MATSALAR TSARO A NAIJA New post 2

MATSALAR MANYANMUNE!!

Matsalar tsaro A’kasata Fitowa ta biyu (!!) ✍️Ismail Hussaini Adam

Matsalar tsaro akasar Nigeria abune mai matukar wuya amaganceta da hanzari, Domin Al’amuran Sun jima Da Cakud’ewa cikin mummunar qaddara da muka samu kanmu aciki musanman Mu Al’umar Arewa. Ansamu akasi tahanyar wasunmu suna goyon bayan ta’addanci aboye, bincki da akeyi ana kin bayyana gaskiya, Shine babban Al’amarin daya gur’bata Al’amuran tsaro A’kasarnan. Wai sai ace anrufa asiri akwai ‘yan Alfarma.

Shifa d’an ta’adda, ko mai goyon bayan ta’addanci, Koda uwarsace data haifeshine yasan zata fallasheshi, Wallahil aziim zai aikata lahira, komai Son da takemai, balle jami’an tsaro ko Masu fad’a aji na gari Wad’anda aganinsu sune Cikas d’insu aharkar dasuke ciki. Yazama wajibi akan hukumomi, Da Shuwagabannin Al’uma ta ayyadar da hukunci, akan dukkan wani mai laifi data kama, takuma yi bincike akan dukkan wanda take zargi da ta’addanci, ko goyon bayan ‘yan ta’adda. Idan Tayi bincike inya tabbata kuma tazartar da hukuncin daya dace.

Hakan shine hanya mafi sauki, Ta hanyar da za’a gyara matsalar tsaro acikin Al’uma.

WANI ABINDA MUKA MANTA

Wad’annan masu laifi da’ake kamawa da sunan ‘barayin gida da masu fasa shagunan, Idan ba’azartar masu da hukuncin daya daceba Sune ake Sayansu Su girmama, Abasu Makamai sucigaba da ta’addanci dakuma Kisan mutane, haka kurum ba gaira ba dalili.

Dole ne acire maganar Alfarma, Dukkan wanda hukunci ta haushi kawai azartar masa shine adalci. Allah yafi kowa son bayinsa Amma yana hukumtasu idan sun aikata ba daidaiba. Tayadda yakema ‘Kona wasuma domin mummunar aiki dasuka aikata. Kuma yayi umarni garemu akan mu zartar da hukunci da adalci akan dukkan wanda doka ta haushi.

Hakika Al’uma tana shiga firgici da mummunar yanayine tahanyar sakaci da’akayi da hukunta masu laifin cikinta. A Nigeria mun sami kanmu cikin wannan yanayi tahanyar Sakacin hukumominmu da shugabanninmu.

RASHIN AIKINYI GA MATASA MA QALUBALENE

Matasa babu aikinyi a kasarnan dalili kuwa Shine, manyanmu basu kishin kafa wadatattun masana’antu burinsu gina gidaje kawai da zuwa ‘kasashen waje. Taya ‘Kasan wajen suka sami Cigabane Bayan samun nagartattun Shugabanni masu kishi Suna kula da hakkin Talakawansu. Yakamata Asamarda wadatattun masana’antu tayadda za’arage masu zaman banza dakuma yan Fasa ‘kwauri akasarnan. A’kasarnan akwai arzi’ki wanda yagirmi lissafi amma kuma munfi kowa Talakawa, wannan yasamo asaline danganeda Rashin tallafin jari da aikinyi ga masu ‘karamin ‘karfi, Saudadama wasu na fara kasuwanci amma da zarar sunsami karayar arzi’ki shikenan yazama abin tausayi. Mai iyuwa ma wanin daganan yakan koma goyan bayan ta’addanci, domin yasamu dukiya koma yazamo member na ‘yan ta’adda.

ANA ZALUNTAR ‘DALIBAN KARATU

Harajin karatu awannan kasa nada wahalar Gaske, ga kuma ana matukar Cin dunduniyar ‘Dalibai tahanyar mugayen Lecturers. Kai harda keta alfarmar (Mutuncin) ‘yan mata. A iya Saninmu ga Manyanmu na yanzu Shine. Sunyi karatune akyauta kokuma cikin sauki, Amma donme suke musgunawa Mutane ayanzu? Mafiya yawan malaman yanzu burinsu shine su samu kudi Suma a’kirgasu acikin masu Arzi’kin ‘Kasa. Bawai su bada karatu ga d’alibai ba kamar yadda yake a hukunce. Wannan yasa suke neman Kudi ido rufe a governati domin cimma burikansu dakuma kirkiro wasu tsaruka mabambamta. wadanda suke da rauni da Da’kushe har’ko’kin ilimi akasarnan.

Strike da ake samu a jami’o’i da Colleges yasamo Asaline daga, Son duniyar wasu daga cikin Malamai. Dolene Govrenati tasan hanyar da zata shawo kan Wannan Al’amari. Mutane na kashe kud’ad’e masu yawa kuma Suna d’aukan dogon Zango kafin su kammala karatunsu. Duk asadin matsalar Yajin aiki (Strike). Kuma akarshe yazamo Sun gama karatu kuma sun rasa aikinyi, Tambaya anan itace, idan mutum mai raunin imani yasha wannan wahalar kuma yarasa aikinyi, Me kuke tunani Zai biyo baya?

MATSALAR ASAMACE

Manyanmu na sama Sune ke morar arzikin ‘kasarnan. Manyan Nigeria mutum daya na d’aukan ma’kudan kud’i a governatin tarayya fiyeda Lissafin mai tunani Amma Nakasansu kuwa suna shan wuya matu’ka, Amma abinda suke samu ko na man mota baya wucewa, ballema aje ga Masarufi, dakuma Suturar jikki da kayan ‘Kawar ado. Don me corruption bazai Existing atsakanin muba Alhali wasunmu naci da gumin wasu. Su kuma manta da Hakkin dake tsakaninsu na zamantakewa. A’ka’idar Zamantakewa ta mususukunci dolene kasan Ci da Shan ma’kocinka Kamar yadda zakasan na Iyalinka.

Amma ayanzu babu ruwan wani da Wani, Anyi watsi da karantarwar addini anbi yahudu kuma gashi an’bace ba akamo yahuduba kuma Ambar Allah. Wadannan ma Suna daga cikin Hanyoyi mafiya girma na sanadin Lalacewar Tsaro a Nigeria. Zanci gaba Insha Allah. Allah ya tabbatar damu akan gaskiya da shiriya.