Nasarorin Ƙungiyar Arewa Media Writers

Nasarorin Da Ƙungiyar “Arewa Media Writers” Ta Samu Cikin Shekaru Biyu, July 2020, Zuwa July 2022

Ga wasu daga cikin nasarorin shekarar farko July 2020 zuwa July 2021;

  • Ƙungiya ta samu karɓuwa a wurin al’ummar yankin Arewa.
  • Haɗin kan Marubutan yankin Arewa.
  • Magana da murya guda a madadin dukkannin Marubutan Arewa.
  • Kare martabar yankin Arewa, da al-ummar yankin, kan ƙalubalen da suka dinga fuskanto yankin.
  • Wayar da kan al’ummar Arewa game da abubuwan da zai amfane su, da wa ‘yanda ba za su amfane suba.
  • Wayar da kan al’ummar Arewa game da kin shiga zanga-zangar EndSars, da ‘yan kudancin Najeriya suka yi a shekarar 2020 wanda ya kusan zamowa fitina.
  • Daƙile manyan labaran ƙarya kafun su yi tasiri a cikin al’umma.
  • Nasarar da ƙungiya ta yi wajan tallata “Ranar Arewa” 20 July 2020 na kowace shekara, bayan wasu masu kishin yankin sun kirkireta, don tunawa tare da jawo hankulan manyan Arewa kan dukkannin kalubalen da yankin ke fuskanta.
  • Koyawa Marubuta yadda ake rubutu, tare da saka Gasa domin zaburar da Marubutan Arewa a wasu daga cikin jihohin Arewa.
  • Jawo hankalin hukumar WAEC a shekarar 2020 kan saka lokacin zana jarabawa a daidai lokacin da musulmai suke gudanar da Ibada a ranar Jumma’a, daga karshe hukumar ta gyara lokacin.
  • Jawo hankalin gwamnatin jihar Jigawa kan ƙalubalen da talakawa zasu fuskanta, idan aka daina karatu kyauta a Jami’a mallakar jihar (Free Education) bayan majalisar jihar ta yi yunƙurin mai da tsarin biyan kuɗi mai yawa ga dukkannin daliban jihar.
  • Jawo hankalin gwamnatin Tarayya da jihohi akan Tallafawa al’ummar da iftila’in ruwa ya shafa, a jihohi da dama na Arewa a shekarar 2020 da shekara ta 2021.
  • Jawo hankalin mahukunta dake da alhakin kunnawa manoman Rani ruwa a garuruwan Bunkure, Kura, Garin Mallan, Da Garin Karfi dake jihar Kano, bayan abinda suke nomawa ya fara bushewa saboda rashin ruwa.
  • Jawo hankalin gwamnatin jihar Adamawa wajan sasanta rikicin masu sana’ar adaidaita (Keke-Napep) a garin Numan dake jihar, duba da yadda dubunnan Al-ummarmu suka dogara da sana’an.
  • Jawo hankalin gwamnatin Najeriya da na jihohi game da halin rashin tsaron da ya addabi yankinmu na Arewa.
  • Jawo hankalin ‘yan kasuwa game da halin matsin rayuwa da al-umma suke ciki, sanadin tsadar Abinci.
  • Rubuce-rubuce tare da zaburar da matasa akan su tashi su nemi sana’a domin su dogara da kansu.
  • Tallafawa daliban makaranta da robobin cin Abinci guda 100 a jihar Zamfara.
  • Nasarar samun goyon bayan manyan Arewa Sarakuna, Dattawa, da sauran manyan dake kishin yankin Arewa, wurin gudanar da ayyukan kungiyar.
  • Gudanar da manyan taruka a wasu daga cikin jihohin Arewa da dama, domin haɗin kan Marubutan Arewa, tare da ƙarfafa zumunci a tsakaninsu don fuskantar duk wani ƙalubale da ya tunkaro yankin.
  • Jawo hankalin gwamnatin Najeriya kan ta gaggauta daukan mataki akan kisan kiyashin da ake yiwa ‘yan uwanmu ‘yan Arewa dake zaune a kudancin kasar.
  • Ankarar da gwamnati game da matsalar gurbacewar ilmi a cikin al’ummah.
  • Kira kirayen ƙungiya ga gwamnati kan a kawo ƙarshen satar yara a makarantu.
  • Jawo hankulan al’ummah kan muhimmancin ilimin ‘ya’ya mata.
  • Tunatar da al’ummah da faɗakar da su na tsawon kwanaki 30 na watan Ramadan a shekarar 2021.
  • Yunƙurin kawo ƙarshen bangar siyasa a kafofin sadarwar zamani.
  • Nasarar samun shiga gidajen Radio da Television a jihohi daban daban don bayyana manufar ƙungiya da kuma alfanun kungiyar.
  • Ƙungiya ta zaburar da dubban matasan Arewa kan su nemi basussukan da gwamnatin Tarayya take bayarwa domin dogaro da kai.
  • Ƙungiya ta samu nasarar ƙulla ƙawance da ƙungiyoyi mabanbanta don ciyar da yankin Arewa gaba.

SHEKARA TA BIYU

Nasarorin da ƙungiyar “Arewa Media Writers” ta samu a cikin shekara ta biyu da kafuwarta daga July 2021, zuwa July 2022.

Ga wasu daga cikin nasarorin;

  • “Arewa Media Writers” tayi nasarar kai koken al-ummar musulman garin Obajana dake Kogi, bayan ruwan sama ya lalata tsohuwar maƙabatarsu, har sarkin Obajana Kirista Engr. Dr Idowu Isenibi, Oba Of Obajana ya baiwa musulman garin Obajana makeken Fili Hetka 10 da samun gudumuwar kudi sama da miliyan daya da rabi.
  • Ƙungiya ta wayar dakan al-ummar Arewa, tare da kira ga al-ummar Arewa da su yi ragistar katin zabe a lokuta daban daban, duba da yadda ‘yan kudancin kasar suka yi mana fintinkau.
  • Ƙungiya ta dau nauyin horar da ‘ya’yan Ƙungiyar wajan koyar da su yadda ake rijistar katin zaɓe ta yanar gizo-gizo a wasu daga cikin jihohin Arewa.
  • Ƙungiya tare da hadin guiwar babban dakin karatu na jihar Kano ta yi nasarar bawa mutane 131 horo akan loyar da su ilimin na’ura mai kwakwalwa.
  • Jami’ar koyar da harsuna ta kasa da kasa “International University of Languages” (IOUL) dake jihar Sokoto ta dau nauyin koyar da membobin kungiyar “Arewa Media Writers” ilimin sanin aikin yaɗa labarai a zamanance “Social Media in ICT” tare da basu Certificate na shaidar karbar horo.
  • Kungiya ta ziyarci tsangaya tare da raba kayan tsaftace muhalli da kayan shayi a babban birnin Tarayya Abuja.
  • Ƙungiya ta bada gudummuwa wurin ganin an raunata jaridar “Sahara Reporters” kan batanci da ta yiwa Annabi (SAW) da yankinmu na Arewa, wanda har yau bata da wo cikin hayyacinta ba.
  • Ƙungiya ta jawo hankalin gwamnati kan gyaran asibitin garin Garun Babba, dake karamar hukumar Garun Malam a jihar Kano, wanda shugaban karamar hukumar ya dau nauyin gyarawa.
  • Ƙungiya ta wayar da kan al’ummar Arewa game da abubuwan da zai amfane su, da wa ‘yanda ba zai amfane suba akan rayuwar yau da kullum.
  • Ƙungiya ta yi tattaki zuwa Abuja, ta kaiwa shugabannin hukumomin tsaron Najeriya budaddiyar wasika kan halin da al-ummar Arewa suke ciki na rashin tsaron da ya addabi wasu yankunan dake yankin, tare da jawo hankalin su da su ƙara zage damtse don ganin an kawo ƙarshen rashin tsaron da ya addabi yankin.
  • Kungiya ta yi nasarar turawa shugaban kasar Najeriya buɗaɗɗiyar wasiƙa, ta gidajen jaridun DAILY Trust, Blueprint, VOA Hausa, da sauran manyan jaridun ƙasar, kan halin da al-ummar Arewa suke ciki na rashin tsaron da ya addabi wasu yankunan dake yankin, tare da jawo hankalin shugaban ƙasar da ya ƙara zage damtse don ganin gwamnatin shi ta kawo ƙarshen rashin tsaron da ya addabi yankin.
  • Ƙungiya ta yi Nasarar rubuta Littafi mai suna “RAYUWAR SAMARI DA ‘YANMATA A SOCIAL MEDIA” wanda aka yi bikin kaddamar dashi a watan junairun shekara ta 2022.
  • Ƙungiya tayi nasar gudanar da taron bita akan amfani da kafofin sadarwar zamani a jihar Filato.
  • Ƙungiya ta ja hankalin matasan Arewa a lokuta da dama, tare da wayar da kansu akan su guji bangar siyasa, don gobensu tayi kyau.
  • Ƙungiya tayi nasarar rubuta littafi mai suna “matar bahaushe” dake dauke da darusa iri-iri, anyi akayi bikin kaddamar dashi a jihar Jigawa.
  • Ƙungiya tayi nasarar horar da membobinta “Excos” reshen jihar Sokoto na tsawon kwanaki uku “3 Days Seminer” akan yadda ake rubutu.
  • Ƙungiya ta gudanar da rubuce-rubucen jan-hankali masu yawa a gidajen jaridu da kafofin sada zumunta, game da cin kashin da ake yiwa ‘yan uwanmu ‘yan Arewa dake zaune a kudancin Najeriya.
  • Kungiya ta yi nasarar horar da marubutan Arewa sama da 500 game da yadda ake aikin jarida da rubutu a kafofin sada zumunta, tare da basu takaddar shaidar karɓar horo (certificate) wanda yanzu haka yake gudana. Insha’Allah kungiyar “Arewa Media Writers” za ta gudanar da irin wannan seminar din a kowace jiha dake Arewacin Najeriya, don horar da dukkannin masu amfani da kafofin sada zumunta a kokarin kungiyar, na tsaftace harkar rubuce-rubuce a kafofin sada zumunta.
  • Ƙungiya ta gudanar da Rubuce-rubuce masu amfani ga al-ummar Arewa, da ba za su ƙirgu ba, tun daga watan July na shekarar 2020 da aka kafata har zuwa yanzu July shekarar 2022.

Mamallakin Wannan Kafa Tareda Alhakin Sanya Rubutu Gamida Hada Manhajar (Appllication).

Danna Maballin da Aka Sanya Manhajar Tarihi, Domin Saukewa Yanzu.

Edited by

(Paper Presentation Committee)

Abdulrahman Suleiman Zaria

Chairaman

Muhammad Kwairi Waziri

Secretary

@Coded Prints 08137556140

Ameera Yusuf Duguri

Treasurer

Huzaifa Ayuba

Member

Bashir Abubakar Gombe

Member

Walida Hussaini

Member


Shared By

ISMAIL HUSSAINI ALPHOLTAWY

Member

Hakkin Sanyawa Awannan Pejin tareda Mallakar Peijin

MASHAHURAN MUSULMAI DA SUKA FARA KIRKIRAN AIKIN LIKITANCI A DUNIYA


Kamar yadda nayi bayani a rubutu na farko Wani abin haushi da Turawan yamma na yanzu suke yi shi ne, na boye sunayen Musuluncin waɗannan mutane, suna sa musu nasu na Turanci, wai don a ce su ma nasu ne.
Ga kadan daga cikin irin wadannan mashahuran Musulmin da suka fara kirkiro abubuwan da har yanzu ake amfani da su: An ba da duka sunayensu na ainihi da na Turancin da kuma zamanin da suka zo:
~ Muhammad bin Zakariyya Al-Rhazi: Rhazes (865-925AD):Mutumin kasarFarisa (kasar Iran ta yanzu), wanda ya ba da gudunmowar da har a yau ba wanda ya ba da irinta a harkar lafiya. Domin ba sau daya ba, ba sau biyu ba, ya sha kawo bayanai na canjin tunani da hujjoji masu
gamsarwa a harkar lafiya. Misali, shi ne wanda ya fara bambance ciwon Agana (mai sa cin zanzana, wanda kuma aka riga aka ga bayanta a yanzu) da Bakon Dauro, wanda duka kwayar cutar birus ce ke kawowa.
Shi ne kuma wanda ya kirkiro kayan aikin likita da dama irinsu. Ya rubuta littattafai a kan harkar lafiya fiye da guda dari. Fitacce a cikinsu shi ne “Al-Hawi”. wanda kundin bayanai ne a kan aikin likita da ya shafi magunguna da yadda suke aiki a jikinmu.
A wani shagube da ya taba yi wa wani mai maganin ciwon ido, wanda ya kawo masa magani don ya sa a idonsa, sai ya tambaye shi da ya yi masa bayanin yadda ido ke aiki amma ya kasa, don haka ya ce maganin karya ne. Wannan ne ke mana tuni da taka-tsan-tsan wajen sayen magunguna a wurin jahilai.
~ Ali Ibn Abbas: Haly Abbas (920-994AD): Shi ma daga Farisa ya fito kuma ana ji da shi a duniyar likitanci. Ya ba da gudunmowa ta hanyar rubuta littattafai cikin harshen Larabci, wadanda suka fi bayani a kan bangaren kwakwalwa da cututtukanta da bayanan falsafar binciken kimiyya irin na zamani.
~ Abul kasim Al-Zahrawi: Abulcasis (936- 1013AD): Wanda yake Balarabe ne wanda aka haifa a kasar Spaniya. Ya yi fice wajen zama likitan tiyata na farko na zamani a duniyar Musulunci saboda kirkiro kayan aiki na leka
wurare da dama na jikin mutum da ya yi, fiye da dari biyu, wadanda daga su ne aka kera na wannan zamani.
Shi ne kuma ya fara nuna wa duniya cewa za a iya samun juna biyu a wajen mahaifa saboda tiyatar da ya sha yi a wannan bangare.
Ya zama likitan Khalifan Musulunci a kasar Andalusiya, wato Khalifa Al-Hakam kuma ya rubuta littattafai da dama a kan aikin tiyata, wanda har yanzu akan samu manhajojin a littattafan wannan zamani. Domin karin bayani, za a iya bincikar Kitabut Tasrif.
~ Abu Ali Ibn Sina: Abicenna (980-1037): Shi ma mutumin kasar Farisa ne, wanda yake da baiwar kaifin hadda da tunani mai zurfi.
Ya haddace Alkur’ani yana dan shekaru goma kacal, sa’annan ya zama likita yana dan shekara sha shida. Ya yi aikin duba marasa lafiya kyauta a wannan birni kuma ya zama babban likitan Khalifan garin.
Daga baya ya yi hijra ya nufi yamma, inda a hanya ya rubuta kundaye a kan bayanai na kula da lafiya da aikin likita, ya kuma koyar da dalibai.
Wannan kundi wanda ake kira ‘kaanun fid dibb’ an dade ana amfani da shi a jami’o’in kasashen
yamma na wancan lokaci, a matsayin littafin koyarwa.
~ Ga kuma irinsu Ishak Al-Ruhawi dan kasar Turkiya, wanda ya fara bayani a kan tarbiyyar likitoci; wato yin tsantseni da taka-tsan-tsan a kan aikin likita da hukuncin da ya kamata a ba likitoci masu ganganci da aiki a cikin littafinsa mai suna ‘Adab Al-Tabib.’ Shi ne kuma ya fara bayanin cewa kowane sabon abu aka samar a kimiyyar likita, dole a samu wasu kwararru a aikin su zurfafa bincike don tabbatar da sabon bayanin ko karyata shi.
~ Sai kuma wasu da dama irinsu malaman wadannan da muka lissafa wadanda ba su yi fice kamar dalibansu ba. Misali, malamin Al Razi, Abu Hassan Al-Tabari, wanda ya yi fice a harkar lafiyar yara.
~ Akwai kuma irinsu Abu Alhassan Ibn Al-Nafis, likitan kasar Suriya wadanda Turawa ma ba su sani ba ko kuma suka sani amma suka ki ambatonsu.
Shi ne wanda ya fara bayanin yadda jini ke zagaya jikinmu, tun kafin ma a haifi Baturen nan William Harbey, wanda suka ce shi ya fara wannan bayani.
Ya Allah ka tabbatar damu akan daidai kasa Aljannar Firdausi itace makomarmu.

واَلسَلامُ عَلَيْكُم وَرَحْمَةُ اَللهِ وَبَرَكاتُهُ‎

TARIHIN SHEIKH ISMA’ILA IDRIS BN ZAKARIYYA

TARIHIN SHEIKH ISMA’ILA IDRIS BN ZAKARIYYA !!!
     **Gwagwar mayarsa wajen Kafa Izala da Sunnah***

Sheikh Isma’ila Idris

yatasone cikin al’umar nan tamu ta Nigeria, ayankin Arewa inda awannan lokacin babu wata aqida a Qasarnan bayan Dariqar Tijjaniyya, Qarqashin jagorancin sheikh Ibrahim Inyas Alkaulahy.
     To dake zamani ya Nausa tafiya tayi nisa, Al’uma tasamu kanta cikin yanayi na Cakuda addini da Son zuciya. Ana samun Malamai masu Sanya Son ransu acikin addini suna anfani dasunan Addini Suna isarda Munanan manufofinsu ga Al’uma kalar Bokanci da Sihirin Duba dama wasu Tsubbace_tsubbace su na Son Zuciya da Neman duniya.
    Wanda yaci karo da koyarwar Addinin Musulunci. Dukkan mai irin wad’annan aiki Bai tabayinsu Saiya fita a addinin Musulunci, Yazamo dukkan wanda yayi Sunansa kafiri da Nassin Aya acikin Suratu baqarah. Haqiqah bayan Wannan Akwai wasu littattafai dadama wadanda Maluma suka shigo dashi ake karantasu na Labaran mafarki da Tatsuniyoyi dasunan Adddini, Irin wadannan abubuwa dakuma makamantansu Sune maqasudin Da’awar ta Sheikh Isma’il Idris, abisa fahimtar masu kyautata masa zato.
    Da’akwai wadanda suke ganin cewa kawai yafara da’awar izala ne kawai Don Neman Suna dakuma Zagin Wasu malamai (Shehunnan ‘Dariqu) dakuma Sufaye. Wanda kuma hakan kuskurene domin  Aikin Musulmi shine kyautatawa juna zato. Da Kuma nemawa juna gafara agunda akayi Kuskure danganeda Sa’banin Ra’ayi ko Fahimta.
    Zamu cigaba ta Tarihi.
    Bayan Malam Yabar aikin Soja wanda acikin Aikin nasa na Soja ya fara da’awa akan barin Tsubbu da Daura layu da makamantansu, Malam yasha tsangwama daga makiya dakuma wadanda basu da ilimi wanda basu fahimceshi ba. Ba awannan Lokaci malam yaga cewar Wannan Da’awa tasa bazata cigaba ba Har saida wata Qungiya Wacce zata Tallafa masa Danganeda samun cikar Qudirinsa na Farkadda mutane game da Sunnah Asali.
    Awannan lokacine malam ya Assasa wata Kungiya mai Suna; ”Jama’atu izalatul Bid’ah ” Ma’ana ( Gungiyar dake kawar da Bidi’ah ) Wannan Kungiya Tasa tasamu karbuwa hatta aciki ‘Yan uwa Sojoji na wannan lokaci, Saidai kuma tasamu naqasu Sosai daga Malaman wannan zamanin Musamman wadanda keda Wannan aqidar ta Tsubbace_tsubbace da Duba. Tayadda sukayita yimasa Tuggu da zagon kasa gurin Sun ga sun dakushe wannan aikin Nasa, Tare da Wargaza aikin Nasa tahanyar kirkiran karya akansa hadda cutar dashi domin Su samu Galaba akansa, Amma ahakan Allah ya Tserataddashi daga dukkan tarakunan nasu Allah ya kuma karfafa Wannan Da’awa tasa har ilayau Qugiyar izala tana nan kuma tana cigaba da aikinta wajen karantar da Al’uma bisa koyarwar magabata dakuma Tabbatar da Qur’ani da Hadisi sune tafarkin Tsira ga Bayi.
    Ahakan aka cigaba da kasancewa har takai yaje izuwa ga Malamin sa na Tauhidi Assheikh Abubakar Mahmud Gumi, Domin neman izini da Karin lamani dangane da Da’awar tasa. Awannan lokacine Sheikh Abubakar Mahmud Gumi ya nuna Bashi Cikakkiyar goyon baya gamida Cikatamasa Sunan Gungoyarsa da ” Wa’iqamatissunnah ”  ma’ana ( Dakuma Tsayar da Sunnah ) Wcce tazamo ” Jama’atu izalatul Bid’ah Wa’iqatissunnah ”
    Ma’an ( Qungiyar dake kawar da Bidi’a kuma take Tsayar da Sunnah )
    Domin acewarsa Sheikh Abubakar Mahmud Gumi; Babu Yadda za’ayi akawar da bidi’a abarta haka ba acike Gurbinta da wani abu ba, Shine Yace to sai Acike Gurbinta Da Sunnah.
    Kunga Ashe kenan ita Izala ba Fitina bace Sabanin Yadda wasu daga cikin maluman ma da basu fahimta ba, Kuma bawai Reshen addini bace kamar yadda wasu suke yimata Mummunar fahimta Har ma wasu ke ganin Cewa in baka ciki to baka cika musulmiba, wasu kuma ke Mata ganin Cewa inkan cikinta Musuluncinka da Gyara Haqiqa Dukkan Mai yiwa Wata Aqidah ta Musulunci ganin Wannan Al’amari, Alal hakika ya Jahilci Hakikanin Musulunci,
    Wannan kadan kenan daga Tarihin Sheikh Isma’ila Idris da Gwagwarmayarsa gurin kafa Izala, insha Allah Anan gaba Zan kawo muku Cigaban da iza ta Kawo Wa Musulunci da Kasarmu baki daya. In Allah mai Komai ya kaimu bayan Sallah.
    Nine naku Isma’il Hussaini Adam Alpholtawy
    Kuma Wannan Shine karshen Rubutuna danganeda Shafukan Tarihin na Bana A Hijira sheka ta 1442 Saikuma Allah ya Kaimu Almuharram Shekara ta 1443 Zan cigaba da Wannan Tarihi.
    Mai karatu ga Addu’a ta Katayani da Ameen.
    Ya ALLAH Kajiqan Mahaifina Hussaini Adam Jumba wanda Ya Rasu a irin Wannan wata Mai Alfarma kuma Aranar Idin Adhhaa, Idin Babban Sallah Allah Kajikansa Ka gafarta masa ka kai Harke Qabarinsa, Kabashi Aljannah Madaukakiya.
    Ya ALLAH Mu Zuri’arsa Da muka Rage a bayan Kasa Allah ka azurtamu da Dogora abisa Addininka, Kabamu Shahada irin tasa, kasanyamu Cikin Wadanda kake Yantawa Zuwa Aljannah.
    Ya ALLAH Ka Sitirtamu da Sutura ta Musulunci, Ka azurtamu da Arzikin imani, da Ikhlasi da Tabbatuwa akan imani, Har Mu Mutu muna masu imani Da Miqa wuya gareka Allah.
    Ya ALLAH ka daukaka musulunci da musulmai, ka Qaskantar da Kafirci da Kafirai kadirkake makiyanka makiyan addini Allah kataimaki bayinka Nagari.

LITTATTAFAN ADDIN

Daga Shafin Alpholtawy media

Zamu Daura Guda Goma insha Allahu muna Kyautata Zaton Zakuci Moriyarsu.

.

MUYIWA KANMU ADALCI

ALAKAR SHEIKH DR AHMAD GUMI DA MASU GARKUWA DA MUTANE

     Kada kayanke Hukunci Sai Ka karanta Dukka

Bayan da Gwamnatin Nigeria karkashin jagorancin Maigirma shugaban kasa Alhaji Muhammadu Buhari Maigaskiya ta dauke service network a jihar Zamfara domin sojoji su gudanar da aiki na musamman akan masu garkuwa da mutane da suka samo asali daga yankin Zamfara suka yadu zuwa wasu jihohin Arewa
Ance Sheikh Dr Ahmad Gumi yace bai kamata Gwamnatin Nigeria ta kyale sojoji suna ruwan wuta ta sama da kasa akan sansanonin barayin dajin Zamfara ba suna hallakasu mazansu da matansu da yaransu, Malam yace kamata yayi Gwamnatin Nigeria ta yiwa barayin afuwa kamar yadda ta yiwa tsagerun Niger Delta afuwa
Fadin wannan maganar naga jama’a suna ta kokarin cin mutunci da zagin Sheikh Dr Ahmad Gumi, har ma wasu suna kira cewa a kamashi, wai yana goyon bayan barayin bindiga, wannan ne ya bani karfin gwiwa domin nayi wannan rubutun
A hakikanin gaskiya duk wanda ya zargi Sheikh Dr Ahmad Gumi da alaka da ‘yan bindiga ko tarayya cikin ayyukansu na ta’addanci to mai wannan zargin idan har ba makiyin Musulunci bane idan ance yana da kwakwalwar jakuna ba laifi bane
Dr Ahmad Gumi sulhu yake jagoranta, kamar yadda aka taba samun wadanda ba Musulmai ba suka jagoranci sulhu tsakanin Gwamnatin Nigeria da tsagerun Niger Delta, aka taba samu har da turawa makiyanmu makiya addinin mu suka jagoranci sulhu tsakanin Gwamnatin Nigeria da ‘yan Boko Haram kan musayen ‘yan matan Chibok
Kowa ya tsaya yayi tunani, shin menene ya faru muka wayi gari fulanin jeji makiyaya suka dauki bindiga suka zama barayin jeji masu garkuwa da mutane?
Wanda bai san abinda ya faru ba to ga cikakken bayani
(1) Rashin adalci na wasu jami’an tsaron Gwamnatin Nigeria Azzalumai maciya amana shi ya tunzura fulanin jeji suka dauki makami suka zama ‘yan ta’addan dole
Wato idan wasu azzaluman jami’an tsaro suka shiga jeji neman barayin shanu, duk wani bafulatani da aka gani yana kiwo sai a kamashi ko a harbeshi a kora shanunsa, ana kashe iyayensu akan idon su, ana kama matansu ana musu fyade a kan idon su, wannan yasa sukace tunda bamuyi komai ba ana kashe mu ana kwace mana shanu to bari mu dauki makami muyi ta’addancin da tushe domin daukar fansa
Wallahi wannan shine farkon abinda ya jawo fulanin jeji suka zama ‘yan ta’adda, marigayi Alhaji Ali Kwara ya tabbatar da wannan a hiran da VOA Hausa tayi dashi, su kansu manyan Kwamandojin barayin daji sun tabbatar da wannan zalunci da wasu jami’an tsaron Gwamnati suka musu a farko, shi ya kaisu zama ‘yan ta’adda a yau
(2) Sannan sai sakaci da Musulmai sukayi: wato aka ki shiga jeji a karantar da fulani addini aka barsu cikin bakin duhu na jahilci, ‘yan bazata (Missionary) suka shiga suka canza musu addini, Faransa ta shiga ta karkashin kasa ta basu makami, Boko Haram da Ansaru suka hada kai dasu suka fara zubar da jinin al’umma ba gaira babu dalili
A takaice wannan shine abinda ya faru, sannan a ilmin tsaro an kasa nau’ukan ta’addanci gida hudu:



Cikin na’ukan ta’addanci guda hudu, uku daga cikinsu suna da saukin magancewa, kuma ilmin tsaro ya tabbatar da ana iya yin sulhu da su imbanda wanda suke ta’addanci akan akida ta addini wanda suke fatan su mutu a kai.
Fulanin jeji suna ta’addanci ne akan daukar fansa, ashe za’a iya yin sulhu da su idan sulhun za’ayi da gaske
An gwada yin sulhu da wasu barayin jeji amma ba’a sanya gaskiya a ciki ba, kuma rashin gaskiya yafi yawa daga bangaren Gwamnati, an sanya yaudara ne saboda ana da wata boyayyar manufa ga zaman lafiya da tsaron Arewacin Nigeria, wannan shine abinda Sheikh Dr Ahmad Gumi yake ta kokarin fahimtar da al’ummar mu
Ni da ku mun sani cewa Sheikh Dr Ahmad Gumi abinda yakeyi ba wai yanayi don biyan bukatar kansa da na iyalansa bane, shi a yadda yake yanzu har ya koma ga Allah Gwamnatin Nigeria zata bashi tsaro a duk inda zai je ya dawo, don haka yanayi ne saboda ni da kai ‘dan uwa talaka wanda bamu kai matsayin da za’a bamu sojoji da ‘yan sanda suyi gadin mu ba har karshen rayuwa
Idan akwai kuskure cikin kokarinnda Dr Ahmad Gumi yake na ayi sulhu to bai wuce guda daya ba, zanyi bayani a rubutu na gaba Insha Allah
Muna fatan Allah Ya tsare mana Sheikh Dr Ahmad Gumi, Allah Ya kawo mana sauki da mafita a tsaron Nigeria

Amin Yaa Hayyu Yaa Qayyum