SUWAYE KHAWARIJ ???

SUWAYE KHAWARIJ???

 

khawarij

Sune Mutanen da Banbancin Aqida Ko Maslahar Rayuwa Tasanya Suke Kafirta Shashin Wasu Bangare daga Cikin Musulmi Bisa Ko Da Ilimi Ko Babu Kuma Suna Kisa, Wacce takai Har Suka ‘Dauki Makami Suna Ya’kar Musulmi Suna Kashesu Kuma Suna Halartar da Jinanansu, Wanda hakan Yasamo Asaline: Daga Tsatson Wani Mutum Mai Suna Zul Khuwaisirah Attamimi.

سبحان الله

Wanda Bayan Anyi Yakin Hunain
Bayan anyi Sulhul Hudaibiyya
Ansamu Ganima ayakin Hunain, Manzan Allah ﷺ Yazo Rabo, Sai Munafukai Suka Fara Gutsiri Tsoma Cikin Zancensu Suna zargin cewa Annabi ﷺ Bazaiyi Adalci ba, Suna Wannan Tattaunawar Tasu Cikin Ayarinsu na Munafukai Sai Wannan Mutum Mai Rashin kunya ( Zulkhuwaisirah Attamimi)
Yace: Shifa Saiyaje Yasameshi Danme Baza afadamasa Gaskiya ba Cewar Su Annabi ﷺBazaiyi Adalci ba.

Bayan Hakane Wannan mutumin Mara Mutunci Yazo Kan Annabi Cikin Yanayi na Rashin Kunya Yana Cewa: Da Annabin ”Kaji Tsoron Allah Kayi Adalci” Wa’iyazu Billah ALLAH Ka La’anci Khawarij Makasa Dangi da Sahabban Manzan ALLAH ﷺ. 

        Cikin Sanyin Murya Annabi Yace Dashi ”Yanzu Inbanyi Adalci ba Waye Zaiyi Adalci ” ﷺ.
Nan da Nan Sayyadina Umar Yazare Takobi Yace: Ya Rasulalllah  Barni Insare Wuyarsa Sai Annabi Yace Dashi: ”Barshi Koka Kasheshi Yana da Tsatso, kuma Wasu Zasu Bayyana a Karshen Zamani Makamantansa, Wadanda Idan kaga Sallahr Su Saika Raina Taka, Komai Sukan yi Na Addini fiye da yadda kuke Zato, Amma kuma Suna Fita Daga Addinin Kamar Yadda kibiya Ke Fita daga cikin Baka, Annabi ﷺ Yayi ta Bada Misalinsu kafin Karshen rayuwar sa, Yadda Yakara da cewa Zakagansu Suna Da kananan Shekaru, Kuma Suna Karanta Alqur’ani Amma Bai Wuce Makoshinsu (Ma’ana Babu Alamun Sanyashi Cikin Ayyukansu).
Kuma Suna da Tsantsan Rashin kunya da Nuna Tsantsaini Akan Duniya, Sunada Wofantattun ‘kwa’kwale (Abu Kad’an Yakan iya Canza Tunaninsu).

Sannan Suna Kafirta Kowa Wanda Baibin Bayansu, Idan Fitinarsu Ta tashi Za Su rin’ka Kashe Musulmi Suna Barin Kafirai, Suna da Jayayya dakuma Rashin Amintaka da Yan uwansu Musulmi, Amma Ba Ruwansu da Kafirai, Burinsu Kullum inane Musulmi Yayi Ba Daidai ba (Bin Diddigin Musulmi).

      Kuma Burinsu Akullum Nasu Itace Turba Inzaka zamo Mafi Tsoron Allah agun Kowa Inbaka Cikinsu Kai Ba Musulmi Bane agunsu Dan Haka Idan Sun Bayyana Ku Kashesu Ku kashesu Ku kashesu.

Bayan Zamani yayi Nisa Kuwa Sai Wadannan Mutane Suka Bayyana  Danhaka Suka Fara Sa’insa da Gofnatin Musulunci Tun Azamanin Sayyadina Umar (R. A) Alamun Hakan Tafara Bayyana, Amma Basu Ware Kansuba, Sun Fara Bayyana kansune cikin Munanan Halayyar su Wanda Annabi ﷺ Ya Ambata, Ananne Suka Fara Nuna Adawarsu Da Tawayensu ga Gofnatin Musulunci Haryakai ga Sun Fara Gutsiri Tsoma Ga Shugabancin Gofnatin Na Sayyadina Umar.

Aganinsu Umar Yana Tsanantawa Gurin Hukunci Tayadda Akasamu Wani acikinsu Mai Suna: Abu Lu’uLu’il Majusi Ya Sokeshi Sayyadina Umar (R. A) Da Wu’ka Acikinsa, Wanda Wannan Itace tazamo Jinyar da Tayi Sanadin Shahadarsa.Bayan Shahadar Sayyina Umar (R. A).
  Sai Sayyadina Usman Yacigaba Da Khalifanci, Wadda dama Annabi ﷺ yafada Wa Sayyadina Usman Cewa: Zaiyi Shahadane Tahanyar hakurin da Zaiyi Yayin Wata Musiba Da Zata Shafeshi, Hakurinsa Itace Maslahar Al’uma Sannan kuma itace Zata Kaishi Aljannah, Zaiga Musiba Akarshen rayuwarsa Dan haka Saiyayi hakuri, Inji Annabi Muhammad ﷺ Saboda haka: Bayan Ya Sami Nasarar Zamowa Khalifa, Sai ya Umarce Mutanen Sa cewa Kada Wani Ya Tunkari Mutanen da Duk Sukazo Domin Niman Ransa.    Domin Tunawa Da Wasiyyar Manzan Allah ﷺ Domin Yasan Cewa Shahadace Karshen Rayuwar sa, Kuma Hakan Zai Farune Tahanyar Wasu Daga cikin Musulmi.
Dan Hakane Har Suka Samu Suka Hauro Katangar gidansa, Suka Sameshi na Karanta Alqur’ani Sukayita Saransa Harsai da Jininsa Ya Zuba Akan Alqur’ani Alhali Yana Azumi, Amma Ko Daga Kansa Baiyi ba Haryakai ga Yayi Shahada Sukuwa Suka Fice daga ciki Gidan Sukayi Tafiyarsu, Sunyi Masa Wannan Ta’addancine: Domin Aganinsu Suna Ganin Cewa Yana ‘Daura Danginsane Kad’ai Amuqaman Gofnatin, Kuma ‘Yan Qabilarsane Danhaka Dangoginsane da Gofnatin, Sukuma Sunfison Dangin Manzan ALLAH ﷺ.
  Amma hakikanin Gaskiya itace Zalunci Ne kawai Da Tayarda Rikici wa Addinin Musulunci.

   Sannan kuma Sai Wadannan Mutanen dake Inkarin Mulkin Na Sayyadina Usman (R. A): Suka Nemi Sayyadina Aliyyu (R. A) Daya Maye Gurbinsa, Acewarsu Yacigaba da Khalifanci Da Jagorancin Musulmi,
Sukayita Kurarashi Da Wasu Dadin Baki Amma Sayyadina Aliyu Yaki Amincewa, Domin Acewarsa Yanajin Kunyan ALLAH Akan Wannan Al’amari, Ankashe Wanda ALLAH da Mala’ikunsa sukejin Kunyarsa, Dan haka Shi Da’awa Yasaba Abarshi Yayi Da’awarsa Azabi Wani Yayi Shugabanci. Sai da Wasu  Daga Cikin Manyan Masu Fad’a aji na Sahabbai Suka Sa Baki Sannan Sayyadina Aliyu Ya Amince.
  Dalilin Daya’ki Amince wa Kuwa: Shine Yana Ganin Cewa Bayadda Za’ayi Ayi Wa Sayyadina Usman Wannan ‘Danyan Aikin Bai Dauki mataki ba, Sannan Kuma Ace Ya Zamto Anbashi Ragamar Shugabanci Kunsan Aliyyu Kadanga Ne: Kasar Yaki Dan Baffan Manzan ALLAHﷺ Aganinsa Ankatse Masa Dukkan Wata Damarsa ta Ganin Ya ‘Dauki Mataki Danganeda Al’amarin Matukar Aka Bashi Ragamar Mulki.

   Bayan Ya amince da Yarjejeniyar Zama Khalifane: Domin magance dakuma daidaita Tsakanin Matsalar Musulmi Domin Khawarij Suna Sonsa Sannan kuma Sauran Sahabbaima Shine Za’binsu, Domin Su Wadannan Mutane Sunce Babu Wanda Zaiyi Jagoranci Awannan Lokacin Sai Shi Sayyidina Aliyyu. Kuma Wasu daga cikin Mutanen kirki acikin SAHABBAI Suma Sungoyi Bayansa. Awannan Lokaci Yaga Maslahar Al’umar kawai Itace Ya Rungumi ‘Kaddara Ya Cigaba da Khalifanci.

Bayan Ya Amince da Hakan Ya Kuma Samu Mubaya’ah daga Dukkan SAHABBAI, Sai Kuma Suka ‘Kara Kunna Wata Sabuwar Rigima, Ta Cewar Sai Ankamo Wadanda Suka Kashe Sayyadina Usman, Domin A Aiwatarwa Musu Da Hukuncin Alhali Kuwa Babu Wanda Yasan Su waye Suka Kasheshi.

Daganan Sai Suka Fara Rura Wutar Rigima Tsakanin Musulumi Na Yankin Madina, Har Rikicin Yafara Shafan Wasu Daga Cikin Sassan Sauran ‘kasashen Musulmi, Wanda Har Wasu Daga cikin SAHABBAI Masu Kyakkyawan Manufa Sanda Wannan Rikici Yaritsa dasu, Wasu Kuma Suka ‘Ki Sanya Baki cikin Rikicin, Wanda Harda da Matan Annabi ﷺ Wadda Dama Suna Madina aka Kashe Sayyadina Usman, Lokacin Sunzo Hajji ‘Kar’kashin Jagorancin Aishatu (R. A). Dasauran Matan Manzan Allah ﷺ Duk Sun Daidaita Akan Cewa Sayyadina Aliyu Yafara Bincike Ya Hukunta Wadanda Sukayi Wannan ‘Danyan Aikin. Shikuwa Sayyadina Aliyyu Burinsa Daidaita Al’amarin Shugabanci Kafin Tsara Yadda Gofnati Zata Gudana, Kafinnan Sai Ya Fara Bincike.

  Daganan Bayan Haka Aka Kai Koken Zuwaga Mu’awuya Tahanyar Wadannan Munafukan, Wadda Shikuma Sayyadina Usman Yakasance ‘Dan Uwan Mu’awuya Ne najini, Sai Shima Mu’awuya Yace Bazai Yi Mubaya’a ga Aliyyu ba Harsai Ya Zartar Da Hukuncin ga Wadanda Suka Kashe Usman. Kasancewar Mu’awuya Shima Gofnane Agarin Basra A’kasar Sham Siriya Watau Iraqi Ayanzu.

ALLAHU Akbar Yau ga Ranar Manzan ALLAH ﷺ Ina Ma Ace yana Cikin Duniyar!!! Wallahi Nasan Wannan Ba Komai Bane Agunsa ﷺ Cikin Sakanni Zaiyi Maganin Matsalar ﷺ.

Daganan fa Sai Labari Ya Riski ‘Dalha Bn Ubaidullah, Cewa Akwai Matsala A Can Basra Inda Mu’awuya (R. A) Yake Mulki, Domin Mu’awuya (R. A) Shi da Mutanen sa Sunce Bazasuyi Mubaya’ah ba ga Aliyu.

   Sannan Madina Tayi Zafi, Rikici Yayi Yawa, Aliyyu Kuma Yakoma (Kufa) Can Ta Yankin Da Mu’awuya Yake Mulki, Domin Mutanen Kufa Sunce Da Aliyyu Yazo Yankinsu Su Sun Aminta dashi, Kuma Sunada Babbar Daula Danhaka Yabar Madina Domin MadinaRikici Yayi Yawa, Yazo Gurinsu, Zasu Bashi Cikakken Goyon Baya Yakafa Daular Musulunci Awannan Yankin, Ya zamo Itace Cibiyar Musulunci Wanda Shugaban Musulmi Yake Cikinta Amaimakon Madina ta Asali Afarko.
Sannan Yacigaba Da Dukkan Wata Qudiri dakuma Aikin Shugabancinsa Zasu Dafa Masa Har abinciko Wadanda Suke Kokarin Rushe Daular.

‘Dalha Bn Ubaidullah da Zubairu Bn Awwam Manyane Daga Cikin Manyan Zaratan Sojojin Manzan ALLAH ﷺ Suma Suka Koma Makka Sai Suka Hadu Da Nana Aisha.
Domin Suma kansu Yayi Zafi Tunaninsu Ya Bambanta dana Sayyadina Aliyu (R. A) Cewar Suna Ganin Yakamata Sayyadina Aliyu yafara Kama Wadanda Sukayi Wannan Mummunar Aiki, Domin Yaji Dadin Mulkinsa Dakuma Magance Matsalar Munafukai dasuke i’kirarin Cewa Harda Hadin Bakinsa Aka Kashe Sayyadina Usman (R. A)

Bayan Sayyadina Aliyu Yakoma Kufa Kuma Ita Kufa Wata Babban Jihace Akasar Iraqi Wanda Har ayanzu Tana Cikin Manyan Daulolin Kasar, Ananma Sai Sayyadina Mu’awuya Yace Bazai Ta’ba Yarda da Khalifancin Sayyadina Aliyu (R. A) Ba Harsai ya Binciko Wadanda Suka Kashshi.

Akan hakan Kuwa Yasa Shi Mu’awuya Yakiyimasa Mubaya’a Domin Sa’banin Ra’ayin dake Tsakanin Su, Sannan Haryakai ga ‘Dalha Bn Ubaidullah Da Azzubair Bn Awwam Suka Taso Daga Makka da Nufin Cewa, Dole Ne Sai Sun Shiga Cikin Matsalarnan Tahanyar: Yin Sulhu Tsakanin Mu’awuya da Sayyadina Aliyu (R. A) Kafin Asamu Maslaha.
  Bayan Sun sami Matsaya Danganeda Shawarwarinsu Saikuwa Suka Shirya Domin Zuwa Sulhu Kasar Iraqi Aisha Ma Tace Hankalinta Bazai Kwanta ba Ga Ahalin Gidan Annabi Muhammad ﷺ Cikin Wani Hali Danhaka Sai Yabisu, Sai Kuwa Suka Sauka A Basra Inda Mu’awuya Yake Mulki, Domin Neman Sa daya Janye Akan Yayi Mubaya’a Wa Sayyadina Aliyu, Awannan Lokaci Ne Munafukai Suka So Rura Wutar Gaba Tsakanin ‘Dalha, Aisha, da Zubair (R. A) Da Gulman Cewa Su AISHATU DA ‘DALHA DA ZUBAIR sunje Gun Mu’awuya Ne Domin Suna Goyon Bayan Mu’awuya.

    Shikuwa Sayyadina Aliyu Ai Ba Wawa bane Rainon Manzan ALLAH ﷺ Ba Wasa Bane, Yafi Karfin Zugon Munafukai Kuma Ashe Yagane Akwai Munafukai Masu Rura Wutar Rigima, Saiya Aiki wani Daga Cikin Manyan Zaratan Kwamanadan Sojojin Manzan ALLAH ﷺ Qa’aqa’a Bn Attamimi.
Domin Ya Binciko Masa Menene ake ciki Domin Kada Ya Yanke Hukuncin ABisa Rashin Sanin Hakikanin Abinda yake Gaskiya, Sai Kuwa Yazomasa Da Labarin Cewar Ai Sunzo Yin Sulhu Ne.
Sai Sayyadina Aliyu Yace Aikuwa Baici tazama ba Dolene Yajema Kawai Caan Ayi Sulhun (Yaje Basra) Ayi Acan Domin Ga Manyan Mutanen dayake Jin Nauyin su Acan Basra. Agefe Guda Kuwa Wadannan Mutane Masu Mummunar Manufar Sunanan Suna ta Kullace_Kullacensu.
   Lokacin da Suka Sami Labarin Cewa Sayyadina Aliyu Yatafi Zaije Sulhu Da Mu’awuya Kuwa: Sai Suka Fara Tunanin Yadda Zasu Wargaza Wannan Sulhun Yazamo Ba’ayi Shiba. Domin Sun Tabbatar  dacewar Anayin Sulhu Kan Al’umar Musulmi Zai Hadu Kuma Za’akamosu Ahukuntasu. Shine Suka Rabu Gida Biyu, D’aya Sukaje Basra.

Bayan Sayyadina Aliyyu Yakama Hanya Tareda Rundunarsa Wadanda Sukace Bazasu Bari Yatafi Shidayaba Dole Sai sunbishi Domin kare Ransa da Lafiyarsa. Hakan Kuwa sukayi Suna tafiyane Sai Dare Yayi Musu Ahanya Sai Kuwa Ya Yada Zango Da Rudunar Mutane Dubu Ashirin A wani Guri domin Dare Yayi Dan Su Huta Sai Safiya Acigaba da Tafiya.  Cikin Dare Sai Wadannan Munafukai Wadanda suka Kasu Gida Biyu: Domin Cimma Mummunar Manufarsu ta Wargaza Sulhu, Wani Bangaren Suka Zo wa Rundunar Sayyadina Aliyyu Suna Kashesu Suna Saransu Wasu Bangare kuwa Suka Je Ga Sayyadina Mu’awuya AKasarsa Suna Kashe Sojojin said Suna Cewa Ba Maganar Sulhu.  Nanma Gun Rindinar Sayyadina Aliyu Suka Kama Saran Sojojin Sa Suna Cewa Babu Sulhu, Daganan Kuma Suka Hade Guri Guda Aka Kama Yaki Musulmi da Musulmi, Ana Kisan Juna ba tareda Ansan Dalilin Yin hakan ba Kowa Na Saran Dan Uwansa Amma Baisan Daliliba Sudai Sunsan Cewa Hari Aka Kawowa Kowanne daga cikin su.
Nagartattun Cikinsu Wasuma Basusaniba Wasu kuwa Sunki shiga Yakin Haka kuma Wadanda Suka shiga ma Sunayine Domin Kare Kansu Domin Su aganinsu Kamar Ankawo Musu Harine.
    Awannan Rikicinne aka Kashe Zubair da Dalha Sannan Wasu daga Cikin Sojojin Aliyyu Sune Suka Kashesu Domin Rashin Sanin Hakikanin Me Yakawosu, Yankin Mu’awuya Aganinsu Sune Suka Ruruta Wutar Rigimar, Wani Daga Cikin Sojojin Aliyu Yasamu Azzubair Ibnl Awwam Yana bacci Yadauki Takobinshi Yakasheshi da Ita, Sannan Kuma Ya dauki Takobin Yakaiwa Sayyadina Aliyyu Domin Nuna Bajintarsa Ga Sayyadina Aliyyu,
Da Sayyadina Aliyyu Yaga Wannan Takobi Sannan Wannan Mutumi Yace Dashi Wannan Takobin Dan Awwam ne Da ita Na Kasheshi Dan Sune Suka ruruta Wutar Rigimarnan, Sai Sayyadina Aliyyu Ya Fashe da Kuka Yana Cewa Shin Kasan Hidimar da Wannan Takobi Tayi wa musulunci kuwa?
     Da Wannan Takobine Akayi Gadin Manzan Allah ﷺLokacin da akayi Yakin Khandaq, Annabi ﷺ Baya Samun Bacci Azzubair Shike Gadin Annabi ﷺ Haryasamu Yin Bacci. Manzan ALLAH ﷺ Yakira Azzubair da Hawariyyinsa, Domin Yace dukkan Annabi Yanada hawariyawa Nikuwa hawariyina Shine azzubair.

Sannan Shima Dalha Ibn Ubauidullah Shima Awannan Yakinne aka kasheshi tahanyar Harbin Kibiya Da akayi masa, Sayyadina Aliyyu (R. A) Yafada wa Sayyadina Hassan (R. A) Yace dashi ”Lokacin da ‘Dalha Yazo Cikawa Yace Dani, Abin Baiyi Masa Dad’iba Domin Sunzo Sulhu  Maimakon Sulhu Kuma Sai Ankama Kashe Juna.
Sayyadina Aliyyu Yana yaki yana kuka Yana Fadin wai Meyafarune!!!.

Bayan Anyi Wannan Yaqinne Sai Sayyadina Aliyyu yace: ”Zamu koma Kufa Domin Abin Baimana Dadin Ji da Ganiba” Aisha Kuwa Da taji Abinda Yafaru hankalinta yatashi Sai Tace Zata Koma Gida, sai Aka Sanya Wasu Rudina Karkashin Jagorancin Mu’awuya (R. A) Sukayi Rakiyarta Gamida Wasu Guziri.
Munafukai kuwa dasukaji haka Har Wani Yafara cewa Aidama Ance Kaza_kaza akanta, Da Sayyadina Aliyyu yaji Haka Saiyasa aka kama wannan Mutumin aka tubeshi akayimasa bulalan ‘Kazafi Na Haddi, Sannan Yace Dashi Wannan itace matar Annabi ﷺ Aduniya kuma Qiyama.

    Dagananne Aka Samu Bangarorinnan Na ‘Yan Tawaye Ahlul Bagyi ‘Bangaren Su (Mu’awuya), Dakuma ‘Bangaren Masu Gofnati Su (Sayyadina Aliyyu), Da Munafukai Masu Fad’a Da Dukkan Tsarin Sune (Khawarij), wadanda Dama Annabi Yafadesu Cewa Akwai Wasu Bangarori Biyu Masu Gaskiya Zasu Yaki Juna, Sannan Wasu kuma Zasu Balle Sukuma dabam, Sunzamo Uku Kuma Duk yayi bayaninsu wanda Duk maihangen Nesa Cikin Sahabbai Yaganosu, Kuma Sune matsalar musulmi, Daman Annabi ﷺ yafada Insun Bayyana Akashesu Kada Abarsu Domin Sudin fitinace Ga Alumar Musulmi, Wadda kuma Aliyyu Ya Aiwatar da Wannan Aikin Na Yakarsu kamar Yadda Annabi ﷺ Yabada wasici, Cewar AYakansu Akwai Lada Mai Dumbin Yawa Daga Bakin Annabin ALLAH ﷺ Sannan Yace Idan Za Ayakesu  Ayimusu Kisan Kiyashi (Ankashe Su Dukka) Danhaka  Sayyadina Aliyu (R. A) Ya yakesu kuma Yakashe Kasho Casa’in Da Biyar Cikin Darinsu Saura Kuma Suka gudu.
Sunefa Masu Da’awa Akan cewa Babu Gofnati Babu Hukunci Saina ALLAH, Wanda Har Sayyida Aliyu Ya turamusu Abdullahi Dan Abbas, Domin Yayi Musu Wa’azi, Domin Sunce Aya Suke Nema Ba ruwansu da Shugabancin Wane Ko hukuncin Wane, Sannan Kuma Su Basa bin Wata Gafnati Tsakanin Aliyyu Ko Mu’awuya Ba ruwansu da Kowa.
     Anyi Nasarar Wasu Sun Tuba Sun Amince Sun koma Rindinar Gofnati, Tayadda Wasu kuma Suka Tangare Suka Nuna Girman Kai daga Nanne Sayyadina Aliyyu Yaganefa Sune Wadanda Annabi Yake ta bada Misalinnan Fa, Dagananne Sayyadina Aliyyu Ya Daura Damarar Yaki dasu Domin Yagano Su Yakashe mafi Yawansu, Wasu kuma suka Gudu, Wadanda Suka gudu Suka Tsira Sune Sukayita Yakin Sunkuru Ga Musulmai, Snayimusu Dauki ‘Daid’ai Haryakaiga Sun Kashe Sayyadina Aliyu (R. A) Da Asuba Yafito Yana Tashin Mutane Su Fito Domin Suyi Sallahr Asubahi, Wanda Yakashe Shi Shine Abdullahi Bn Muljum Domin Suna Ganin Su Sayyidina Aliyyu  sun kafirta Saikuma yakama Da’awar Cewa In ankasheshi Yayi Shahada.

Wannan Shine Matsalar Da Musulmi Suka taba Samu Gameda Shugabanci Kuma Shine Dalilin Shahadar Sayyadina Aliyyu Dakuma Dalha Da Zubair Rahmatullahi Alaihim Ajmain.

Kuma Siffar Khawarijawa Kenan: Tawaye wa Aqidar Mutane da Gofnati Da Daukan Makami Akan Al’umar Musulmi.

ANNABI MUHAMMAD ﷺ

  • Nasarorin Ƙungiyar Arewa Media Writers
    Nasarorin Da Ƙungiyar “Arewa Media Writers” Ta Samu Cikin Shekaru Biyu, July 2020, Zuwa July 2022 Ga wasu daga cikin nasarorin… Read more: Nasarorin Ƙungiyar Arewa Media Writers
  • TARBIYYAR ‘YA’YA AMUSULUNCI
    ══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════TARBIYYAR ‘YA’YA AMUSULUNCI══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════ ══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════                       GABATARWA══════ ❁✿❁ ═════ ❁✿❁ ═════                           … Read more: TARBIYYAR ‘YA’YA AMUSULUNCI
  • ZATIN UBANGIJI
    SHAUQI CIKIN AL AMARIN GAIBIYYA Kasantuwar Ubangiji A Buya Bai zama tawaya Ga Imanin Mai imani Sai dai Yana kara imanine… Read more: ZATIN UBANGIJI
  • GODIYA TA GA ALLAH BUWAYI
    Ban Shan Sigari Ban Shan MoringaBan Shan 200 Kayan zamani Ban Leqa tagaKayan Wani bai idona Ni nai ga KatangaShiga Sha`anin… Read more: GODIYA TA GA ALLAH BUWAYI
  • KUJI TAUSAYIN MARAYAN ALLAH
    Bansan me Nayi mussu baNufata da Sharri suke basu barniba Nayi kukan ZuciyaHar na Ido Hawayena Basu fad’i ba Ganinan na… Read more: KUJI TAUSAYIN MARAYAN ALLAH
  • FASAHAR ZAMANI
    Menene capacitor?  Dauki masu gudanar da wutarlantarki guda biyu (abubuwan da suka bari Wutarlantarki ta ratsa su) sai ka raba su da insulator(kayan da ba su barin wuta ya ratsa sosai) sai kayi capacitor: wani abu da zai iya adanamakamashin wutar lantarki. Kara makamashinlantarki ga mai iya aiki shi ake kira caji ; fitar dakarfin daga mai iya aiki shi aka sani dadischarging. Capacitor yana dan kama da baturiya, amma yanada wani aiki daban. Baturiya na amfani dasinadarai don adana makamashin lantarki da sake shi a hankalita hanyar zagaye; wani lokaci (a yanayin agogonkwata) zai iya daukar shekaru da dama. Mai iyaaiki yana sakin karfinsa da sauri-sau da yawa acikin sakanni ko kasa da haka. Idan kana daukanhoton flash, misali, kana bukatar kyamararka don samar da babban burst na haskea cikin fraction na sakan daya. Wani mai iko daaka hađe da bindigogin flash na ‘yan sakanni taamfani da makamashi daga batirin kyamararka.(Yana daukar lokaci kafin caji capacitor shi yasayawanoci dole ka jira kadan.) Da zarar an caji maikarfin, zai iya sakin duk karfin nan take ta hanyarxenon flash bulb. Zap! What is a capacitor?Take two electrical conductors (things that letelectricity flow through them) and separate… Read more: FASAHAR ZAMANI

Kanun bayannai

  • Nasabar Sa
  • Iyayen Sa
  • Haihuwar Sa
  •  Aiko Shi
  •  Hijirar Sa zuwa Madina
  •  Yaƙoƙinsa
  • Matan Sa
  • Yayayen Sa
  •  Masu yi masa hidima na musamman

 Muhammad  Annabi ne kuma Manzo ne wato ma’aikin Allah Madaukakin Sarki. Allah Ya aiko shi domin ya tabbatar da addinin da Annabawan da suka gabace shi suka koyar, Kamar Annabi Ibrahim da Annabi Musa da Annabi Annabi Isah da dukkannin sauran Annabawan Allah (tsira da amincin Allah ya kara tabbata a gare su) Annabi Muhammad (s.a.w) shine cikamakon Annabawa, wato Annabin karshe wanda daga kansa babu wani annabin Allah. Dukkan wanda yayi ikirarin annabta bayan zuwan Annabi Muhammad (s.a.w) to karya yake. Shine kuma ya hada kan dukkan larabawa suka dunkule waje daya, tare da daidaita yan adam ta hanyar koyarwar sa da Alkue’anin da yazo da shi.   

Nasabar Sa

Muhammad ɗan Abdullahi ɗan Abdul-Muɗɗalibi ɗan Hashimi ɗan Abdu-Manafi ɗan Ƙusayyi ɗan Kilabi, Sallallahu alaihi wa aalihi wa sallam, (Harshen Larabci: Abūl-Qāsim Muḥammad ibn ʿAbd Allāh ibn ʿAbd al-Muṭṭalib ibn Hāshim ibn ˁAbd Manāf ibn Qusayy ibn Kilāb) nasabarsa maɗaukakiya tana tuqewa zuwa ga Annabi Ibrahim, alaihi salatu wassalam. Manzon Allah ne. Khataman-Nabiyyin da addinin Musulunci. 

Iyayen Sa

Mahaifiyarsa: Ita ce Aminatu (Āminah) ‘yar Wahbi ɗan Abdu-Manaf ɗan Zuhrata ɗan Kilabi (Radhi Allahu anha). Alkunyarsa: Abu-Qasim, Abu Ibrahim. 

Laƙabinsa:

Al-Musɗafa (zababben Allah) yana da sunaye da suka zo a cikin Ƙur’ani Mai Girma kamar, Khataman-Nabiyyin, da Al-Ummi da Al-Muzzammil da Al-Muddassir da An-Nazir da Al-Mubin da Al-Karim da An-Nur da An-Niˁima da Ar-Rahma da Al-ˁAbdu da Ar-Ra’uf da Ar-Rahim da Ash-Shahid da Al-Mubasshir da An-Nazir da Ad-Da’i da sauransu. 

Haihuwar Sa

An haifi Annabi Muhammad (s.a.w) a wajen shekara ta 570Miladiyya. Mahaifinsa shine Abdullahi ya rasu kafin haihuwar Sa. Mahaifiyar sa Amina itama ta rasu lokacin da yake dan shekara shida a [[duniya]. Haka yasa kakan sa Abdul-Mudallib ya rike shi har zuwa lokacin daya rasu, lokacin Annabi Muhammad (s.a.w) yana dan shekara takwas a duniya. Daga nan sai kawun sa Abu-Talib yaci gaba da rikon sa. Abu-Talib ya taimaka ma Manzon Allah (s.a.w) sosai a rayuwar sa. 

Aiko Shi 

Kogon Hira, wajen da aka fara wa Annabi WahayiAikoshi: An aiko shi a Makkah 27 Rajab yana ɗan shekara arba’in. Koyarwarsa Ya zo da daidaito tsakanin dukkan halitta da ‘yan-uwantaka da rangwame na gaba ɗaya ga wanda ya shiga musulunci, sa’annan ya kafa shari’a maɗaukakiya da dokoki na adalci da ya karɓo daga wajan Allah su kuma musulmi suka karɓa daga gare shi.

 Mu’ujizozinsa

 Mu’ujizarsa madauwamiya ita ce Ƙur’ani amma waɗanda suka faru a farkon Musulunci suna da yawa ba sa kuma kirguwa. Kiransa Ya kira mutane zuwa ga Tauhidi a Makkah a ɓoye shekara uku ya kuma kira su a bayyane shekara goma. 

Hijirar Sa zuwa Madina

Bayan Tsanani da takurawar Kafuran Makkah akan Annabi Muhammad (s.a.w) da wadanda sukayi inami da shi yayi yawa, sai Allah Yayi ma Manzon Sa da sauran Wadan da sukayi imani da shi izinin akan suyi kaura daga garinsu na haihuwa wato birnin Makka zuwa wani garin daban na wati Madina. Mutanen birnin Madina kuwa sunyi matukar murna da zuwan sa garin su kuma sun bashi kyakkyawan masauki. Sanna kuma sukayi imani dashi suka shiga AddiMusulunci. A farkon Hijira dai Shi Annabi da kansa dakuma babban aminin sa kuma na farko wajen imani dashi wato Sayyadina Abubakar Sukayi tasu hijirar tare. Sannan sauran musulmai sukayi ta bin bayansu daya bayan daya. Kaurar Annabi (s.a.w) daga Makka zuwa Madina shine ake kira Hijira kuma shine farkon kalandar Musulunci. 

Yaƙoƙinsa

Inaso Mai Karatu Yayi haquri, Wannan Babi Zamu daukeshi amatsayin Darasinmu na Gaba

إن شاء الله 

Matan Sa

Annabin Musulunci Muhammad Ya auri mata goma sha daya, ga Jerin sunayen su. 

  • Khadijah(Kubura ‘yar kuwailadu)
  • Saudat
  • A’ishah(‘yar Abubakar )
  • Hafsah(‘yar Umar)
  • Zainab(‘yar Kuzaimata)
  • hindatu(ummu salama)
  • Zainab(‘yar jahshin)
  • juwairiyya
  • ramlat
  • safiyya
  • maimunah

Yayayen Sa

Ammominsa: Tara ne, su ‘ya’yan ˁAbdul-Muɗɗalib ne: Al-Haris da Zubair da Abu Ɗalib da Hamza da Al-Ghaidaq da Dirar Al-Muqawwam da Abu Lahab da ˁAbbass. Ammominsa mata: Su shida ne daga iyaye mata daban-daban su ne: Aminah da Ummu Hakima da Barra da Atiqa da Safiyya da Arwa. Wasiyyansa goma sha biyu ne, su ne: Amirul-Mu’minina Ali ɗan Abi Ɗalib (a.s) da Hasan ɗan ˁAli da Hussain ɗan ˁAli da ˁAliyyu ɗan Husaini da Muhammad ɗan ˁAli da Jaˁfar ɗan Muhammad da Musa ɗan Jaˁfar da ˁAli ɗan Musa da Muhammad ɗan ˁAli da ˁAli ɗan Muhammad da Alhassan ɗan ˁAli da Muhammad ɗan Hassan Mahadi (a.s). 

Masu yi masa hidima na musamman

Mai tsaron ƙofarsa: Anas ɗan Malik. Mawaƙinsa: Hassan ɗan Sabit, da ˁAbdullahi ɗan Rawahata, da Ka’abu ɗan Malik. Mai kiran sallarsa: Bilal Al-Habashi da ˁAbdullahi ɗan Ummu Maktum da Saˁad Al-Kirdi. Tambarin zobensa: Muhammadur Rasulullah! Tsawon rayuwarsa: shekaru 63. Tsawon lokacin Annabtarsa: shekaru 23. Tarihin wafatinsa: 28 Safar 11 H. 

Wajan da ya yi wafati: Madinah.

 Inda aka binne shi: Madinah a Masallaci Maɗaukaki Mai Alfarma. Ka sani cewa Muhammad (S.A.W) shi ne ƙarshen annabawa kuma addininsa shi ne musulunci mai shafe duk wani addini kuma shari’arsa zata wanzu har zuwa qiyama kuma ita kaɗai ce shari’ar da zata arzuta mutum da tabbatar masa da burinsa da amincinsa har zuwa ƙarshen rayuwar duniya da lahira. Kamar yadda shi kaɗai ne mutum abin koyi ga dukkan duniya baki ɗaya, dukkan mutanen duniya idan suna son alheri ga kawukansu to dole ne su bi tarfarkinsa su yi koyi da kyawawan halyensa (S.A.W) da kuma sanin sashen tarihinsa da ba makawa mu kawo wasu daga siffofinsa (S.A.W): Shi ne Muhammad ɗan ˁAbdullah (S.A.W) kuma babarsa ita ce Aminatu ‘yar Wahab. An haife shi a Makkah ranar juma’a goma sha bakwai ga watan Rabi’ul awwal bayan ɓollolwar alfijir a shekarar giwa, a zamanin sarki mai adalci Kisra . (wato idan an kwatanta shi da ire-irensa). 

Aiko Annabi Mai Daraja (S.A.W)

 An aiko Annabi Muhammad (S.A.W) da saqo a 27 ga Rajab bayan yana ɗan shekara 40 yayin da Jibrilu (A.S) ya sauka gareshi daga wurin Allah (S.W.T) yana kogon Hira wanda yake dutse ne a Makkah ya ce masa ka karanta kuma ya saukar masa da ayoyi biyar na surar Alaƙi . Sai ya zo ya tsaya a kan dutsen Safa a masallaci mai alfarma na Makkah a lokcin akwai jama’a masu yawa a wurin da ake taruwa ya isar da saƙon Allah na shiryar da mutane zuwa ga imani da shi yana cewa da su: “Ku ce babu abin bauta sai Allah kwa rabauta” . A lokacin tunda mutanen Makkah mushrikai ne, kuma suna ganin maslaharsu ita ce shirka kuma suna tsoron maslaharsu sai suka riƙa yi masa isgili suna yi masa dariya suna cutar da shi. Kuma duk sa’adda ya dage wajen shiryar da su sai su dage wajen cutar da shi har ya ce: “Ba a cutar da wani Annabi ba kamar yadda aka cutar da ni” . Ba wanda suka yi imani da shi sai mutane ƙalilan, na farkonsu Imam ˁAli sannan sai matarsa Khadijah (A.S) sannan sai wasu mutane. Farkon wanda ya yi imani da shi daga maza Imam Ali sannan daga mata sai Hadiza (A.S). Yayin da takurawar mushrikai ta yi yawa sai ya yi hijira zuwa Madinah wannan kuwa ita ce hijirar farko a tarihin Musulmi, yayin da suka yi yawa sai qarfinsu ya daɗu kuma suka samu koyarwa daga Manzon Allah da shari’arsa Mai Sauƙi Mai Hikima, da kuma misali na kyawawan halaye da mutumtaka da wayewa da cigaba a Madinah har suka fi dukkan duniya da addini na sama da waɗanda ba na sama ba. Kuma an samu yaƙoƙi masu yawa a Madinah kuma dukkanninsu sun zama domin kare kai ne daga maƙiya mushrikai da yahudawa da kiristoci da suke kai hari kan musulmi, kuma Annabi a kowne lokaci yana zaɓar ɓangaren sulhu da zaman lafiya ne da rangwame, don haka ne ma adadin waɗanda ake kashewa daga ɓangarorin biyu ba su da yawa a dukkan yaƙoƙinsa tamanin da wani abu, wato; waɗanda aka kashe na musulmi da kafirai duka ba su kai sama da dubu ɗaya da ɗari huɗu ba. Mutuwa Mai Zafin Gaske Tun lokacin da aka aiko Annabi da saƙo har ya tafi daga duniya wahayi yana sauka gareshi kuma Jibrilu (A.S) shi ne ake aiko masa daga wajen Ubangiji (S.W.T) a hankali a hankali har littafin Ƙur’ani ya ciki a cikin shekaru ishirin da uku, sai Manzo (S.A.W) ya yi umarni da a haɗa shi kamar yadda yake a yau ɗin nan. Manzo (S.A.W) ya kasance yana tsara wa musulmi duniyarsu da addininsu, yana sanar da su littafi da hikima kuma yana yi musu bayanin dokokin ibada da biyayya da mu’amala da zamantakewa da siyasa da tattalin arziki da sauransu.

Continue reading

TARIHIN GWARGWARMAYAR KAFA IZALA

ASSASA IZALA A NIGERIA

Izala Ikon ALLA ﷻ

KADAN DAGA TARIHIN SHEIKH ISMA’ILA IDRIS BN ZAKARIYYA !!!

kamar yadda nayi maku Alqawari


     **Gwagwar mayarsa wajen Kafa Izala da Sunnah**

Sheikh Isma’ila Idris yatasone cikin al’umar nan tamu ta Nigeria, ayankin Arewa inda awannan lokacin babu wata aqida a Qasarnan bayan Dariqar Tijjaniyya, Qarqashin jagorancin sheikh Ibrahim Inyas Alkaulahy.
     To dake zamani ya Nausa tafiya tayi nisa, Al’uma tasamu kanta cikin yanayi na Cakuda addini da Son zuciya. Ana samun Malamai masu Sanya Son ransu acikin addini suna anfani dasunan Addini Suna isarda Munanan manufofinsu ga Al’uma kalar Bokanci da Sihirin Duba dama wasu Tsubbace_tsubbace su na Son Zuciya da Neman duniya.
    Wanda yaci karo da koyarwar Addinin Musulunci. Dukkan mai irin wad’annan aiki Bai tabayinsu Saiya fita a addinin Musulunci, Yazamo dukkan wanda yayi Sunansa kafiri da Nassin Aya acikin Suratu baqarah. Haqiqah bayan Wannan Akwai wasu littattafai dadama wadanda Maluma suka shigo dashi ake karantasu na Labaran mafarki da Tatsuniyoyi dasunan Adddini, Irin wadannan abubuwa dakuma makamantansu Sune maqasudin Da’awar ta Sheikh Isma’il Idris, abisa fahimtar masu kyautata masa zato.
    Da’akwai wadanda suke ganin cewa kawai yafara da’awar izala ne kawai Don Neman Suna dakuma Zagin Wasu malamai (Shehunnan ‘Dariau) dakuma Sufaye. Wanda kuma hakan kuskurene domin  Aikin Musulmi shine kyautatawa juna zato. Da Kuma nemawa juna gafara agunda akayi Kuskure danganeda Sa’banin Ra’ayi ko Fahimta.


    Zamu cigaba ta Tarihi.
    Bayan Malam Yabar aikin Soja wanda acikin Aikin nasa na Soja ya fara da’awa akan barin Tsubbu da Daura layu da makamantansu, Malam yasha tsangwama daga makiya dakuma wadanda basu da ilimi wanda basu fahimceshi ba. Ba awannan Lokaci malam yaga cewar Wannan Da’awa tasa bazata cigaba ba Har saida wata Qungiya Wacce zata Tallafa masa Danganeda samun cikar Qudirinsa na Farkadda mutane game da Sunnah Asali.
    Awannan lokacine malam ya Assasa wata Kungiya mai Suna; ”Jama’atu izalatul Bid’ah ” Ma’ana ( Gungiyar dake kawar da Bidi’ah ) Wannan Kungiya Tasa tasamu karbuwa hatta aciki ‘Yan uwa Sojoji na wannan lokaci, Saidai kuma tasamu naqasu Sosai daga Malaman wannan zamanin Musamman wadanda keda Wannan aqidar ta Tsubbace_tsubbace da Duba. Tayadda sukayita yimasa Tuggu da zagon kasa gurin Sun ga sun dakushe wannan aikin Nasa, Tare da Wargaza aikin Nasa tahanyar kirkiran karya akansa hadda cutar dashi domin Su samu Galaba akansa, Amma ahakan Allah ya Tserataddashi daga dukkan tarakunan nasu Allah ya kuma karfafa Wannan Da’awa tasa har ilayau Qugiyar izala tana nan kuma tana cigaba da aikinta wajen karantar da Al’uma bisa koyarwar magabata dakuma Tabbatar da Qur’ani da Hadisi sune tafarkin Tsira ga Bayi.
    Ahakan aka cigaba da kasancewa har takai yaje izuwa ga Malamin sa na Tauhidi Assheikh Abubakar Mahmud Gumi, Domin neman izini da Karin lamani dangane da Da’awar tasa. Awannan lokacine Sheikh Abubakar Mahmud Gumi ya nuna Bashi Cikakkiyar goyon baya gamida Cikatamasa Sunan Gungoyarsa da ” Wa’iqamatissunnah ”  ma’ana ( Dakuma Tsayar da Sunnah ) Wcce tazamo ” Jama’atu izalatul Bid’ah Wa’iqatissunnah ”
    Ma’an ( Qungiyar dake kawar da Bidi’a kuma take Tsayar da Sunnah )
    Domin acewarsa Sheikh Abubakar Mahmud Gumi; Babu Yadda za’ayi akawar da bidi’a abarta haka ba acike Gurbinta da wani abu ba, Shine Yace to sai Acike Gurbinta Da Sunnah.
    Kunga Ashe kenan ita Izala ba Fitina bace Sabanin Yadda wasu daga cikin maluman ma da basu fahimta ba, Kuma bawai Reshen addini bace kamar yadda wasu suke yimata Mummunar fahimta Har ma wasu ke ganin Cewa in baka ciki to baka cika musulmiba, wasu kuma ke Mata ganin Cewa inkan cikinta Musuluncinka da Gyara Haqiqa Dukkan Mai yiwa Wata Aqidah ta Musulunci ganin Wannan Al’amari, Alal hakika ya Jahilci Hakikanin Musulunci,
    Wannan kadan kenan daga Tarihin Sheikh Isma’ila Idris da Gwagwarmayarsa gurin kafa Izala, insha Allah Anan gaba Zan kawo muku Cigaban da iza ta Kawo Wa Musulunci da Kasarmu baki daya. In Allah mai Komai ya kaimu bayan Sallah.
    Nine naku Isma’il Hussaini Adam Alpholtawy


    Kuma Wannan Shine karshen Rubutuna danganeda Shafukan Tarihin na Bana A Hijira sheka ta 1442 Saikuma Allah ya Kaimu Almuharram Shekara ta 1443 Zan cigaba da Wannan Tarihi.
    Mai karatu ga Addu’a ta Katayani da Ameen.
    Ya ALLAH Kajiqan Mahaifina Hussaini Adam Jumba wanda Ya Rasu a irin Wannan wata Mai Alfarma kuma Aranar Idin Adhhaa, Idin Babban Sallah Allah Kajikansa Ka gafarta masa ka kai Harke Qabarinsa, Kabashi Aljannah Madaukakiya.
    Ya ALLAH Mu Zuri’arsa Da muka Rage a bayan Kasa Allah ka azurtamu da Dogora abisa Addininka, Kabamu Shahada irin tasa, kasanyamu Cikin Wadanda kake Yantawa Zuwa Aljannah.
    Ya ALLAH Ka Sitirtamu da Sutura ta Musulunci, Ka azurtamu da Arzikin imani, da Ikhlasi da Tabbatuwa akan imani, Har Mu Mutu muna masu imani Da Miqa wuya gareka Allah.
    Ya ALLAH ka daukaka musulunci da musulmai, ka Qaskantar da Kafirci da Kafirai kadirkake makiyanka makiyan addini Allah kataimaki bayinka Nagari.

Mawallafi Ismail Hussaini Adam Alpholtawy

AQEEDAH TA ITACE MUSULUNCI

AQEEDATA

Dasunan ALLAH MAI RAHAMA MAI JINKAI

      Wasallahu Alaa man Laa Nabiyya ba’adahu Muhammadun bn Abdullah .(ﷺ) Salawatullahi Alaihi, wa Alaa Aalihi wasahbihi wasallama tasliiman khasira.

Waba’ad;
Assalamu alaikum warahmatullahi warahmatullahi wabarkatuhu, Mai karatu idan baka manta ba ada nayi Alqawwarin fadawa mai karatu mecece aqedata, dakuma matsayata dangane da halascin wakokin yabo da kirari da Haramcin kida Amusulunci.

Ⓜ Mashaa ALLAH Alkawwari yacika;
     Ni Ismail Hussaini Basalafene (Assalafy) Ne. Sala ba Kungiyace ta Aikin addini bawai Shi`anci bane. Wata al umace dake aiki akan Hani ga barna dakuma umarni da aikin Alkhairi. wacce take kuma koyi da magabata. Ainihin Kalmar Salaf tana nufin Magabata.

Salagiyya kuma tana nufin Bin tafarkin magabata. Wannan itace Al umar damuke koyi dasu na kwarai din cikinsu. Amma mu musulmaine kamar Sauran musulmi. Kuma munyi imani da Alqur`ani da hadisai kuma manzon mu shine مُحَمَّد ﷺ

Shi muke kwaikwayo a hali dakuma ayyukan.
Basai nayi bayani akan ko mene aqidah ba. Domin abaya nayi bayani akai karin bayani dan ganeda aqidar salafawa shine { (Aqeedadussalafussalih bi muwafaqati Sunnatin_nabawiyya wa Ashabuhum) (Ma ana aqidar bin tafarkin annabawa da sahabbansu) }.
   Aqidar itama Ahlussunnah ce akarkashinta akwai izala kamar yadda akasani, wadda suke da manufa iri daya dan ganeda da`awa da tsarukan karantarwa iiri daya saidai ita salafiyya kuma tafi yada da awarta ta social media fiye dana izala. ma`ana tafi dukufa wajan rubuce rubucen tarihi ta hanyar wayar da kai ga addinin musulunci da musulmai bisa yadda Zamani yakasance.  Dawayar da kan mutane Dan ganeda rayuwarsu dazamantakewarsu da Ladaftar dasu da koya masu dabarun rayuwa dawayar dasu Ga addini suyishi sukuma dabbakashi dayadashi a duniya.  Dukka sune Aikin salafawa.
Kar nazurfafa atakaice wannan itace aqidata. saikuma magana akan maulidi da kasidu masu kida da da marasa kida.

WAKOKIN YABON ANNABI
Haqiqa wakokin yabon annabi babu Kida ya halasta kaidai dolene yazama duk yaren dazakayi wakan yabon annabi dashi. yazamana kana da ilimi akan yaran sosai domin kiyaye kalmomin da zakayi amfani dosu, donyin yabon kuma dolene ka koyi ilimomi aka yaran kamar haka: ilimin balaga, Qaamusu, Ka`idojin rubutu, Ilimin Grammar, Dakuma tarihim annabin dama mawakansa  nada, domin azamanin annabi  ﷺ Anyi masa waqoqi dayawa harma ayari yake dasu na mawaka Ammafa su basuyi da kida bakuma yi sukeba Dan holewarsu ba ssunayine domin maida martani wa kafirai sai kuma domin dafawa Ga fiyayyen halittaﷺ kutambayi malamai zasu baku karin bayani akai.
    To awannan zamani namu akwai mawakan dake waqoqi nayabo amma da kida ko nace kayan sauti mabanbanta. wallahi! Tallahi!! Billahillazi La ilaha illahuwa wuce gona a kayan kida sautin shaidanune!!!

Me karatu kayi shari ah ta adalci٠
Masu wakokin yabo ayanzu musan man agun maulidi shin kaso hamsin cikin dari suna tantance me suke fada kafin su fada awakokinsu? babu shakka Amsar itace a`a.
   Muyi wa kanmu adalci waqa na ilimi wanda ba kida nayabon Annabi yahalasta amusulunci, ko muma a Tafiyarmu ta salafawa munada mawaqan yabon annabi amma basuyi da kida kuma sai an karantaddasu kuma littafai suke bugawa akuma tantancesu agaban malamai kafin suje subayar ga masu hazakar furuci su rera wakokinsu ba cinzarafi da zagi ko aibata wani ko wata aqida da ace ´yan d`ariqun sufaye da ´yan Shi`ah suma zasuyi adalci wa kawunansu dasai suma su rage msu hankalin cikinsu yakamata su daina waka da kida suyi waqa tsarkakakkiya da yabo wanda yadace da tunani mai kyau da koyarwar Addinin musulunci.
 

 BIKIN MAULIDI 

Bashakka bikin Maulidi Bai ingantaba koda ahadisine mai raunine babu, ba  ko wata yarjeniya ta wata ayari namaluman sunnah danayanzu dana da duk sun daidaita akan bai ingantaba. Hasalima suna kirantane da bidi´ah muhadatha ma`ana bidi`ah kirkirarriya. Batada tushe ko asali daga magabata, akwai hadisai dayawa wadanda suke tsawatarwa danganeda kirkira a addini. Arufai na tsawatarwa danganeda kirkira a addini. Ayanzu acikin maulidi allah ﷻ Shine kawai yasan bidi`o`in da aka kirkiro.
  Banso Raba rubutun  ba amma dolene ta saka `yan uwa kuyi hakuri muhadu arubutu nagaba mai Taken Aqeedata