ZATIN UBANGIJI

SHAUQI CIKIN AL AMARIN GAIBIYYA

Kasantuwar Ubangiji A Buya Bai zama tawaya Ga Imanin Mai imani Sai dai Yana kara imanine ga Mai imani Yayin da Yake Halarto da Imani Azuciyar Mara shi Matukar ya Kasance Mai Nazarin Lissafin Hangen Nesa da tunani Mai Zurfi.

Imani Gatane  da Yanci na Samar da Sukuni Azucikatan Bayi gamida Samuwar Hasken Zuciya dana Ruhi, Wanda Yazamo Tasirin Samuwar Kyakkyawar Rayuwa Mai Inganci Aduniya dakuma Samun Kyakkyawar Sakamako Bayan Mutuwa.
Wannan Duk darajace da Muqami amma ga Wanda Ya Gasgata Ubangiji Kuma yake Tsoran sa, Shi kadai Baya Tsoron Sharri Sai abinda Ubangijiﷻ Yanufa Shi zai Iya faru Gareshi arayuwa.

Ubangiji ya Boye Zatinsa Na Wanzuwar Siffarnan tasa Madaukakiya, Yayi mana gata Ya Bayyana Mana ilimin Saninsa ta Hanyar Turomana Da Annabawa, Ya Rayamu bisa rayuwa Ingantacciyaya, Bamu kasance Cikin dimuwa da Makantacciyar Zuciya ba.

   Makauniyar Rayuwa itacee Rashin gane Waye Ubangiji Hakan ke tabbatar dakai Ahalaka da Tabewa Kasantuwar hakan zai sanya Maka Kaskantar da Kanka ga Abida Shine yakamata ya Girmamaka, Akasin Hakan Kuwa zai sana Ka koma kana Nema Agun Wanda Saika bashi kake kuma Rokonsa.

  Ka Kaskantar da kanka ga ubangiji da Qaramin Aikinka ga Mai Halittawa Kuma ka Rage burinka ga Duniya Domin Hidima da Bada lokaci cikin Bautawa Maqaginka domin Gyara wa  Rayuwarka na Gaba.

One thought on “ZATIN UBANGIJI

Comments are closed.