KUJI TAUSAYIN MARAYAN ALLAH

Bansan me Nayi mussu ba
Nufata da Sharri suke basu barniba

Nayi kukan Zuciya
Har na Ido Hawayena Basu fad’i ba

Ganinan na Sarqafe
Igiyar suce Suka ya’ban nashiga fargaba

Ba Mai Karni Ni
Inhar JALLAH bai Qadarinsa akaina Ba

Zasuyi dana Sani
Biyar Dasuke fatansu Bazai Cini ba

Natashi Da Safiya
Qadarin gobe Bazan Sanshi ba

Tafiyar Tayi Nisa
Garin danaje Basu Sanni ba

Nasamu Masauki
Agidan danake Ba’aso Ganina Agefe ba

Suna So Muyi Fira
Kuma Zancena Bazasu Suqi Jinta ba

Gareni Sun Tako
Mararina Suke Kullum basu Barniba

Ya Rabbi Ka nufa
Gani Zamanin da ake Gudun Mai gaskiya

Ya Mai Raya Rayayyen Marayan Daya Rayu Cikin rayuwa da Ruwayar Maruwaita Rayayyun Ruhi da Ra’ayin Ribar Rabauta A Ranar Ramawa Ramammun Ruhanan da suka Rayu Cikin Ramawa Rayayyen Rai Ra’ayinta Randa Ba’a Raina Rukunin Ribatar Raunin Ruwayar Rayayyu.

Ismail Hussaini Adam

Alpholtawy

JAWABAI MUHIMMAI

TARIHIN SAHABBAI 001

TARIHIN SAYYIDINA ABUBAKAR SADDIK ALLAH YA YARDA DA SHI,

(manzon Allah S. A. W) “yace ya Abubakar kai ne farko wanda zai shiga Aljanna daga al’umma ta”

Sayyidina Abubakar shi ne Abdullahi dan Abu kuhafatu ” usman” usman dan Amir dan Amir dan ka”abu dan sa”adu da taimu dan murratu dan ka”abu dan lu”aayu, bakuraishe. Bataime. Nasabarshi ta hadu da manzon allah ta wajan murratu dan ka”abu kakansu na biyar. Sunan shi a lokacin jahiliya “Abdul ka” aba” daya musuluta sai manzon allah ( S. A. W) yakara shi “Abdullahi” An yi mishi alkunya da Abubakar saboda riganyenshi wajan dabi”antuwa da kyamara halaye. Kuma an yimasa lakabi da saddik sabo da saurin bayar da gaskiyar shi ga dukkan abunda manzon allah (S. A. W) ya fada kuma manzon allah (S. A. W) yakara shi da “Atiku” shine mutumin da yafara musuluta a manyan. Shi ne mutum na farko, da ya fara kira zuwa ga addinin musulunci. Bayan manzon Allah Annabi Muhammad (S. A. W) shine yafara haduba a addinin musulunci. Shine abokin zaman kogo tare da manzon Allah na farko kuma shine nafarko cikin sahabbai goma da aka musu albishir da gidan Aljannah tun a duniya shine farkon Amirul hajji kuma yana cikin marubuta wahayin da akema Annabi Muhammad (S. A. W) An haifi Sayyidina abubakar (R. A) a makka bayan Shekara giwaye da shekaru uku (573 A. D) manzon Allah. Ya girma shi da shekaru uku. Yana cikin manyan shuwagabannin kuraishawa a lokacin jahiliya kuma a bakin manzon allah ne na kasa tun kafin aiko shi. Sau dayawa ma. Yakanje gidan shi su tattauna shine mafi sani duk larabawa game da tarihin nasabar kuraishawa. 
Kuma yakira mutane da yawa zuwa ga addinin musulunci. Biyar daga cikin su suna cikin sahabbai goma. Da aka yiwa bishara da Aljannah sune kamar haka :  
Ya sha a zaba iri – iri daga kafiran makka saboda shigar shi musulunci 
Har takai babu wani musulmai da azabtu kamar shi. Duk da irin matsananciyar azabar da suka sha suda sauran musulman farko daga kafiran makka. Bai yi kauraba zuwa kasar habasha ba. Ya tare ga manzon allah (S. A. W) lokacin kaura zuwa madina yana tare da Annabi Muhammad (S. A. W), tare suka shiga kogo kafin suwuce zuwa madina shine cukon mutane biyu da Allah ya ambata a alkur”ani in da yace : ” Idan baku taimakeshiba. ( Annabi), to ai Allah ya taimake shi yayin da kafurai suka fitar da shi ( daga makka) na biyu (mutane) biyu yayi dasuka shiga cikin kogo yake cewa da abokin shi (Abubakar)” kada kaji tsoro, Mu Hakika Allah ya na tare damu “( da taimako shi)” cikin suratul tauba:40, yayin da suka isa madina. Sayyida Abubakar, A wurin kharijatu dan zaidu. Da shi kuma manzon allah yahada su ‘yan uwantaka yayi da ya rinka hada yan’ uwantaka (ta musulunci) tsakanin mutane makka ( muhajiruna), da na madina (Ansaru) Sayyida Abubakar shine tamkar Waziri ga Annabi Muhammad (S. A. W), wajan gudanar da al’amuran daular musulunci. Mai babbar hedikwata a madina: birnin manzo,,,

Abubakar saddik ( R. A) ya dukkan yake _ yaken daukaka musulunci da yada shi da Annabi Muhammad (S. A. W) a yakin badar shine kan gaba wajan kula da wurin da manzon allah yake. Yana shir yanda yake zai gudana tare da rokon allah. har dai allah ya amsa addu’ar Annabi, ya aiko da rundunar mala”iku. Musulmai suka samu nasara. A yakin uhudu kuwa, Sayyida Abubakar. Shine jagora tsirarun Manyan sahabbai, suka gabata a filin yakin. Tare da manzon allah (S. A. W) yayin da kafurai suka tarwatsa rundunar musulmai.

Bissalam

Continue reading

INGANCIN ZUQATAN BAYI

INGANCIN ZUCIYA!!! ***************************************** Hakika gyaran zuciya itace maqasudin kar´bar aiki. Da Akwai Ayoyi da hadisai ingantttu dake nuna jinjina ga ayyukan bayi amma dukkansu suna yabawane akan tsarkin zuciya domin shine (sababin karbar aikin). Hakazalika. ibadar da Allah yafisoma, ~Maqasudinsa zuciyace watau (Azumi).

Shi Azumi ALLAHﷻ (s.w.a) Shine kadai keda hakikanin gasgata maiyinsa, Saikuma Zuciyar maiyinsa, Sa`annan kuma ma ALLAHﷻ shi da kansa yake cewa yana son masu tuba damasu tsarki Ma´ana masu tsarkake zuciyoyinsu daga bari munanan ayyuka. Da ayyukan da aka kyamata. Gashinan in arabic text إن الله یحب التوابین ویحب المتطهری Manzon ALLAH ﷺyana cewa إن فی الجسد مضغة إذا صلحت صلح الجسد کله وإذا فسدة فسد الجسد کله علی وهی القلب Arufai kuyimin afuwa nai muku Shisshigi inda kuskere atusaddani. Dan Adam ajizine ALLAHﷻShine masani. dafatan anyi Juma`ah lafiya

AREWA 24 TAMUCE

AREWA 24 TAMUCE
Faduwar Dalibai A Jarrabawar JAMB

   Sau dayawa harda wasu acikin Malamai na ta fadar cewa Kallon Shirye_Shiryen Film Series. Sune Silar Faduwar Dalibanda Sukayi JAMB A bana 2021.

Daga Alqalamin ✍️Ismail Hussaini Alpholwy

@MatanasanMarutanBauchi

       Sabanin Ra’ayi danganeda Fahimtata dakuma Wadansu damuka tattauna akan batun awani ganawar damukayi ta Online da ‘Yan uwana marubuta.
A iya fahimtarmu bakawai Kallon series bane yakayarda Mutane a jarrabawar bana ba. Duk da Cewa yana daya daga cikin abubuwa uku acikinsu. Sune Kallan film, Yawan Sauraron kida, dakuma Wasannin Wayar hannu (Games)

  Wadanda dukka wadannan abubuwa suna Faruwane ta cikin wayoyin hannuwan mu. Yadda zakasamu Mace ko na miji yana da Game Apps Sama da Goma Sha ga kuma Film Series Suma Sama da Ashirin Ga kuma wakoki na Hippop dama Jazz Music dana Hausa dama na Turanci dana Kudanci Hardana Videos na Fitsara da Lalata Tarbiyya.

   To taya yaro zai dau littafi yayi karatu, bacin ga irin wadannan Shirmen da lalacewan acikin wayarsa. Dasu zai kwana kuma yatashi kuma ba akoyar dashi Tsoron Allah ba.

   Laifin iyayene dasuke sakaci da Wayoyin Yaransu dakuma Yaran dasuka taso Basu bibiyar kafafen Alkhairi acikin wayoyin dakuma Social Media.
Dolene Mu kame daga barin abinda Zai Cutar mana da imaninmu dama Kuruciyarmu gaba daya.
Burin Turawan yamma akoda Yaushe Shine Muzama Malalata Mukasa komai Sai sun mana.

     In iyayenmu basu ankaraddamu  ba wataran Za’a iya wayar gari bazamu iyayin komaiba, Sai abinda Turawa Sukaso suyi damu, domin anriga da makara komai ayanzu nasu ake kwaikwayo. Anmanta da Cewa akwai Tsarin Rayuwa Islamiyya dakuma Christianity. Duk abinda Yahudu Sukazo dashi Shine Ake bi.

    Idan da wasu iyayen Zasu duba Profile na Socil Media na Yaranau Musamman Facebook da Twitter dakuma Istagram da Tictok Wallahil Azim sai sun farfasa Wayoyin Yaransu. Yin hakan kuma abanza ne. Don zai je ga na Abokansa.

      Mafita garemu Shine Adasawa Yara Tsoron Allah Acikin Zuqatansu kawai tahanyar Nasihohi da Addu’ar Shiriya domin Tafiya tayi Nisa. baza’a taba iya Hanasu rike wayoyi Dukansu inma babu ahannun wancan akwai ahannan wancan kuma Munsan Cewa ba’a Rowan Wuta. in aikin Shedancine kana Zaune za Akawomaka, kuma ba aganin Tsadarsa domin Akan iya Sayan plartform domin Series Film Amma daukar Nauyin Tafseer kuwa Sai cikin Azumi.

Domin Allah iyaye Akoyar da ‘ya’ya Tsoron Allah, Allah yakawo mana mafita Arayuwa.