallakasu da karyar ta’addanci kamar yadda yafaru awadancan kasashen, Na gabas tatsakiya, inda akatabin masu hikima da fasahar tsaro da tattalin arzikinsu akayi ta kashewa, da sunan yaki da ta’addanci. 4. Dalili na hudu kuwa shine Yadda ake samun makamai ahannun ‘yan ta’addan Nigeria: har yana fin na Jami’an tsaron governati. Wanene ke bawa ‘yan ta’adda makamai haka yadda kasan ba aduniyarnan suke samuba. To Wallahil Azim koda Aljanune suke basu inbabu Munafinci da Gilli da Tuggu. Wallahi za’asan Suwaye. Wadanda ke basu makamai. Masu basu kuwa sune ‘yan world totalirial government. kuma sune wadanda sukeson ahada duniya karkashin mallakin Mulki guda. Wadanda suka sha Alwashin gamawa da dukkan wata Al’uma dasuke ganin zai kawo musu cikas, gurin cimma burikansu na mulkan duniya. Domin a imaninsu shine babu wata rayuwa bayan ta duniya, balle sakamako yabiyo baya. Tayadda suke anfani da ‘Yan ta’adda dakuma salon tsarin ta’addanci, da babu irinsa kamar kirkiran gungiyoyin Shan jini, dakuma na Zubaddda jini. wato kashe halittu abayan kasa, tahanyar amfani da makamai, da kwayoyi, dakuma ma abubuwan ci, dana sha, harda suturar sakawa dakuma iskar damuke She’ka. Kuma wadannan Mutane Sanannune aduniya. kuma suna da Cibiya tasu Me zaman kansnta. inda suke Aiwatarda munanan manufofinsu, kama daga Mulkin mallaka, dakuma sa baki aharkokin tsaron kasashen duniya. Wadannan kad’an kenan daga cikin kananan Burikansu, kafin manyan su bayyana dakuma cikar ‘Kudirinsu. Muna rokon Allah yakarya Wannan daula, yakuma wulakanta mambobinta gaba dayansu. Allah yadirkakesu yataimaki bayinsa Nagari. 5. Dalili na biyar kuma na karshe a dalilaina daga cikin wadannan dalilan Shine. Faruwar EndSers dakuma wanzuwa da tasirin da sukayi a Nigeria. ayankin Kudancinta, Sun yi tasiri wajan Illata muhallan wasu, da Shaguna, da kwantina, da kona kone. Hakika babu shakka masu wadannan mummunar manufa, sunada wakilansu akowace kasa, inda suke amfani dasu, Su hura wutar rigima da tashin hankali, da Hatsaniya tareda tallafawa wani sashi acikinsu. Da taimaka musu da makamai kamar dai yadda yake faruwa. Hakika Sunyi abinda sukayi na Zalinci. Harda suka kuma kara ingiza yan Arewa suma su motsa. Sai kuma Allah yasanya musu saukin rai. tareda nuna rashin yarda domin ‘bata kasane. Ahakikanin gaskiya gidajan juna muke rusawa, kuma masana’antun ‘yan uwa muke konawa kuma illar mu zata shafa, tayadda daga baya zamuzo mu ciza yatsa, muyi Allah wadai da Lamarin Mu da kanmu. Idan da Za a kama rikicin a Arewa dakuwa Sabuwar masifa ta kara aukuwa acikin kasa. daga nan sai sukawo tallafin magunguna da abinci. Muna Ci muna Mutuwa. Ga matsalar tsaro kuma, Sai su kawo Jami’ansu na kungiyar World totalirial goverment. Za’a kawosu suci gaba da kashemu dasunan yaki dayan ta’adda. Har awargaza kasanmu kamar yadda yafaru agabas ta tsakiya. Kuma sunfara da al’umar Musulmine domin musulmi sunfi yasa. Kuma sunfi karfi. Amma idan sunjiyo kan kawo zasu afka. Don haka #Mukula. Nigeria maza da mata manya da yara Christians and Muslims ayi hattara. # Qaalu_Bale_garemu Muyita Rokon Allah yakawo mana mafita Amma saina gyara ka gyara Mun gyara Kun gyara Sun gyara. Allah yakaremu, kataimakemu da gyara.