AHLUSSUNNAH MUFARKA

DA’ACE KISHIN QUNGIYANCIN MU NA ADDINI NE DA MUN WUCE HAKA ACIGABA

      Ahlussunnah Mufarka
Jiya kotu a Kaduna ta wanke Amirul Jaish na rundinar shi’ah (IMN) Ibrahim Yakubu Zakzaky daga tuhumar da Gwamnatin jihar Kaduna ta masa, biyo bayan abinda ya faru a Gazwatu Hussainiyyah Zaria da sojojin janar Buratai a 2015
Ni abinda na fahimta lokacin da Gwamnati ta gindaya masa ne kawai yayi ta sakeshi da kuma tasirin da Zakzaky yake dashi a cikin wannan Gwamnatin, amma ba wai don ta rasa hujjar da zata cigaba da tsareshi ba
Sannan bayan matakin da kotun Kaduna ta zartar, har ila yau inda ace Gwamnatin Kaduna tana da niyyar cigaba da garkame Zakzaky da tayi hakan ta hanyar daukaka kara a kotun tarayya dake Abuja, kamar yadda dokar kasa ta tanadar
Zakzaky yana da manyan mutane a Kasarnan wanda suna da tasirin da zasu iya nema masa alfarma har a gurin shugaban Kasa, idan baku sani ba Zakzaky yana da Manyan Ministoci har guda biyu a cikin wannan Gwamnatin wanda a baya har muzahara suna fita kafin a kafa Gwamnatin Buhari a 2015
Gareka Musulmi Ahlussunnah, ka sani cewa ba ruwan Gwamnatin Nigeria bane ta yaki wani mutum saboda yana dauke da akidar da ta saba da ra’ayinta, shi tsarin kundin Constitution da yake rike da tsarin gudanarwan Kasa, fada ma yake da kowace irin akida ta Musulunci
Duk abinda ya faru da Zakzaky bai da nasaba da addini ko akida, zallar siyasa ce kawai, zargi ne marar tushe da ake cewa Kasar Saudiyyah cibiyar Ahlussunnah tana da hannu a abinda ya faru da Zakzaky
Jama’ar Musulmi da muke kiyayya da shi’ah ku sani cewa akwai babban kalubale a garemu idan bamu gyara, yawan da muke dashi ba zai taba amfanar mu ba, Ya ku Ahlussunnah me zai hana kuyi irin tsarin da Zakzaky yayi har ya samu karfi da kuma tasiri da ya mallaki manyan wakilai da yake dashi a kowace ma’aikata a Gwamnatin Nigeria?
Shin Ahlussunnah kuna da tsarin da kuke daukar nauyin karatun matasa masu fikra da basira a cikinku suna zuwa Kasashen turai suna karanta Medical Doctor, Pilot, Nuclear Physics, Astronomy, Mechanical Engineering, International Law, Computer Science, Ethical Hacking, Cyber Security da sauran fannonin ilmi masu tasiri a zamani kamar yadda Zakzaky yake yi?
Shin Ahlussunnah kuna da tsarin bangare a cikin da’awar Sunnah ko kungiyar Sunnah da yake da bangare na Likitoci Ahlussunnah, bangare na Malaman makarantar boko tun daga Primary har University, bangare na jami’an tsaro, bangare na siyasa, bangare na ‘yan kasuwa, bangare na ma’aikatan Gwamnatin tarayya da na jihohi da kananan hukumomi kamar yadda Zakzaky yake da wannan tsarin?
Ahlussunnah ba mu da wannan tsarin ko guda daya, an bar Ahlussunnah a baya, an bar Ahlussunnah da yiwa juna raddi da hassada, abinda ba za’a taba samu ba kenan a cikin da’awar shi’ah a Nigeria, idan kunga bangaren RAAF suna sukar IMN Taqiyyah ne, manufarsu daya ce
Tsarin da Zakzaky yayi ba shakka idan Allah Ya bashi tsawon rai sai ya kafa Gwamnatin shi’ah a Nigeria, domin Billahi yayi kafuwar da ya wuce tunanin duk wani mai nisan tunani, na rantse da Allah inda ace da’awar shi’ah abune mai kyau da na jima da zama ‘dan shi’ah, kuma da yanzu bana Kasarnan saboda girman gudunmawa da zan bayar a tafiyar, amma shi’ah ba abune mai kyau ba
Namu jagororin sun zama ‘yan duniya, sun fara nesanta kansu da da’awar Sunnah, tsarinsu ya koma irin na ‘yan duniya kawai, sun koma karya da yaudara da zakin baki, takaicin wannan abin yana matukar sanya ni kuka da zubar da hawaye
Halin da Musulmi Ahlussunnah muke ciki a yau ya kamata ya dinga hanamu bacci, ya zamto muna tunanin hanyar da zamu bi mu gyara kuskure domin mu tunkari abokan gaban mu
Yaa Allah Ka bamu mafita na alheri Amin Yaa Hayyu Yaa Qayyum
Daga Malam Datti Assalafiy

RAYUWAR MATASHI

YAN UWANA MATASA!!! MU KOMA GA ALLAH

Mu kula da Rayuwa Zata Kai Tabaro mu

  Rayuwar Matashi abin tausayine, Kana fama da Quruciya Ga kuma bakin Aluma akanka. Idan zaafadi Damuwar Aluma dubu, Kaso ´Dari Tara da Hamsin (950) Na Matasa ne.
Qalubale Garemu Matasa, Ban cire kainaba domin nima cikin Quruciya nake.
Tabbas Muna Fuskantar Qalubalen rayuwa daga ´Bangaren zamantakewa, Har da Ibada. Saidai Raunin zuciya kuwa ya danganta da Yadda mutum yataso, Wahala ko Qunci, Tarbiyya ko Akasin hakan (Garari), Riskar iyaye da Rai ko Tashin Maraici. Idan Kasamu yin Makaranta Fani’ima (Haka akeso) In MA bakasamu ba Kaidai kada Kabar Neman ilimin Addini Domin Shidin Yalwatacce NE. Ako Ina akwaishi Amma kayi Takatsan_tsan Maluman da Kake Saurara. KADA kabi Maison Zuciya.
Dukkan Wadannan Matsololin Rayuwa ce, Kirata Agaremu Shine, Mugane inane hanyar tsira kuma mecece mafita ta rayuwar mu, Ina Muka fito, Ina Zamuje, Me zamu Riska, Ina Tafiyar zata Tiqe?


MATASA BAYIN ALLAH NE✍️👇


Kada Mushagaltu da Rudin Rayuwar duniya, Ko kuma Yanayin juyin Rayuwa yasanya Mu ´Bata Rayuwar mu da Shaye_shaye, ko Taaddanci, ko Daba, Da zamaYan Iskan gari.
Mugyara Rayuwarmu tahanyar kaucewa hadarurrukan da Suka shafi aikata Munanan Laifuka, Mutuna Cewa Allah yake bada arziki, kuma Shike bada lokaci dakuma damar Amfanar Arzikin namu. Zamu iya tarawa ahanyar 'Barna (Haram) Amma mu mutu, bamu ciba kuma Hisabinta Nanan Akan mu. Zamu iya shiga Matsalar Rayuwa, Mugur´bata Rayuwar mu da Shaye_shaye ko garari Sanadiyyar wani, ko wata Mattsala, Mun manta cewa ga Allah za a koma kuma akwai hisabi, Shifa Allah ako ina Mukayi kuka Yana jinmu. Idan Ka Shiga Mummunar Hali Mu tuna da ALLAH. Sannan Mu dunga Yawan Ambaton Allah din kada Muce zamu Sha kwaya, ko Mu Kunna Sigari, Yi Hakan kamar An watsa maka Kashine ka Wanke da Kwata. ‘Barna bata Kawar da ‘Barna.
Mu waita yin Istigfari, Wata Qila Jarrabawace ta Yawan zunubin mu, Allah yakeso ya kankare mana. Allah ya yafe mana Yakuma ´Dauramu akan Shiriyar Addininsa, Yakuma Tseratar damu daga Tabewa da Halaka, Allah ka Albarkanci Iyayenmu, da Malumanmu, da Yayunmu, da Kannen mu, Damu kanmu, Wadanda Suka Rasu a Gafartamasu Musamman Mahaifina Allah kajikansa Da Rahama.
Sakon Barka da SALLAR ADHHA ( Eidin Layya) Kutayani Yad’a wannan Sa’kon.
daga ✍️Alqalamin Ismail Hussaini Alpholtawy

MATSALAR TSARO A NAIJA New post 2

MATSALAR MANYANMUNE!!

Matsalar tsaro A’kasata Fitowa ta biyu (!!) ✍️Ismail Hussaini Adam

Matsalar tsaro akasar Nigeria abune mai matukar wuya amaganceta da hanzari, Domin Al’amuran Sun jima Da Cakud’ewa cikin mummunar qaddara da muka samu kanmu aciki musanman Mu Al’umar Arewa. Ansamu akasi tahanyar wasunmu suna goyon bayan ta’addanci aboye, bincki da akeyi ana kin bayyana gaskiya, Shine babban Al’amarin daya gur’bata Al’amuran tsaro A’kasarnan. Wai sai ace anrufa asiri akwai ‘yan Alfarma.

Shifa d’an ta’adda, ko mai goyon bayan ta’addanci, Koda uwarsace data haifeshine yasan zata fallasheshi, Wallahil aziim zai aikata lahira, komai Son da takemai, balle jami’an tsaro ko Masu fad’a aji na gari Wad’anda aganinsu sune Cikas d’insu aharkar dasuke ciki. Yazama wajibi akan hukumomi, Da Shuwagabannin Al’uma ta ayyadar da hukunci, akan dukkan wani mai laifi data kama, takuma yi bincike akan dukkan wanda take zargi da ta’addanci, ko goyon bayan ‘yan ta’adda. Idan Tayi bincike inya tabbata kuma tazartar da hukuncin daya dace.

Hakan shine hanya mafi sauki, Ta hanyar da za’a gyara matsalar tsaro acikin Al’uma.

WANI ABINDA MUKA MANTA

Wad’annan masu laifi da’ake kamawa da sunan ‘barayin gida da masu fasa shagunan, Idan ba’azartar masu da hukuncin daya daceba Sune ake Sayansu Su girmama, Abasu Makamai sucigaba da ta’addanci dakuma Kisan mutane, haka kurum ba gaira ba dalili.

Dole ne acire maganar Alfarma, Dukkan wanda hukunci ta haushi kawai azartar masa shine adalci. Allah yafi kowa son bayinsa Amma yana hukumtasu idan sun aikata ba daidaiba. Tayadda yakema ‘Kona wasuma domin mummunar aiki dasuka aikata. Kuma yayi umarni garemu akan mu zartar da hukunci da adalci akan dukkan wanda doka ta haushi.

Hakika Al’uma tana shiga firgici da mummunar yanayine tahanyar sakaci da’akayi da hukunta masu laifin cikinta. A Nigeria mun sami kanmu cikin wannan yanayi tahanyar Sakacin hukumominmu da shugabanninmu.

RASHIN AIKINYI GA MATASA MA QALUBALENE

Matasa babu aikinyi a kasarnan dalili kuwa Shine, manyanmu basu kishin kafa wadatattun masana’antu burinsu gina gidaje kawai da zuwa ‘kasashen waje. Taya ‘Kasan wajen suka sami Cigabane Bayan samun nagartattun Shugabanni masu kishi Suna kula da hakkin Talakawansu. Yakamata Asamarda wadatattun masana’antu tayadda za’arage masu zaman banza dakuma yan Fasa ‘kwauri akasarnan. A’kasarnan akwai arzi’ki wanda yagirmi lissafi amma kuma munfi kowa Talakawa, wannan yasamo asaline danganeda Rashin tallafin jari da aikinyi ga masu ‘karamin ‘karfi, Saudadama wasu na fara kasuwanci amma da zarar sunsami karayar arzi’ki shikenan yazama abin tausayi. Mai iyuwa ma wanin daganan yakan koma goyan bayan ta’addanci, domin yasamu dukiya koma yazamo member na ‘yan ta’adda.

ANA ZALUNTAR ‘DALIBAN KARATU

Harajin karatu awannan kasa nada wahalar Gaske, ga kuma ana matukar Cin dunduniyar ‘Dalibai tahanyar mugayen Lecturers. Kai harda keta alfarmar (Mutuncin) ‘yan mata. A iya Saninmu ga Manyanmu na yanzu Shine. Sunyi karatune akyauta kokuma cikin sauki, Amma donme suke musgunawa Mutane ayanzu? Mafiya yawan malaman yanzu burinsu shine su samu kudi Suma a’kirgasu acikin masu Arzi’kin ‘Kasa. Bawai su bada karatu ga d’alibai ba kamar yadda yake a hukunce. Wannan yasa suke neman Kudi ido rufe a governati domin cimma burikansu dakuma kirkiro wasu tsaruka mabambamta. wadanda suke da rauni da Da’kushe har’ko’kin ilimi akasarnan.

Strike da ake samu a jami’o’i da Colleges yasamo Asaline daga, Son duniyar wasu daga cikin Malamai. Dolene Govrenati tasan hanyar da zata shawo kan Wannan Al’amari. Mutane na kashe kud’ad’e masu yawa kuma Suna d’aukan dogon Zango kafin su kammala karatunsu. Duk asadin matsalar Yajin aiki (Strike). Kuma akarshe yazamo Sun gama karatu kuma sun rasa aikinyi, Tambaya anan itace, idan mutum mai raunin imani yasha wannan wahalar kuma yarasa aikinyi, Me kuke tunani Zai biyo baya?

MATSALAR ASAMACE

Manyanmu na sama Sune ke morar arzikin ‘kasarnan. Manyan Nigeria mutum daya na d’aukan ma’kudan kud’i a governatin tarayya fiyeda Lissafin mai tunani Amma Nakasansu kuwa suna shan wuya matu’ka, Amma abinda suke samu ko na man mota baya wucewa, ballema aje ga Masarufi, dakuma Suturar jikki da kayan ‘Kawar ado. Don me corruption bazai Existing atsakanin muba Alhali wasunmu naci da gumin wasu. Su kuma manta da Hakkin dake tsakaninsu na zamantakewa. A’ka’idar Zamantakewa ta mususukunci dolene kasan Ci da Shan ma’kocinka Kamar yadda zakasan na Iyalinka.

Amma ayanzu babu ruwan wani da Wani, Anyi watsi da karantarwar addini anbi yahudu kuma gashi an’bace ba akamo yahuduba kuma Ambar Allah. Wadannan ma Suna daga cikin Hanyoyi mafiya girma na sanadin Lalacewar Tsaro a Nigeria. Zanci gaba Insha Allah. Allah ya tabbatar damu akan gaskiya da shiriya.

RAYIWAR YAN MATA

📝 QALUBALE GA RAYUWAR ‘YAN MATA ✍️ ******* GABATARWA *******

Assalamu alaikum warahmatullahi wabarkatuhu mai karatu.

Zanyi wannan rubutunne don nuni zuwaga yan uwana maza, domin kusan wa zaku auro ku kawo cikin gidanku, amatsayin abokiyar zama. Mata kuma su san dawa zasuyi qawance don gudun faďawa akomar halaka. Inda hali kutsaya kukaranta gabaki ďaya, domin zaka/zaki k’aru kuma inshaa Allahu zaku rabauta da waďannan zantuka nawa.

Ina bukatan addu’arku Allah ya haskaka qabarin mahaifina, dana mai karatu idan kuma suna raye, Allah yasa mugama dasu lafiya yakuma basu rabon cikawa da imani. Allah ka albarkaci rayuwar lahaifiyata da ayyukan alkhairi daku mumaďin gabaki ďaya.

‘YAN MATAN JAMI’A

Allah sarki rayuwarsu gwanin birgewane, saidai kuma abin tausayine awani bangaren, tayadda zaka samesu mafi yawancinsu akwai tsaftar jiki dana tufi. sannan sun san yakamata matuka, Saidai wasu acikinsu suna son yin aure kuma Suďin sun kame kansu. amma rashin dama takansa wasu acikinsu afkawa izuwa ga zina, Allah yakare. Hakan yana faruwane don rashin samun dama daga iyayensu. Zasu fidda gwani amma sai suce sam sai kin kammala karatu, sun manta da wasiyyar manzon Allah (s.a.w). Wasu kuma suna sheke ayarsune kawai tahanyar biyan bukatarsu ga maza, aduk sadda sha’awarsu ta motsa. Wasu kuma na fama da jimamin rayuwa tayadda suke fama da fuskantar barazanar lecturers lalatattu, da yunkuri batamasu tarbiyya da fansar jarrabawarsu da mutuncinsu. Iyaye ayi hattara zaku iya shiga wuta akan hakkin ‘ya’yayenku don rashin sadaukar musu da hakkinsu daya rataya akanku

‘YAN MATAN LUNGU

Idan akace matan lungu: sune mata masu talle akan titi, dakuma lungu da sashen unguwanni da sakokin ma’aikata, da shaguna (Kwantinan) kasuwanni. irin wadannan matan, idan basu sami kulawar tarbiyyaba sunfi kowasu mata sharri. Domin awani bangaren sukan ‘boye kamarsu suyi kama da mutanen kikrki amma sam bahakan bane azahirance. Kuma mafi yawanci acikinsune ake samun masu sace_sace, da bin maza bayan sunyi aure. domin sun saba da rike kudi masu kauri ahannayensu, ayayin budurcinsu. Hakazalika wasu acikin sunma suna saida budurcinsu kafin aure, a son zuciyarsu kokuma ara’ayin iyayensu mata. Ko uwayen goyensu na bariki. tayadda sukan taradda wulakanci agun mazajensu, dalilin rashin budurci bayan sunyi aure, hakan yake tursasu fita karuwanci bayan aure, ko sata wa mazansu na aure.

‘YAN MATAN BARIKI

Irin wadannan matan basuda mutunci. wanda su kansu sun yadda da hakan, kuma suna iya furtawa da kansu cewa su marasa kunyane amma daga fitsararrun cikinsu. Irin wadannan matan sukan tasone aguri mai lalacewar tarbiyya.

A gunda iyayensu ke zaune babu tarbiyya kuma iyayen basu kulawa da tarbiyyarsu. kuma babu addini agunda suke zaune. Saidai holewa da sha’anin duniyanci dakuma ta’ada, da muta kabbaranci. Ga uwa uba rashin dattako don ko waye ‘yar bariki zata zaki asalinsa ko da kuwa shugaban unguwarsune ko sarkin gari. Wadannan matan ko acikin garine shigarsu daban take sune Manzon Allah (s.a.w) yayimanz ishara dasu acikin hadisi ruwayar bukhari da muslim ” Akwai wasu nau’in mutane da Annabi baigansuba amma zasuzo anan gaba yake fadawa sahabbansa. Yace dasu dukkan wadannan mutane ‘yan wutane. ” na farko dai shugabanni azzalumai yake nufi kokuma masu hukunci da zalinci. nabiyu kuma yace; wasu matane zaku gansu da kaya ajikinsu amma tsaraicinsu na waje suna tafiya suna karairaya jiki, sa’annan kawunansu kamar tozon rakumi, yace kuma bazasu shiga aljannaba, kuma bazasu ta’ba jin kanshin aljannah ba. Domin awani qaulin anajin kamshin aljanna a tsahon tafiyar shekaru dari biyu ko dari biyar.” Allah kakare ‘ya’yanmu da ‘ya’yan ‘yan uwanmu daga Gurbacewar tarbiya.

‘YAN MATAN ASALI

Allah sarki wadannan sune abin tausayi, kuma sune masu wahala, kuma sune masu rabauta duniya da lahira. Tayadda suke fitowa daga gida na mutunci, iyayensu nagartattune su kuma kamammune. Sukan rike budurcinsu iya jimawar da zasuyi gabanin suyi aure. dashi suke samun martaba da nagartar zamantakewarsu ta aure. Kuma kafin suyi aure basu koda cakuduwane cikin maza ballema suyi wani mummunr mu’amala da namiji, hartakai ga sun zubadda mutuncinsu da budurcinsu. Suna matukar Kula ha hakkokin dake kansu na addini dana zamantakewar rayuwa. sune Allah ya ambacesu acikin Alqur’ani yadda yake cewa a Suratul_ahzab. surah ta-33 Aya ta:35 ”Lalle, Musulmi maza da Musulmi mãtã da muminai maza da muminai mãtã, da mãsu tawãli’u maza da mãsu tawãlĩu mãtã da mãsu gaskiya maza da mãsu gaskiya mãtã, da mãsu haƙuri maza da mãsu haƙuri mãtã, da mãsu tsõron Allah maza da mãsu tsõron Allah mãtã, da mãsu sadaka maza da mãsu sadaka mãtã, da mãsu azumi maza da mãsu azumi mãtã da mãsu tsare farjõjinsu maza da mãsu tsare farjõjinsu mãtã, da mãsu ambaton Allah da yawa maza da mãsu ambatonsa mãtã, Allah Ya yi musu tattalin wata gãfara da wani sakamako mai girma.”

Hakika mata masu addini sune mafi dacewa ga dukkanin wani ďa namiji musulmi. Kuma sune zakasamesu masu kyakkyawan hallayya dakuma tsaftatacciyar budurcin wanda babu kazanta acikinsa.

Duk da cewar kwaciyar aure na rana daya tak, yana wanke dattin kazantar bariki, duk jimawar da akayi dashi. Amma kuma duk da hakan kazanta bariki, yakan sanya zargi atsakanin ma’aurata, Zargi na har abada. Musamman ma yazamanto shima mijin mutumin banzane.

Allah karabamu da danasanin duniya da hasarar lahira. Ameen Dukkannin wanda yakaranta wannan rubutun nawa ya sanya aransa shima zai bada gudun mawa wajen gyara yau da goben Al’umar mususulmi kusani acikin addu’arku dani da mahaifana. Albarkacin wannan wata mai albarka ta Raladhana.

INGANCIN ZUQATAN BAYI

INGANCIN ZUCIYA!!! ***************************************** Hakika gyaran zuciya itace maqasudin kar´bar aiki. Da Akwai Ayoyi da hadisai ingantttu dake nuna jinjina ga ayyukan bayi amma dukkansu suna yabawane akan tsarkin zuciya domin shine (sababin karbar aikin). Hakazalika. ibadar da Allah yafisoma, ~Maqasudinsa zuciyace watau (Azumi).

Shi Azumi ALLAHﷻ (s.w.a) Shine kadai keda hakikanin gasgata maiyinsa, Saikuma Zuciyar maiyinsa, Sa`annan kuma ma ALLAHﷻ shi da kansa yake cewa yana son masu tuba damasu tsarki Ma´ana masu tsarkake zuciyoyinsu daga bari munanan ayyuka. Da ayyukan da aka kyamata. Gashinan in arabic text إن الله یحب التوابین ویحب المتطهری Manzon ALLAH ﷺyana cewa إن فی الجسد مضغة إذا صلحت صلح الجسد کله وإذا فسدة فسد الجسد کله علی وهی القلب Arufai kuyimin afuwa nai muku Shisshigi inda kuskere atusaddani. Dan Adam ajizine ALLAHﷻShine masani. dafatan anyi Juma`ah lafiya