–
“Shi imani ga bawa yana tsufa kuma yana sabunta, yana raguwa kuma yana ƙaruwa”
–
“Yana tsufa ko raguwa da yawan saɓon Allah, sannan kuma yana sabunta ko ƙaruwa da biyayya ga Allah“
“A lokacin da Allah ta’ala yaso nufarka da alkhairi, sai ya jarabceka a rayuwarka sannan kuma ya baka damar cin wannan jarabawar don ya sauƙaƙa maka hanyar shiga aljannah”
–
“Gwargwadon imaninka ga Allah gwargwadon jarrabawarsa gareka, bawa baya zama mai cikakken imani ga Allah har sai sanda ya haƙurtar da kansa abisa jarabawowin da Allah buwayi yake jarabtarsa dasu a rayuwarsa ya kuma jure bai gaza cin wannan jarabawar ba, lallai kada mu manta! Tabbas dukkanin girman wata jarabawa, tana tareda girman kyakkyawan sakamako a gurin Allah, ya Allah ka jarabcemu daidai imanin mu”
–


You must be logged in to post a comment.