MASHAHURAN MUSULMAI DA SUKA FARA KIRKIRAN AIKIN LIKITANCI A DUNIYA


Kamar yadda nayi bayani a rubutu na farko Wani abin haushi da Turawan yamma na yanzu suke yi shi ne, na boye sunayen Musuluncin waɗannan mutane, suna sa musu nasu na Turanci, wai don a ce su ma nasu ne.
Ga kadan daga cikin irin wadannan mashahuran Musulmin da suka fara kirkiro abubuwan da har yanzu ake amfani da su: An ba da duka sunayensu na ainihi da na Turancin da kuma zamanin da suka zo:
~ Muhammad bin Zakariyya Al-Rhazi: Rhazes (865-925AD):Mutumin kasarFarisa (kasar Iran ta yanzu), wanda ya ba da gudunmowar da har a yau ba wanda ya ba da irinta a harkar lafiya. Domin ba sau daya ba, ba sau biyu ba, ya sha kawo bayanai na canjin tunani da hujjoji masu
gamsarwa a harkar lafiya. Misali, shi ne wanda ya fara bambance ciwon Agana (mai sa cin zanzana, wanda kuma aka riga aka ga bayanta a yanzu) da Bakon Dauro, wanda duka kwayar cutar birus ce ke kawowa.
Shi ne kuma wanda ya kirkiro kayan aikin likita da dama irinsu. Ya rubuta littattafai a kan harkar lafiya fiye da guda dari. Fitacce a cikinsu shi ne “Al-Hawi”. wanda kundin bayanai ne a kan aikin likita da ya shafi magunguna da yadda suke aiki a jikinmu.
A wani shagube da ya taba yi wa wani mai maganin ciwon ido, wanda ya kawo masa magani don ya sa a idonsa, sai ya tambaye shi da ya yi masa bayanin yadda ido ke aiki amma ya kasa, don haka ya ce maganin karya ne. Wannan ne ke mana tuni da taka-tsan-tsan wajen sayen magunguna a wurin jahilai.
~ Ali Ibn Abbas: Haly Abbas (920-994AD): Shi ma daga Farisa ya fito kuma ana ji da shi a duniyar likitanci. Ya ba da gudunmowa ta hanyar rubuta littattafai cikin harshen Larabci, wadanda suka fi bayani a kan bangaren kwakwalwa da cututtukanta da bayanan falsafar binciken kimiyya irin na zamani.
~ Abul kasim Al-Zahrawi: Abulcasis (936- 1013AD): Wanda yake Balarabe ne wanda aka haifa a kasar Spaniya. Ya yi fice wajen zama likitan tiyata na farko na zamani a duniyar Musulunci saboda kirkiro kayan aiki na leka
wurare da dama na jikin mutum da ya yi, fiye da dari biyu, wadanda daga su ne aka kera na wannan zamani.
Shi ne kuma ya fara nuna wa duniya cewa za a iya samun juna biyu a wajen mahaifa saboda tiyatar da ya sha yi a wannan bangare.
Ya zama likitan Khalifan Musulunci a kasar Andalusiya, wato Khalifa Al-Hakam kuma ya rubuta littattafai da dama a kan aikin tiyata, wanda har yanzu akan samu manhajojin a littattafan wannan zamani. Domin karin bayani, za a iya bincikar Kitabut Tasrif.
~ Abu Ali Ibn Sina: Abicenna (980-1037): Shi ma mutumin kasar Farisa ne, wanda yake da baiwar kaifin hadda da tunani mai zurfi.
Ya haddace Alkur’ani yana dan shekaru goma kacal, sa’annan ya zama likita yana dan shekara sha shida. Ya yi aikin duba marasa lafiya kyauta a wannan birni kuma ya zama babban likitan Khalifan garin.
Daga baya ya yi hijra ya nufi yamma, inda a hanya ya rubuta kundaye a kan bayanai na kula da lafiya da aikin likita, ya kuma koyar da dalibai.
Wannan kundi wanda ake kira ‘kaanun fid dibb’ an dade ana amfani da shi a jami’o’in kasashen
yamma na wancan lokaci, a matsayin littafin koyarwa.
~ Ga kuma irinsu Ishak Al-Ruhawi dan kasar Turkiya, wanda ya fara bayani a kan tarbiyyar likitoci; wato yin tsantseni da taka-tsan-tsan a kan aikin likita da hukuncin da ya kamata a ba likitoci masu ganganci da aiki a cikin littafinsa mai suna ‘Adab Al-Tabib.’ Shi ne kuma ya fara bayanin cewa kowane sabon abu aka samar a kimiyyar likita, dole a samu wasu kwararru a aikin su zurfafa bincike don tabbatar da sabon bayanin ko karyata shi.
~ Sai kuma wasu da dama irinsu malaman wadannan da muka lissafa wadanda ba su yi fice kamar dalibansu ba. Misali, malamin Al Razi, Abu Hassan Al-Tabari, wanda ya yi fice a harkar lafiyar yara.
~ Akwai kuma irinsu Abu Alhassan Ibn Al-Nafis, likitan kasar Suriya wadanda Turawa ma ba su sani ba ko kuma suka sani amma suka ki ambatonsu.
Shi ne wanda ya fara bayanin yadda jini ke zagaya jikinmu, tun kafin ma a haifi Baturen nan William Harbey, wanda suka ce shi ya fara wannan bayani.
Ya Allah ka tabbatar damu akan daidai kasa Aljannar Firdausi itace makomarmu.

واَلسَلامُ عَلَيْكُم وَرَحْمَةُ اَللهِ وَبَرَكاتُهُ‎

TARBIYAR MATASA

•••°°°TARBIYAR MATASA°°°•••

Godiya ta tabbata ga ALLAH madaukakin sarki, Tsira da amincin ALLAH su tabbata ga fiyayen Halitta, kuma cikamakin ANNABAWA DA MANZANNI, shugabanmu Annabi Muhammad (SAW) da Alayensa da Sahabbansa tare da mabiya sunnah har zuwa ranar qarshe.
Bayan haka ‘yan uwana ina mai farin cikin gabatar muku da wannan muhadara wanda na sanya mata taken ★TARBIYAR MATASA★ badon wai na iya ba, ba kuma don nuna qwarancewa ba a’a kawai dai ina ganin ya kamata mu rinqa tattaunawa abisa matsalolin rayuwarmu ta yau da kullum.

•••WANENE MATASHI???•••
MATASHI shine (Almukallab) wato baligi wanda shari’a ta hau kansa, shine wanda idan yayi aiki Nagari za’a rubuta masa ladan aikinsa haka kuma idan yayi mummuna nan ma za’a rubuta masa abunda ya aikata acikin littafinsa.

°FARKON ABINDA YAKE WAJABA AKAN MATASHI° Farkon abinda yake wajaba akan matashi shine yayi imani da ALLAH ma’ana ya kadaita ALLAH shi kadai ya kuma shaida Muhammad bawan ALLAH ne kuma Manzon sa ne (SAW), kuma yayi imani da littatafanda ALLAH ya sauqar kuma yayi imani da qaddara mai kyau da maras kyau, kuma ya san da cewa akwai kwanciyar kabari akwai kuma tambayoyin cikin kabari akwai tashin alqiyama akwai hisabi akwai sakamako akwai tsallaka siradi, akwai wuta akwai aljannah. Kuma ya san cewa duniya gidan aro ce, lahira ita ce gida na gaskia ya kuma kyautatawa mahaifansa, kuma ya tsaida ibadarsa kamar yadda aka umurci dan Adam.

••TA YAYA ZAI ZAMA NAGARI GA AL`UMMA???••
Dole ne sai matashi ya kiyaye abubuwa muhimmai na rayuwa wa enda matuqar yana son ya zamanto matashi daga cikin matasa ingantattu kuma nagartattu, sai ya kiyaye addininsa, sai ya kasance mai Hakuri, mai ladabi, mai biyayya, mai neman ilimi, mai kauracewa alfasha, mai girmama na gaba dashi, mai tunani kafin aiwatar da wani abu mai neman shawara kafin gabatar da wani abu, mai sada zumunci mai yawan tausayi, mai gudun duniya, mai dogaro da kansa da neman abun kansa ta hanyar halak, wadannan abubuwa da muka lissafa sune zasu karfafa ★TARBIYAR MATASA★.
Ita dai TARBIYA ta samo asali ne daga tushen iyaye, Tarbiya tana ginuwa ne daga samun uwa tagari domin ita ke kasancewa makaranta ga ‘yayanta. Shiyasa Annabi MUHAMMAD (SAW) yayi umurni da a auri mace ma’abociyar addini domin kasancewar saita san addini sannan tasan yadda zata yi ta tarbiyantar da ‘yayanta.
A yau mun wayi gari Tarbiyar Matasanmu yana gur6acewa ta hanyoyi da dama a wannan zamani da muke ciki.★TARBIYAR MATASA★ tana samun matsala daga manyan mutane walau masu siyasa walau sarakuna ta hanyar amfani da matasa a wannan lokaci da suke yi na haddasa gaba da qiyayya a tsakani, da yin qoqarin aiki da matsa wajen basu makamai don kashe musu abokan gabansu wannan ba daidai bane. Ya kamata MATASA suyiwa kansu fada kuma su duba duk sanda aka umurce su da kai hari na kisa ba zaka ga daya daga cikin ‘yayan wanda suka tura su don ta’addancin ba, saboda haka mai zai sa su tsaya suna kashe junansu???, bayan ALLAH (SWT) yana cewa acikin suratul Anfaal: ( FATTAQULLA WA ASLIHU ZATA BAINIKUM WA’ADILLAHA WARASULAHU INKUNTUM MU’AMINEEN). Ma’ana:- (kuji tsoron ALLAH kuma ku daidaita tsakaninku kuma kubi ALLAH da Manzonsa idan kun kasance muminai)
Kuma ALLAH (SWT) ya qara cewa acikin suratul Hujurat :- (INNAMAL MU’UMINUNA IKHWATUN FA ASLIHU BAINA AKAWAIKUM WATTAQULLAHA LA’ALLAKUM TURHAMUUN). Ma’ana :- (su muminai yan’uwan juna ne don haka idan wani abu ya faru, to ku daidaita tsakaninku kuma kuji tsoron Allah ko a jiqanku) to saboda me matasa zasu rinqa kashe junansu.

•MATSALOLIN MATASA A YAU•
Yau an wayi gari MATASA sune shaye shaye, batsa duk wani abunda bayida kyau sai a samu MATASA ne suke aikata shi. Alal haqiqa ana samun iyayenda suke yiwa yaransu cikakkiyar tarbiya amma daga bisani sai yaran sufi karfinsu. Ba wani abu bane ke kawo haka illa zamantakewa na rayuwa a wurare guda (4) GIDA, MAKARANTA, KAN HANYA, ABOKAI wadannan abubuwa suke kawo illoli ga ★TARBIYAR MATASA★ a wannan qarni a wannan zamani da muke ciki.
Cudanyar Mata da Maza tana daga cikin hanyar lalacewar ★TARBIYAR MATASA★ musamman MATA zaku ga mace don tana ganin ta girma tana ganin tsayinta yayi daidai dana mahaifiyarta, tana ganin ta hadu da abokai na banza masu fure mata kunnuwa, to wallahi ki sani duk wani taqama da kikeyi a rayuwa da sanya damammun kaya masu fidda surorinki a bayyane tare da yin tozo da kanki kamar tozon raqumi wanda ake qira da a cuci gara saboda kina jin ke kin balaga kina jin tashe yana tashi a tare dake to wallahi kiji tsoron ALLAH. Domin Annabi MUHAMMAD (SAW) yace (Mata mafi yawansu ma’abota wuta ne, kuma Manzon ALLAH (SAW) Ya siffanta mata nau’i nau’i da ya gani acikin wutan jahannama, Wallahi Mata abun tausayi ne amma sai suka zama masu bijirewa baiwar da ALLAH yayi musu suka tsiri koyi da yahudawa da nasara. Abun mamaki wai Yarinya tasa Hijab har qasa ta fita sai kaji tace maka kunya take ji saboda tsantsar koyi da yahudawa.
Mafi yawan MATASA basa bada hankalinsu wajen karatun Addini kowa ka ta6a Boko, musamman mata zaku ga akan karatun boko tamkar zata kashe kanta, amma idan aka bincika wata zaka samu ko farillan al’awala bata sani ba, amma idan ka tambayeta Geography, Biology, chemistry zata yita kawo maka tamkar a qwaqwalwarta aka gina su, Haba Matasa !!!
Ina qara jan Hankalin ‘yan uwana Matasa dasu kiyaye Tarbiyarsu, su kula da rayuwarsu kada su shagala da wannan duniyar domin Annabi (SAW) yace: Duniya kurkukun Mumini ce kuma aljannar kafiri ce) Muslim ne ya ruwaito wannan Hadeeth din.
Kuma Manzon ALLAH (SAW) yayi qiran Matasa da cewa:- Yaku taron samari duk wanda yake da iko acikinku to yayi aure don yafi rintse ido kuma yafi kame farji, wanda kuma bai samu iko ba to na hore shi da yin azumi domin shi yana kashe sha’awa) (Bukhari da Muslim da Tirmizi da Abu Dawud da Nasa’i suka ruwaito wannan hadeethin). Ina Qara qira ga ‘yanuwana Matasa dasu kasance masu neman abun Hannunsu, ma’ana su kasance masu sana’a, domin fadin ALLAH (SWT) acikin suratul Naba’i :- (WAJA’ALNAN NAHARA MA’ASHA) ma’ana:- (Mun sanya muku rana domin ku fita ku nemi abinci). Kuma Manzon ALLAH (SAW) yace (ALLAH yana son mumini mai riqe da sana’a saboda ALLAH. Manzon Allah Ya qara cewa:- (Mafificiyar sana’a ita ce sana’ar mai akikin hannu idan yayi adalci) (Ahmad ne ya ruwaito wannan hadeeth din a musnadinsa).
Haka kuma bayani yaxo daga cikin Hadithin Abu-Huraira cewa an tambayi Manzon ALLAH (SAW) cewa wace sana’a ce tafi dadi??? Sai Manzon ALLAH (SAW) yace aikinda mutum yake yi da hanunsa da dukkan wani ciniki ingantacce (Ahmad ne ya ruwaito shi). Saboda haka ya kamata MATASA su kwadaitu ga yin sana’a kuma ayi sana’ar saboda ALLAH. Ina kuma qara qira ga ‘yanuwana matasa har da dukkan dan ‘adam da su guji KARYA, ZINA, SHANGIYA, ANNAMIMANCI, KASHE JUNA, GIBA (GULMA), RASHIN TAUSAYI, CACA, SON DUNIYA, YAUDARA da dai sauransu. Ina ganin wannan shine dan abunda ALLAH ya iyar dani wajen kawowa game da ★TARBIYAR MATASA★ ina kuma roqon ALLAH ya qara shiryar damu a bisa hanya madaidaiciya yasa muyi kyakykyawar qarshe.
Ina kuma roqon ALLAH dukkan abunda muka fada daidai ya hadamu gaba daya acikin ladan, abunda muka fada bisa kuskure kuma ALLAH ya gafarta mana daman ALLAH shine ya sani ba muba.

Daga:
Yar Uwarku
Faridah Bintu Salis
(Bintus~Sunnah)

TARIHIN SHEIKH ISMA’ILA IDRIS BN ZAKARIYYA

TARIHIN SHEIKH ISMA’ILA IDRIS BN ZAKARIYYA !!!
     **Gwagwar mayarsa wajen Kafa Izala da Sunnah***

Sheikh Isma’ila Idris

yatasone cikin al’umar nan tamu ta Nigeria, ayankin Arewa inda awannan lokacin babu wata aqida a Qasarnan bayan Dariqar Tijjaniyya, Qarqashin jagorancin sheikh Ibrahim Inyas Alkaulahy.
     To dake zamani ya Nausa tafiya tayi nisa, Al’uma tasamu kanta cikin yanayi na Cakuda addini da Son zuciya. Ana samun Malamai masu Sanya Son ransu acikin addini suna anfani dasunan Addini Suna isarda Munanan manufofinsu ga Al’uma kalar Bokanci da Sihirin Duba dama wasu Tsubbace_tsubbace su na Son Zuciya da Neman duniya.
    Wanda yaci karo da koyarwar Addinin Musulunci. Dukkan mai irin wad’annan aiki Bai tabayinsu Saiya fita a addinin Musulunci, Yazamo dukkan wanda yayi Sunansa kafiri da Nassin Aya acikin Suratu baqarah. Haqiqah bayan Wannan Akwai wasu littattafai dadama wadanda Maluma suka shigo dashi ake karantasu na Labaran mafarki da Tatsuniyoyi dasunan Adddini, Irin wadannan abubuwa dakuma makamantansu Sune maqasudin Da’awar ta Sheikh Isma’il Idris, abisa fahimtar masu kyautata masa zato.
    Da’akwai wadanda suke ganin cewa kawai yafara da’awar izala ne kawai Don Neman Suna dakuma Zagin Wasu malamai (Shehunnan ‘Dariqu) dakuma Sufaye. Wanda kuma hakan kuskurene domin  Aikin Musulmi shine kyautatawa juna zato. Da Kuma nemawa juna gafara agunda akayi Kuskure danganeda Sa’banin Ra’ayi ko Fahimta.
    Zamu cigaba ta Tarihi.
    Bayan Malam Yabar aikin Soja wanda acikin Aikin nasa na Soja ya fara da’awa akan barin Tsubbu da Daura layu da makamantansu, Malam yasha tsangwama daga makiya dakuma wadanda basu da ilimi wanda basu fahimceshi ba. Ba awannan Lokaci malam yaga cewar Wannan Da’awa tasa bazata cigaba ba Har saida wata Qungiya Wacce zata Tallafa masa Danganeda samun cikar Qudirinsa na Farkadda mutane game da Sunnah Asali.
    Awannan lokacine malam ya Assasa wata Kungiya mai Suna; ”Jama’atu izalatul Bid’ah ” Ma’ana ( Gungiyar dake kawar da Bidi’ah ) Wannan Kungiya Tasa tasamu karbuwa hatta aciki ‘Yan uwa Sojoji na wannan lokaci, Saidai kuma tasamu naqasu Sosai daga Malaman wannan zamanin Musamman wadanda keda Wannan aqidar ta Tsubbace_tsubbace da Duba. Tayadda sukayita yimasa Tuggu da zagon kasa gurin Sun ga sun dakushe wannan aikin Nasa, Tare da Wargaza aikin Nasa tahanyar kirkiran karya akansa hadda cutar dashi domin Su samu Galaba akansa, Amma ahakan Allah ya Tserataddashi daga dukkan tarakunan nasu Allah ya kuma karfafa Wannan Da’awa tasa har ilayau Qugiyar izala tana nan kuma tana cigaba da aikinta wajen karantar da Al’uma bisa koyarwar magabata dakuma Tabbatar da Qur’ani da Hadisi sune tafarkin Tsira ga Bayi.
    Ahakan aka cigaba da kasancewa har takai yaje izuwa ga Malamin sa na Tauhidi Assheikh Abubakar Mahmud Gumi, Domin neman izini da Karin lamani dangane da Da’awar tasa. Awannan lokacine Sheikh Abubakar Mahmud Gumi ya nuna Bashi Cikakkiyar goyon baya gamida Cikatamasa Sunan Gungoyarsa da ” Wa’iqamatissunnah ”  ma’ana ( Dakuma Tsayar da Sunnah ) Wcce tazamo ” Jama’atu izalatul Bid’ah Wa’iqatissunnah ”
    Ma’an ( Qungiyar dake kawar da Bidi’a kuma take Tsayar da Sunnah )
    Domin acewarsa Sheikh Abubakar Mahmud Gumi; Babu Yadda za’ayi akawar da bidi’a abarta haka ba acike Gurbinta da wani abu ba, Shine Yace to sai Acike Gurbinta Da Sunnah.
    Kunga Ashe kenan ita Izala ba Fitina bace Sabanin Yadda wasu daga cikin maluman ma da basu fahimta ba, Kuma bawai Reshen addini bace kamar yadda wasu suke yimata Mummunar fahimta Har ma wasu ke ganin Cewa in baka ciki to baka cika musulmiba, wasu kuma ke Mata ganin Cewa inkan cikinta Musuluncinka da Gyara Haqiqa Dukkan Mai yiwa Wata Aqidah ta Musulunci ganin Wannan Al’amari, Alal hakika ya Jahilci Hakikanin Musulunci,
    Wannan kadan kenan daga Tarihin Sheikh Isma’ila Idris da Gwagwarmayarsa gurin kafa Izala, insha Allah Anan gaba Zan kawo muku Cigaban da iza ta Kawo Wa Musulunci da Kasarmu baki daya. In Allah mai Komai ya kaimu bayan Sallah.
    Nine naku Isma’il Hussaini Adam Alpholtawy
    Kuma Wannan Shine karshen Rubutuna danganeda Shafukan Tarihin na Bana A Hijira sheka ta 1442 Saikuma Allah ya Kaimu Almuharram Shekara ta 1443 Zan cigaba da Wannan Tarihi.
    Mai karatu ga Addu’a ta Katayani da Ameen.
    Ya ALLAH Kajiqan Mahaifina Hussaini Adam Jumba wanda Ya Rasu a irin Wannan wata Mai Alfarma kuma Aranar Idin Adhhaa, Idin Babban Sallah Allah Kajikansa Ka gafarta masa ka kai Harke Qabarinsa, Kabashi Aljannah Madaukakiya.
    Ya ALLAH Mu Zuri’arsa Da muka Rage a bayan Kasa Allah ka azurtamu da Dogora abisa Addininka, Kabamu Shahada irin tasa, kasanyamu Cikin Wadanda kake Yantawa Zuwa Aljannah.
    Ya ALLAH Ka Sitirtamu da Sutura ta Musulunci, Ka azurtamu da Arzikin imani, da Ikhlasi da Tabbatuwa akan imani, Har Mu Mutu muna masu imani Da Miqa wuya gareka Allah.
    Ya ALLAH ka daukaka musulunci da musulmai, ka Qaskantar da Kafirci da Kafirai kadirkake makiyanka makiyan addini Allah kataimaki bayinka Nagari.